< Luka 5 >

1 Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
Hypoet taw Bawipa Jesu ce thlang kqeng mi Genesaret tuili keng awh dyi hy, cawh thlang kqeng ing Khawsak awi ce ngai uhy,
2 sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
tui keng awh ngak hawikhqi ing a mi taak hyt lawng pakkhih ce hu hy, ngak hawikhqi taw a mi lawk chuk uhy.
3 Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
Lawng pynoet ak khuiawh ce lut hy, cawhkaw lawng cetaw Simon a lawng na awm hy. Lawng ce tui benna tun bet aham Simon ce kqawn pehy. Cekcoengawh lawng awh ce ngawi nawh thlangkhqi ce cawngpyi hy.
4 Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
Awi ak kqawn boeih coengawh, Simon venawh, “Tuili dung na thoeih nawh lawk ce khawng lah,” tina hy.
5 Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
Simon ing, “Bawipa than oet pyt khawng hawh hlai u nyng ikawawm am hu u nyng. Cehlai nak awi awh khawng lah vang nyng,” tina hy.
6 Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
Lawk ce amik khawng awhtaw, nga khawzah tu unawh lawk ce teek pit pit hy.
7 Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
Cedawngawh lawng ak chang nakaw a mi pyikhqi ce ak bawm aham a mi kut ing vaih uhy, cekkhqi ce law unawh lawng ang cum pit pit dyna nga ce ak be na tu uhy.
8 Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
Simon Piter ing a huh awh, Jesu a khawkung awh khuk sym doena, “Bawipa, ni cehtaak mai, thlak thawlh na awm nyng,” tina hy.
9 Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
Nga a mim tu awh Piter ingkaw a pyikhqi ce a mik kawpoek kyi hy,
10 Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
Simon a pyi, Zebedee a caqawi Jakob ingkaw Johan awm anik kawpoek kyi hy. Cekcoengawh Jesu ing Simon a venawh, “Koeh kqih; tuh awhkawng thlang ak tukung na awm hawh kawp ti,” tina hy.
11 Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
Lawng ce kawngceng na amik dawh coengawh, ik-oeih boeih ce cehta unawh a hu awh bat uhy.
12 Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
Khaw pynoet awh a awm awh, mynqai ak neh thlang pynoet ce law hy. Jesu ce a huh awh, dek na koep nawh qeennaak thoeh hy, “Bawipa, na ngaih awhtaw ni ciimcaih sak lah,” tina hy.
13 Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
Jesu ing a kut zyng nawh bi hy. “Ngaih nyng, qoei hlah!” tina hy. Cawh a mynqai ce caih pahoei hy.
14 Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
Jesu ing a venawh, “U a venawh awm koeh kqawn, cet nawh khawsoeih a venna na pum ce nam huh coengawh, na qoeinaak a dawngawh Mosi ak awipeek a myihna, a mingmih ing a mi simnaak aham bulnaak ce sai lah,” tina hy.
15 Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
Cehlai anih akawng ce thang khqoet hy, cedawngawh ak awi ngai ham ingkaw tlawhnaak qoei sak aham thlangkhqi ce law uhy.
16 Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
Cehlai Jesu taw a dingnaak na amah doeng cet poepa nawh cykcah hy.
17 Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
Hypoet taw thlang a cawngpyi awh, Kalili qam, Judah qam ingkaw Jerusalem khaw awhkaw Farasikhqi ingkaw anaa awi cawngpyikungkhqi ce amah cawh ngawi uhy. Cawh thlak tlo qoei sak aham Bawipa ak thaawmnaak ce a venawh awm hy.
18 Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
Thlang vang ing ak khawn thlang pynoet ce a hiphaih awh kawt law uhy, ipkhui na khyn phaat unawh a haiawh tloeng peek aham ngaih uhy.
19 Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
Cehlai thlang a be aih a dawngawh ipkhui na am khyn thai uhy, cedawngawh iptih na kaai unawh qui ing thlang anglak li awh, Jesu a haiawh hiphaih mah na nuk thlaak pe uhy.
20 Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
A mingmih ak cangnaak ce Jesu ing a huh awh, “Thlang pa aw, na thawlhnaak ce qeenna awm hawh hy,” tina hy.
