< Luka 4 >

1 Yesu kuwa cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga Urdun, Ruhu kuma ya kai shi cikin hamada,
Or Jésus, plein de l’Esprit Saint, s’en retourna du Jourdain et fut mené par l’Esprit dans le désert,
2 inda kwana arba’in, Iblis ya gwada shi. Bai ci kome ba a cikin kwanakin nan, a ƙarshensu kuwa ya ji yunwa.
étant tenté par le diable 40 jours. Et il ne mangea rien pendant ces jours-là; et lorsqu’ils furent accomplis, il eut faim.
3 Iblis ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka faɗa wa wannan dutse yă zama burodi.”
Et le diable lui dit: Si tu es Fils de Dieu, dis à cette pierre qu’elle devienne du pain.
4 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba.’”
Et Jésus lui répondit, disant: Il est écrit que « l’homme ne vivra pas de pain seulement, mais de toute parole de Dieu ».
5 Iblis ya kai shi can kan wani wuri mai tsawo, ya nunnuna masa a ƙyiftawar ido dukan mulkokin duniya.
Et le diable, le menant sur une haute montagne, lui montra, en un instant, tous les royaumes de la terre habitée.
6 Ya ce masa, “Zan ba ka dukan ikonsu da darajarsu, gama ni aka danƙa wa, kuma zan bai wa duk wanda na ga dama.
Et le diable lui dit: Je te donnerai toute cette autorité et la gloire de ces royaumes; car elle m’a été donnée, et je la donne à qui je veux.
7 Saboda haka in ka yi mini sujada, dukan wannan zai zama naka.”
Si donc tu te prosternes devant moi, elle sera toute à toi.
8 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, kuma shi kaɗai za ka bauta wa.’”
Et Jésus, lui répondant, dit: Il est écrit: « Tu rendras hommage au Seigneur ton Dieu, et tu le serviras lui seul ».
9 Sai Iblis, ya kai shi Urushalima ya sa ya tsaya a kan wuri mafi tsayi na haikali ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka yi tsalle daga nan zuwa ƙasa.
Et il l’amena à Jérusalem, et le plaça sur le faîte du temple et lui dit: Si tu es Fils de Dieu, jette-toi d’ici en bas;
10 Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, su kiyaye ka da kyau;
car il est écrit: « Il donnera des ordres à ses anges à ton sujet, pour te garder;
11 za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
et ils te porteront sur leurs mains, de peur que tu ne heurtes ton pied contre une pierre ».
12 Yesu ya amsa ya ce, “An ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
Et Jésus, répondant, lui dit: Il est dit: « Tu ne tenteras pas le Seigneur ton Dieu ».
13 Da Iblis ya gama dukan wannan gwajin, ya bar shi sai lokacin da wata dama ta samu.
Et ayant accompli toute tentation, le diable se retira d’avec lui pour un temps.
14 Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka.
Et Jésus s’en retourna en Galilée, dans la puissance de l’Esprit; et sa renommée se répandit par tout le pays d’alentour.
15 Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.
Et lui-même enseignait dans leurs synagogues, étant glorifié par tous.
16 Ya tafi Nazaret, inda aka yi renonsa. A ranar Asabbaci kuma, ya shiga majami’a kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe don yă yi karatu.
Et il vint à Nazareth où il avait été élevé; et il entra dans la synagogue au jour du sabbat, selon sa coutume, et se leva pour lire.
17 Aka kuwa ba shi naɗaɗɗen littafin annabi Ishaya. Da ya buɗe, sai ya sami wurin da aka rubuta,
Et on lui donna le livre du prophète Ésaïe; et ayant déployé le livre, il trouva le passage où il était écrit:
18 “Ruhun Ubangiji yana kaina, domin ya shafe ni, in yi wa matalauta wa’azin bishara. Ya aiko ni in yi shelar’yanci ga’yan kurkuku, in kuma buɗe idanun makafi, in ba da’yanci ga waɗanda aka danne.
