< Luka 4 >

1 Yesu kuwa cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga Urdun, Ruhu kuma ya kai shi cikin hamada,
Now Jesus being full of the holy Spirit, returned from Jordan, and was led by the Spirit into the wilderness, being forty days tempted by the devil;
2 inda kwana arba’in, Iblis ya gwada shi. Bai ci kome ba a cikin kwanakin nan, a ƙarshensu kuwa ya ji yunwa.
and He did eat nothing in all those days: and when they were ended, at last He was hungry.
3 Iblis ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka faɗa wa wannan dutse yă zama burodi.”
And the devil said to Him, If thou art the Son of God, command this stone to become bread.
4 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba.’”
And Jesus answered him, saying, It is written, that man shall not live by bread only, but on every word of God.
5 Iblis ya kai shi can kan wani wuri mai tsawo, ya nunnuna masa a ƙyiftawar ido dukan mulkokin duniya.
And the devil taking Him up into an high mountain, shewed Him all the kingdoms of the world in an instant,
6 Ya ce masa, “Zan ba ka dukan ikonsu da darajarsu, gama ni aka danƙa wa, kuma zan bai wa duk wanda na ga dama.
and said to Him, All this power will I give thee, and the glory of them: for it is committed to me, and I give it to whomsoever I will.
7 Saboda haka in ka yi mini sujada, dukan wannan zai zama naka.”
Therefore, if thou wilt but worship me, they all shall be thine.
8 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, kuma shi kaɗai za ka bauta wa.’”
And Jesus answering him said with indignation, Get thee behind me, Satan: for it is written, Thou shalt worship the Lord thy God, and Him only shalt thou serve.
9 Sai Iblis, ya kai shi Urushalima ya sa ya tsaya a kan wuri mafi tsayi na haikali ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka yi tsalle daga nan zuwa ƙasa.
And he brought Him to Jerusalem, and set him on a battlement of the temple, and said to Him, If thou art the Son of God, cast thyself down from hence;
10 Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, su kiyaye ka da kyau;
for it is written, He shall give his angels charge concerning thee,
11 za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
to keep thee, and they shall bear thee up in their hands, least thou dash thy foot against a stone.
12 Yesu ya amsa ya ce, “An ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
And Jesus answered him, it is said, Thou shalt not tempt the Lord thy God.
13 Da Iblis ya gama dukan wannan gwajin, ya bar shi sai lokacin da wata dama ta samu.
And when the devil had ended all the temptation, he departed from Him for a time.
14 Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka.
And Jesus returned by the influence of the Spirit into Galilee: and a fame was spread through all the country round about concerning Him:
15 Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.
and He taught in their synagogues with universal applause.
16 Ya tafi Nazaret, inda aka yi renonsa. A ranar Asabbaci kuma, ya shiga majami’a kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe don yă yi karatu.
And He came to Nazareth, where He had been brought up: and according to his custom He went into the synagogue on the sabbath-day, and stood up to read.
17 Aka kuwa ba shi naɗaɗɗen littafin annabi Ishaya. Da ya buɗe, sai ya sami wurin da aka rubuta,
And there was delivered to Him the book of the prophet Esaias; and opening the book, He found the place where it was written,
18 “Ruhun Ubangiji yana kaina, domin ya shafe ni, in yi wa matalauta wa’azin bishara. Ya aiko ni in yi shelar’yanci ga’yan kurkuku, in kuma buɗe idanun makafi, in ba da’yanci ga waɗanda aka danne.
"The spirit of the Lord is upon me to the end, for which He hath anointed me: He hath sent me to publish good tidings to the poor, to heal the broken-hearted, to proclaim deliverance to the captives, and recovery of sight to the blind, to release them that are bruised,
19 In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
and to preach the acceptable year of the Lord."
20 Sai ya naɗe naɗaɗɗen littafin ya mayar wa mai hidimar, ya kuma zauna. Dukan idanun waɗanda suke a majami’ar, suka koma a kansa.
And He folded up the book, and gave it again to the minister, and sat down: and the eyes of all in the synagogue were fixed upon Him.
21 Sai ya fara ce musu, “A yau, Nassin nan, ya cika a kunnenku.”
And He said unto them, this day is this scripture fulfilled in your ears.
22 Duk suka yabe shi, suka yi mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suka yi tambaya, suna cewa, “Anya, wannan ba ɗan Yusuf ba ne?”
And they all bare witness to Him, and wondered at the gracefulness of the words, which proceeded from his mouth, and said, Is not this the son of Joseph?
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce, na san za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka! Ka kuma yi abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, a nan garinka.’”
And He said unto them, No doubt ye will apply to me this proverb, "Physician, cure thyself, and do here in thy own country what we have heard were done at Capernaum."
24 Ya ci gaba, da ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, babu annabin da ake yarda da shi a garinsa.
But, said He, indeed I must tell you, that no prophet is well received in his own country.
