< Luka 4 >

1 Yesu kuwa cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga Urdun, Ruhu kuma ya kai shi cikin hamada,
Then Jesus, being full of the Holy Spirit, returned from the Jordan River, and was led by the Spirit in the wilderness,
2 inda kwana arba’in, Iblis ya gwada shi. Bai ci kome ba a cikin kwanakin nan, a ƙarshensu kuwa ya ji yunwa.
where for forty days he was tempted by the devil. He ate nothing during those days, and at the end of that time he was hungry.
3 Iblis ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka faɗa wa wannan dutse yă zama burodi.”
The devil said to him, “If you are the Son of God, command this stone to become bread.”
4 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da abinci kaɗai mutum zai rayu ba.’”
Jesus answered him, “It is written, 'Man does not live on bread alone.'”
5 Iblis ya kai shi can kan wani wuri mai tsawo, ya nunnuna masa a ƙyiftawar ido dukan mulkokin duniya.
Then the devil led Jesus up and showed him all the kingdoms of the world in an instant of time.
6 Ya ce masa, “Zan ba ka dukan ikonsu da darajarsu, gama ni aka danƙa wa, kuma zan bai wa duk wanda na ga dama.
The devil said to him, “I will give to you all this authority and all their splendor, for they have been given to me, and I can give it to anyone I want.
7 Saboda haka in ka yi mini sujada, dukan wannan zai zama naka.”
So then, if you will bow down and worship me, it will be yours.”
8 Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, kuma shi kaɗai za ka bauta wa.’”
But Jesus answered and said to him, “It is written, 'You will worship the Lord your God, and you will serve only him.'”
9 Sai Iblis, ya kai shi Urushalima ya sa ya tsaya a kan wuri mafi tsayi na haikali ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka yi tsalle daga nan zuwa ƙasa.
Then the devil led Jesus to Jerusalem and put him on the very highest point of the temple building, and said to him, “If you are the Son of God, throw yourself down from here.
10 Gama a rubuce yake, “‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai, su kiyaye ka da kyau;
For it is written, 'He will give orders to his angels regarding you, to protect you,'
11 za su tallafe ka da hannuwansu, don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’”
and, 'They will lift you up in their hands, so that you will not strike your foot against a stone.'”
12 Yesu ya amsa ya ce, “An ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’”
Answering him, Jesus said, “It is said, 'Do not put the Lord your God to the test.'”
13 Da Iblis ya gama dukan wannan gwajin, ya bar shi sai lokacin da wata dama ta samu.
When the devil had finished testing Jesus, he went away and left him until another time.
14 Yesu ya koma Galili cikin ikon Ruhu. Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a ƙauyuka.
Then Jesus returned to Galilee in the power of the Spirit, and news about him spread throughout the entire surrounding region.
15 Ya yi ta koyarwa a majami’unsu, kowa kuwa ya yabe shi.
Then he began to teach in their synagogues and he was praised by all.
16 Ya tafi Nazaret, inda aka yi renonsa. A ranar Asabbaci kuma, ya shiga majami’a kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe don yă yi karatu.
He came into Nazareth, where he had been raised, and as was his custom, he entered the synagogue on the Sabbath day and he stood up to read aloud.
17 Aka kuwa ba shi naɗaɗɗen littafin annabi Ishaya. Da ya buɗe, sai ya sami wurin da aka rubuta,
The scroll of the prophet Isaiah was handed to him. He opened the scroll and found the place where it was written,
18 “Ruhun Ubangiji yana kaina, domin ya shafe ni, in yi wa matalauta wa’azin bishara. Ya aiko ni in yi shelar’yanci ga’yan kurkuku, in kuma buɗe idanun makafi, in ba da’yanci ga waɗanda aka danne.
“The Spirit of the Lord is upon me, because he anointed me to tell good news to the poor. He has sent me to proclaim freedom to the captives, and recovery of sight to the blind, to set free those who are oppressed,
19 In yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji.”
to proclaim the year of the Lord's favor.”
20 Sai ya naɗe naɗaɗɗen littafin ya mayar wa mai hidimar, ya kuma zauna. Dukan idanun waɗanda suke a majami’ar, suka koma a kansa.
Then he rolled up the scroll, gave it back to the attendant, and sat down. The eyes of all in the synagogue were fixed on him.
21 Sai ya fara ce musu, “A yau, Nassin nan, ya cika a kunnenku.”
He began to speak to them, “Today this scripture has been fulfilled in your hearing.”
22 Duk suka yabe shi, suka yi mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suka yi tambaya, suna cewa, “Anya, wannan ba ɗan Yusuf ba ne?”
Everyone there spoke well of him and they were amazed at the gracious words which were coming out of his mouth, and they asked, “Is this not the son of Joseph?”
23 Yesu ya ce musu, “Tabbatacce, na san za ku faɗa mini karin maganan nan, ‘Likita, warkar da kanka! Ka kuma yi abin da muka ji ka yi a Kafarnahum, a nan garinka.’”
He said to them, “Surely you will say this proverb to me, 'Doctor, heal yourself. Whatever we heard that you did in Capernaum, do the same in your hometown.'”
24 Ya ci gaba, da ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, babu annabin da ake yarda da shi a garinsa.
But he said, “Truly I say to you, no prophet is received in his own hometown.
