< Luka 5 >

1 Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
And it came to pass while the multitude was pressing on him to hear the word of God, and he was standing by the lake of Gennesaret,
2 sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
that he saw two ships standing by the lake: but the fishermen had gone out of them, and were washing their nets.
3 Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
And he entered one of the ships, which was Simon’s, and requested him to push out a little from the land. And he sat down and taught the multitude from the ship.
4 Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
And when he had made an end of speaking, he said to Simon: Push out into the deep water, and let down your nets for a draught.
5 Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
And Simon answered and said to him: Master, we have toiled all night and have caught nothing; but at thy command, I will let down the net.
6 Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
And when they had done this, they inclosed a great number of fishes, and their net began to break;
7 Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
and they beckoned to their partners who were in the other ship, to come and help them. And they came and filled both the ships, so that they began to sink.
8 Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
And when Simon Peter saw it, he fell down at the knees of Jesus, and said: Depart from me, Lord, for I am a sinful man.
9 Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
For amazement at the draught of fishes which they had caught had seized upon him and all that were with him;
10 Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
and in like manner also upon James and John the sons of Zebedee, who were partners with Simon. And Jesus said to Simon: Fear not; from this time forth you shall catch men.
11 Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
And when they had brought their ships to the land, they left all and followed him.
12 Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
And it came to pass, that he was in one of their cities; and behold, a man full of leprosy; and when he saw Jesus, he fell on his face and besought him, saying: Lord, if thou wilt, thou canst make me clean.
13 Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
And stretching out his hand, he touched him, and said: I will; be clean. And immediately his leprosy departed from him.
14 Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
And he charged him to tell no one; but go, show yourself to the priest, and make offering for your cleansing, as Moses commanded, that it may be a testimony to them.
15 Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
But his fame went abroad the more; and many multitudes came together to hear, and to be cured by him of their infirmities.
16 Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
And he withdrew to the deserts and prayed.
17 Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
And it came to pass, on a certain day, that he was teaching, and there were Pharisees and teachers of the law sitting by, who had come from every village of Galilee and Judea and Jerusalem; and the power of the Lord was exerted to heal them.
18 Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
And behold, men brought, on a bed, a man who was a paralytic. And they sought how they might bring him in, and lay him before him.
19 Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
And finding no way by which they could bring him in, because of the multitude, they went up on the top of the house, and, through the tiling, let him down, with his bed, into the midst before Jesus.
20 Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
And when he saw their faith, he said to him: Man, your sins are forgiven you.
21 Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
And the scribes and Pharisees began to reason, saying: Who is this that utters impious words? Who can forgive sins but God alone?
22 Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
But Jesus perceived their reasonings, and answered and said to them: Why are you reasoning in your hearts?
23 Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
Which is easier, to say., Your sins are forgiven you; or to say, Arise and walk?
24 Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
But that you may know that the Son of man on the earth has power to forgive sins, (he said to the paralytic, ) I say to you, Arise, and take up your bed, and go to your house.
25 Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
And he immediately arose before them, took up that on which he had been lying, and went away to his own house, glorifying God.
26 Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
And astonishment seized upon all, and they glorified God, and were filled with fear, saying: We have seen strange things to-day.
27 Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
And after these tilings, he went out and saw a publican named Levi, sitting at the custom-house; and he said to him: Follow me.
28 Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
And leaving all, he arose and followed him.
29 Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
And Levi made him a great feast at his own house; and there was a great multitude of publicans and others, who reclined at table with them.
30 Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
And their scribes and the Pharisees murmured against his disciples, saying: Why do you eat and drink with publicans and sinners?
31 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
And Jesus answered arid said to them: They that are well have no need of a physician, but they that are sick.
32 Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
I have not come to call righteous men, but sinners, to repentance.
33 Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
And they said to him: Why do the disciples of John fast often, and make prayers, and likewise the disciples of the Pharisees, but yours eat and drink?
34 Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
And he said to them: Can you make the sons of the bride-chamber fast, while the bridegroom is with them?
35 Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
But the days will come when the bridegroom shall be taken from them; then shall they fast in those days.
36 Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
And he spoke also a parable to them: No one patches an old garment with a piece taken from a new garment. If so, the new tears it, and the patch from the new suits not the old.
37 Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
And no one puts new wine into old bottles; if so, the new wine will burst the bottles, and it will be spilled, and the bottles will be destroyed.
38 A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
But new wine must be put into new bottles, and both will be preserved.
39 Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”
And no one, after drinking old wine, immediately desires new; for he says: The old is better.

< Luka 5 >