21 Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
Cawh Farasikhqi ingkaw anaa awi cawngpyikungkhqi ing, “U nu Khawsa ak the ak khanaak ve? Khawsa doeng am awhtaw u ing nu thawlh qeenkhaw ang ngai thai?” ti uhy.
22 Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
A mingmih ak kawpoek ce Jesu ing sim pe khqi nawh, “Ikawtih cemyihna namik kawlung khuiawh namik poek uh?
23 Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
Han nu ak zoei bet: 'Na thawlh qeenna awm hawh hy,' tive nu, am awhtaw 'Tho nawh cet hlah,' tive nu?
24 Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
Cehlai thlanghqing Capa ing khawmdek awh thawlh qeennaak tahy, tice nami simnaak aham,” tinak khqi hy. Ak khawn na ce, “Ka nik kqawn peek, tho, na hiphaih ce lo nawh imna voei hlah,” tina hy.
25 Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
A mingmih haiawh ce dyi pahoei nawh, a hiphaih ce a lawh coengawh Khawsa kyihcah doena im na ce cet hy.
26 Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
Thlang boeih a mik kawpoek kyi nawh Khawsa ce kyihcah uhy. Ngaih kyi doena, “Tuhngawi awh kawpoek kyi ik-oeih ni hu uhy,” ti uhy.
27 Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
Cekcoengawh Jesu ce cet nawh mangmu cawinaak awh ak ngawi mangmu ak cawikung Levi ak mingnaak thlang pynoet ce hu hy. A venawh, “Ka hu awh bat lah,” tina hy.
28 Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
Levi ce tho nawh ik-oeihkhqi ce a cehtaak coengawh a hu awh bat hy.
29 Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
Cekcoengawh Levi ing amah a im awh Jesu aham buh veelnaak poei ak bau soeih sai pehy. Mangmu ak cawikungkhqi ingkaw thlak changkhqi thlang khawzah ce Jesu mi buh ai haih hy.
30 Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
Cehlai Farasikhqi ingkaw anaa awi cawngpyikungkhqi ing a mi huh awh ce a hubatkhqi venawh saai bi uhy, “Kawtih mangmu ak cawikung 'Thlak thawlhkhqi' mi buh a mi ai haih?” tinak khqi uhy.
31 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
Jesu ing, “Sakdip thlang ing siboei am ngoe hy, cehlai thlak tlo ing ni a ngoe.
32 Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
Thlak dyng khy aham am law nyng, thlak thawlh a zutnaak aham ni ka law,” tinak khqi hy.
33 Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
A mingmih ing a venawh, “Johan a hubatkhqi ingtaw buh zeih poepa unawh cykcah uhy, Farasikhqi a hubatkhqi ingawm, cehlai nang a hubatkhqi ingtaw aw a ai uhy,” tina uhy.
34 Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
Jesu ing, “Zuk lokung a awm khuiawh ak khinkhqi buh namik zeih hly sak nu?
35 Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
Cehlai zuk lokung lawh peek valhnaak a tym ce pha kaw; cawh buh zeih bit kawm uh,” tinak khqi hy.
36 Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
A mingmih a venawh vawhkaw nyhtahnaak awi ve kqawn pehy: “U ingawm hi ak thai ce teek nawh hi ak kqym ap bu na khawi hy. Ak bunaak man, hi ak thai ce awm teek kaw, cekcoengawh hi ak kqym ingawm am qoep laklaw kaw.
37 Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
U ingawm misur tui ak thai ce cikthlyng ak kqym awh am thun khawi hy. A thun mai mantaw, misur tui ak thai ing cikthlyng ak kqym ce hqe kawmsaw, misur tui ingkaw cikthlyng ce plawci bawk kaw.
38 A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
Cedawngawh misur tui ak thai taw cikthlyng ak thai awh thun aham awm hy.
39 Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”
Misur tui ak kqym ce tui khqoet hy a mi ti a dawngawh, u ingawm misur tui ak kqym a awk coengawh misur tui ak thai ce am ngaih khawi hy,” tinak khqi hy.

< Luka 5 >