25 Ina tabbatar muku a zamanin Iliya, akwai gwauraye da yawa a Isra’ila, sa’ad da aka rufe sararin sama har shekara uku da rabi, aka kuma yi yunwa mai tsanani ko’ina a ƙasar.
And I assure you, there were many widows in Israel, in the days of Elias, when the heaven was shut up for three years and six months, and there was a great famine through all the land;
26 Duk da haka, ba a aiki Iliya ga ko ɗaya a cikinsu ba. Sai dai zuwa ga wata gwauruwa da take a Zarefat, a yankin Sidon.
but Elias was sent to none of those widows, but to a widow-woman at Sarepta in the territory of Sidon.
27 Akwai kuma mutane da yawa a Isra’ila masu kuturta a zamanin annabi Elisha, amma ba ko ɗayansu da aka tsarkake sai Na’aman mutumin Suriyan nan kaɗai.”
There were also many lepers in Israel, in the time of Elisha the prophet, and none of them was cleansed; but Naaman the Syrian was.
28 Dukan mutanen da suke cikin majami’a suka fusata ƙwarai da jin wannan.
And all the synagogue were filled with rage, when they heard these things,
29 Suka tashi, suka fitar da Yesu bayan gari, suka kai shi goshin tudun da aka gina garin, don su ture shi ƙasa,
and they rose up and drove Him out of the city, and dragged Him to the brow of the hill, on which their city was built, in order to throw Him down the precipice.
30 amma sai ya bi ta tsakiyar taron ya yi tafiyarsa.
But He passed through the midst of them, and went away.
31 Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a Galili, a ranar Asabbaci kuma, ya fara koya wa mutane.
And He came down to Capernaum a city of Galilee, and taught them on the sabbath-days,
32 Suka yi ta mamakin koyarwarsa, domin saƙonsa yana da iko.
and they were astonished at his doctrine; for He spake with authority.
33 A cikin majami’ar, akwai wani mutum mai aljani, wani mugun ruhu. Mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce,
And there was a man in the synagogue possessed by the spirit of an impure demon, and he cried out with a loud voice,
34 “Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki na Allah!”
saying, Let us alone, what hast thou to do with us, Jesus of Nazareth? art thou come to destroy us? I know who thou art, the holy one of God:
35 Yesu ya tsawata masa da ƙarfin cewa, “Yi shiru! Ka fita daga cikinsa!” Sai aljanin ya fyaɗa mutumin da ƙasa a gabansu duka, sa’an nan ya fita, ya bar shi ba wani rauni.
but Jesus rebuked him, saying, Be silent, and come out of him. And the demon threw him down in the midst of the assembly, and came out of him, having done him no hurt.
36 Dukan mutanen suka yi mamaki, suka ce wa junansu, “Wace irin koyarwa ce haka? Da ƙarfi da iko, yana ba wa mugayen ruhohin umarni suna kuma fita!”
And they were all amazed, and said one to another, What a speech is this? for with authority and power He commandeth the impure spirits, and they come out!
37 Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a cikin ƙasar.
And his fame spread all over the country round about.
38 Yesu ya fita daga majami’ar, ya tafi gidan Siman. Surukar Siman kuwa tana fama da zazzaɓi mai tsanani, sai suka roƙi Yesu yă taimake ta.
And He rose up and went out of the synagogue, and came into the house of Simon: now Simon's wife's mother had a violent fever, and they intreated Him on her behalf.
39 Sai ya sunkuya kusa da ita, ya kuma tsawata wa zazzaɓin, sai zazzaɓin ya sāke ta. Nan take ta tashi, ta yi musu hidima.
And he stood over her, and rebuked the fever, and it left her: and immediately she arose and waited upon them.
40 Rana tana fāɗuwa, sai mutane suka yi ta kawo wa Yesu dukan waɗanda suke da cuta iri-iri, sai ya ɗibiya wa kowannensu hannuwansa, ya warkar da su.
And at sun-set all that had any persons sick of any diseases, brought them to Him: and He laid his hands on every one of them and healed them.
41 Bugu da ƙari, aljanu suka fiffita daga cikin mutane da yawa suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya kwaɓe su, ya hana su magana, don sun san cewa shi ne Kiristi.
And demons also came out from many, crying out, Thou art the Messiah the Son of God. And He rebuked them, and suffered them not to say, that they knew Him to be the Christ.
42 Da gari yana wayewa, sai Yesu ya je inda ba kowa. Mutane suka yi ta nemansa, da suka zo inda yake, sai suka yi ƙoƙari su hana shi barinsu.
And when the day was coming on, He went out and retired into a solitary place; and the people sought for Him, and came to Him, and would fain have detained Him, that He might not go from them.
43 Amma ya ce, “Dole in yi wa’azin bisharar mulkin Allah ga sauran garuruwa, saboda wannan ne aka aiko ni.”
But He said unto them, I must preach the kingdom of God to other cities also: for therefore am I sent.
44 Sai ya dinga yin wa’azi a majami’un Yahudiya.
So He went on preaching in the synagogues of Galilee.

< Luka 4 >