25 Ina tabbatar muku a zamanin Iliya, akwai gwauraye da yawa a Isra’ila, sa’ad da aka rufe sararin sama har shekara uku da rabi, aka kuma yi yunwa mai tsanani ko’ina a ƙasar.
But in truth I tell you that there were many widows in Israel during the time of Elijah, when the sky was shut up for three years and six months, and a great famine came upon all the land.
26 Duk da haka, ba a aiki Iliya ga ko ɗaya a cikinsu ba. Sai dai zuwa ga wata gwauruwa da take a Zarefat, a yankin Sidon.
But Elijah was sent to none of them, but only to Zarephath in Sidon, to a widow living there.
27 Akwai kuma mutane da yawa a Isra’ila masu kuturta a zamanin annabi Elisha, amma ba ko ɗayansu da aka tsarkake sai Na’aman mutumin Suriyan nan kaɗai.”
There were many lepers in Israel during the time of Elisha the prophet, but none of them were healed except Naaman the Syrian.”
28 Dukan mutanen da suke cikin majami’a suka fusata ƙwarai da jin wannan.
All the people in the synagogue were filled with rage when they heard these things.
29 Suka tashi, suka fitar da Yesu bayan gari, suka kai shi goshin tudun da aka gina garin, don su ture shi ƙasa,
They got up, forced him out of the town, and led him to the cliff of the hill on which their town was built, so they might throw him off the cliff.
30 amma sai ya bi ta tsakiyar taron ya yi tafiyarsa.
But he passed through the middle of them and he went to another place.
31 Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a Galili, a ranar Asabbaci kuma, ya fara koya wa mutane.
Then he went down to Capernaum, a city in Galilee, and he began to teach them on the Sabbath.
32 Suka yi ta mamakin koyarwarsa, domin saƙonsa yana da iko.
They were astonished at his teaching, because he spoke with authority.
33 A cikin majami’ar, akwai wani mutum mai aljani, wani mugun ruhu. Mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce,
Now in the synagogue there was a man who had the spirit of an unclean demon, and he cried out with a loud voice,
34 “Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne don ka hallaka mu? Na san wane ne kai, Mai Tsarki na Allah!”
“Ah! What do we have to do with you, Jesus of Nazareth? Have you come to destroy us? I know who you are—the Holy One of God!”
35 Yesu ya tsawata masa da ƙarfin cewa, “Yi shiru! Ka fita daga cikinsa!” Sai aljanin ya fyaɗa mutumin da ƙasa a gabansu duka, sa’an nan ya fita, ya bar shi ba wani rauni.
Jesus rebuked the demon, saying, “Do not speak! Come out of him!” When the demon had thrown the man down in the middle of them, he came out of him, and did not harm him in any way.
36 Dukan mutanen suka yi mamaki, suka ce wa junansu, “Wace irin koyarwa ce haka? Da ƙarfi da iko, yana ba wa mugayen ruhohin umarni suna kuma fita!”
All the people were very amazed, and they kept talking about it with one another. They said, “What kind of words are these? He commands the unclean spirits with authority and power and they come out.”
37 Labarinsa kuwa ya bazu ko’ina a cikin ƙasar.
So news about him began to spread into every part of the surrounding region.
38 Yesu ya fita daga majami’ar, ya tafi gidan Siman. Surukar Siman kuwa tana fama da zazzaɓi mai tsanani, sai suka roƙi Yesu yă taimake ta.
Then Jesus left the synagogue and entered into the house of Simon. Now Simon's mother-in-law was suffering with a high fever, and they pleaded with him on her behalf.
39 Sai ya sunkuya kusa da ita, ya kuma tsawata wa zazzaɓin, sai zazzaɓin ya sāke ta. Nan take ta tashi, ta yi musu hidima.
So he stood over her and rebuked the fever, and it left her. Immediately she got up and started serving them.
40 Rana tana fāɗuwa, sai mutane suka yi ta kawo wa Yesu dukan waɗanda suke da cuta iri-iri, sai ya ɗibiya wa kowannensu hannuwansa, ya warkar da su.
When the sun was setting, people brought to Jesus everyone who was sick with various kinds of diseases. He laid his hands on every one of them and healed them.
41 Bugu da ƙari, aljanu suka fiffita daga cikin mutane da yawa suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya kwaɓe su, ya hana su magana, don sun san cewa shi ne Kiristi.
Demons also came out from many of them, crying out and saying, “You are the Son of God!” Jesus rebuked the demons and would not let them speak, because they knew that he was the Christ.
42 Da gari yana wayewa, sai Yesu ya je inda ba kowa. Mutane suka yi ta nemansa, da suka zo inda yake, sai suka yi ƙoƙari su hana shi barinsu.
When daybreak came, he went out into a solitary place. Crowds of people were looking for him and came to the place where he was. They tried to keep him from going away from them.
43 Amma ya ce, “Dole in yi wa’azin bisharar mulkin Allah ga sauran garuruwa, saboda wannan ne aka aiko ni.”
But he said to them, “I must also preach the good news about the kingdom of God to many other cities, because this is the reason I was sent here.”
44 Sai ya dinga yin wa’azi a majami’un Yahudiya.
Then he continued to preach in the synagogues throughout Judea.

< Luka 4 >