« L’Esprit du Seigneur est sur moi, parce qu’il m’a oint pour annoncer de bonnes nouvelles aux pauvres; il m’a envoyé pour publier aux captifs la délivrance, et aux aveugles le recouvrement de la vue; pour renvoyer libres ceux qui sont foulés,
19 In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
et pour publier l’an agréable du Seigneur ».
20 Sai ya naɗe naɗaɗɗen littafin ya mayar wa mai hidimar, ya kuma zauna. Dukan idanun waɗanda suke a majami’ar, suka koma a kansa.
Et ayant ployé le livre, et l’ayant rendu à celui qui était de service, il s’assit; et les yeux de tous ceux qui étaient dans la synagogue étaient arrêtés sur lui.
21 Sai ya fara ce musu, “A yau, Nassin nan, ya cika a kunnenku.”
Et il se mit à leur dire: Aujourd’hui cette écriture est accomplie, vous l’entendant.
22 Duk suka yabe shi, suka yi mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suka yi tambaya, suna cewa, “Anya, wannan ba ɗan Yusuf ba ne?”
Et tous lui rendaient témoignage, et s’étonnaient des paroles de grâce qui sortaient de sa bouche, et ils disaient: Celui-ci n’est-il pas le fils de Joseph?
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce, na san za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka! Ka kuma yi abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, a nan garinka.’”
Et il leur dit: Assurément vous me direz cette parabole: Médecin, guéris-toi toi-même; fais ici aussi dans ton pays toutes les choses que nous avons entendu dire qui ont été faites à Capernaüm.
24 Ya ci gaba, da ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, babu annabin da ake yarda da shi a garinsa.
Et il dit: En vérité, je vous dis qu’aucun prophète n’est reçu dans son pays.
25 Ina tabbatar muku a zamanin Iliya, akwai gwauraye da yawa a Isra’ila, sa’ad da aka rufe sararin sama har shekara uku da rabi, aka kuma yi yunwa mai tsanani ko’ina a ƙasar.
Et, en vérité, je vous dis qu’il y avait plusieurs veuves en Israël, aux jours d’Élie, lorsque le ciel fut fermé trois ans et six mois, de sorte qu’il y eut une grande famine par tout le pays;
26 Duk da haka, ba a aiki Iliya ga ko ɗaya a cikinsu ba. Sai dai zuwa ga wata gwauruwa da take a Zarefat, a yankin Sidon.
et Élie ne fut envoyé vers aucune d’elles, sinon à Sarepta de la Sidonie vers une femme veuve.
27 Akwai kuma mutane da yawa a Isra’ila masu kuturta a zamanin annabi Elisha, amma ba ko ɗayansu da aka tsarkake sai Na’aman mutumin Suriyan nan kaɗai.”
Et il y avait plusieurs lépreux en Israël au temps d’Élisée le prophète; et aucun d’eux ne fut rendu net, sinon Naaman, le Syrien.
28 Dukan mutanen da suke cikin majami’a suka fusata ƙwarai da jin wannan.
Et ils furent tous remplis de colère dans la synagogue en entendant ces choses;
29 Suka tashi, suka fitar da Yesu bayan gari, suka kai shi goshin tudun da aka gina garin, don su ture shi ƙasa,
et s’étant levés, ils le chassèrent hors de la ville, et le menèrent jusqu’au bord escarpé de la montagne sur laquelle leur ville était bâtie, de manière à l’en précipiter.
30 amma sai ya bi ta tsakiyar taron ya yi tafiyarsa.
Mais lui, passant au milieu d’eux, s’en alla.
31 Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a Galili, a ranar Asabbaci kuma, ya fara koya wa mutane.
Et il descendit à Capernaüm, ville de Galilée, et il les enseignait au jour de sabbat.
32 Suka yi ta mamakin koyarwarsa, domin saƙonsa yana da iko.
Et ils s’étonnaient de sa doctrine, parce que sa parole était avec autorité.
33 A cikin majami’ar, akwai wani mutum mai aljani, wani mugun ruhu. Mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce,
Et il y avait dans la synagogue un homme qui avait un esprit de démon immonde; et il s’écria à haute voix,
34 “Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki na Allah!”
disant: Ha! qu’y a-t-il entre nous et toi, Jésus Nazarénien? Es-tu venu pour nous détruire? Je te connais, qui tu es: le Saint de Dieu.
35 Yesu ya tsawata masa da ƙarfin cewa, “Yi shiru! Ka fita daga cikinsa!” Sai aljanin ya fyaɗa mutumin da ƙasa a gabansu duka, sa’an nan ya fita, ya bar shi ba wani rauni.
Et Jésus le tança, disant: Tais-toi, et sors de lui. Et le démon, l’ayant jeté au milieu [de tous], sortit de lui sans lui avoir fait aucun mal.
36 Dukan mutanen suka yi mamaki, suka ce wa junansu, “Wace irin koyarwa ce haka? Da ƙarfi da iko, yana ba wa mugayen ruhohin umarni suna kuma fita!”
Et ils furent tous saisis d’étonnement, et ils parlaient entre eux, disant: Quelle parole est celle-ci? car il commande avec autorité et puissance aux esprits immondes, et ils sortent.
37 Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a cikin ƙasar.
Et sa renommée se répandait dans tous les lieux d’alentour.
38 Yesu ya fita daga majami’ar, ya tafi gidan Siman. Surukar Siman kuwa tana fama da zazzaɓi mai tsanani, sai suka roƙi Yesu yă taimake ta.
Et s’étant levé, [il sortit] de la synagogue et entra dans la maison de Simon. Et la belle-mère de Simon était prise d’une grosse fièvre, et on le pria pour elle.
39 Sai ya sunkuya kusa da ita, ya kuma tsawata wa zazzaɓin, sai zazzaɓin ya sāke ta. Nan take ta tashi, ta yi musu hidima.
Et s’étant penché sur elle, il tança la fièvre, et [la fièvre] la quitta; et à l’instant s’étant levée, elle les servit.
40 Rana tana fāɗuwa, sai mutane suka yi ta kawo wa Yesu dukan waɗanda suke da cuta iri-iri, sai ya ɗibiya wa kowannensu hannuwansa, ya warkar da su.
Et comme le soleil se couchait, tous ceux qui avaient des infirmes atteints de diverses maladies, les lui amenèrent; et ayant imposé les mains à chacun d’eux, il les guérit.
41 Bugu da ƙari, aljanu suka fiffita daga cikin mutane da yawa suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya kwaɓe su, ya hana su magana, don sun san cewa shi ne Kiristi.
Et les démons aussi sortaient de plusieurs, criant et disant: Tu es le Fils de Dieu. Et, les tançant, il ne leur permettait pas de parler, parce qu’ils savaient qu’il était le Christ.
42 Da gari yana wayewa, sai Yesu ya je inda ba kowa. Mutane suka yi ta nemansa, da suka zo inda yake, sai suka yi ƙoƙari su hana shi barinsu.
Et quand il fut jour, il sortit et s’en alla en un lieu désert; et les foules le recherchaient et vinrent jusqu’à lui; et elles le retenaient, afin qu’il ne s’en aille point d’auprès d’elles.
43 Amma ya ce, “Dole in yi wa’azin bisharar mulkin Allah ga sauran garuruwa, saboda wannan ne aka aiko ni.”
Mais il leur dit: Il faut que j’annonce le royaume de Dieu aux autres villes aussi; car j’ai été envoyé pour cela.
44 Sai ya dinga yin wa’azi a majami’un Yahudiya.
Et il prêchait dans les synagogues de la Galilée.

< Luka 4 >