< Luka 3 >

1 A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Kaisar Tiberiyus, a lokacin Buntus Bilatus ne gwamnar Yahudiya, Hiridus kuma yana sarautar Galili, ɗan’uwansa Filibus yana sarautar Ituriya da Tarakunitis, Lisaniyas kuma yana sarautar Abiline.
E no anno quinze do imperio de Tiberio Cesar, sendo Poncio Pilatos presidente da Judea, Herodes tetrarcha da Galilea, e seu irmão Philippe tetrarcha da Iturea e da provincia de Traconites, e Lysaneas tetrarcha da Abylinia,
2 A lokacin ne Annas da Kayifas suke manyan firistoci. Sai maganar Allah ta zo wa Yohanna, ɗan Zakariya a hamada.
Sendo Annás e Caiphás summos sacerdotes, veiu no deserto a palavra de Deus a João, filho de Zacharias.
3 Ya zaga dukan ƙasar da take kewaye da Urdun, yana wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
E percorreu toda a terra ao redor do Jordão, prégando o baptismo de arrependimento, para o perdão dos peccados;
4 Kamar yadda yake a rubuce a littafin annabi Ishaya. “Muryar mai kira a hamada, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.
Segundo o que está escripto no livro das palavras do propheta Isaias, que diz: Voz do que clama no deserto: Preparae o caminho do Senhor; endireitae as suas veredas.
5 Za a cike kowane kwari, a farfashe kowane dutse da kowane tudu. Za a miƙe hanyoyin da suka karkace, a gyaggyara hanyoyi masu gargaɗa su zama sumul.
Todo o valle se encherá, e todo o monte e outeiro se abaixará; e os caminhos tortos se endireitarão, e os caminhos escabrosos se aplanarão;
6 Dukan’yan Adam kuwa za su ga ceton Allah!’”
E toda a carne verá a salvação de Deus.
7 Yohanna ya ce wa taron da suke zuwa domin yă yi musu baftisma, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku, ku guje wa fushin nan mai zuwa?
Dizia pois João á multidão que sahia a ser baptizada por elle: Raça de viboras, quem vos ensinou a fugir da ira que está para vir?
8 Ku yi ayyukan da suka dace da tuba. Kada ma ku yi tunani za ku iya ce wa kanku, ‘Ai, muna da mahaifinmu Ibrahim.’ Ina gaya muku cewa daga cikin duwatsun nan Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim.
Dae pois fructos dignos de arrependimento, e não comeceis a dizer em vós mesmos: Temos Abrahão por pae; porque eu vos digo que até d'estas pedras pode Deus suscitar filhos a Abrahão.
9 An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.”
E tambem já está posto o machado á raiz das arvores; toda a arvore, pois, que não dá bom fructo, corta-se e lança-se no fogo.
10 Sai taron suka tambaye shi, suka ce “Me za mu yi ke nan?”
E a multidão o interrogava, dizendo: Que faremos pois?
11 Ya amsa ya ce, “Ya kamata, mutumin da yake da riguna biyu, yă raba da wanda ba shi da riga, mai abinci kuma yă yi haka.”
E, respondendo elle, disse-lhes: Quem tiver duas tunicas, reparta com o que não tem, e quem tiver alimentos faça da mesma maneira.
12 Masu karɓar haraji ma suka zo, domin a yi musu baftisma. Suka yi tambaya, suka ce “Malam, me ya kamata mu yi?”
E chegaram tambem uns publicanos, para serem baptizados, e disseram-lhe: Mestre, que devemos fazer?
13 Ya ce musu, “Kada ku karɓa fiye da abin da aka ce a karɓa.”
E elle lhes disse: Não peçaes mais do que o que vos está ordenado.
14 Sai waɗansu sojoji suka tambaye shi, “Mu fa? Me ya kamata mu yi?” Sai ya amsa ya ce, “Kada ku ƙwace kuɗin mutane, kada kuma ku yi shaidar ƙarya. Ku yi haƙuri da abin da ake biyanku.”
E uns soldados o interrogaram tambem, dizendo: E nós que faremos? E elle lhes disse: Não trateis mal, nem defraudeis alguem, e contentae-vos com o vosso soldo.
15 Mutane suka zuba ido, suna kuma tunani a zuciyarsu, ko Yohanna ne Kiristi wanda ake sauraron zuwansa.
E, estando o povo em expectação, e pensando todos de João, em seus corações, se porventura seria o Christo,
16 Yohanna ya amsa musu duka ya ce, “Ina muku baftisma da ruwa. Amma wani wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban ma isa in kunce igiyar takalmansa ba. Shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da wuta kuma.
Respondeu João a todos, dizendo: Eu, na verdade, baptizo-vos com agua, mas vem um mais poderoso do que eu, a quem eu não sou digno de desatar a correia das alparcas; esse vos baptizará com o Espirito Sancto e com fogo.
17 Matankaɗinsa yana a hannunsa don yă tankaɗe sussukarsa ya kuma tattara alkama cikin rumbunsa, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
E a sua pá está em sua mão; e limpará a sua eira, e ajuntará o trigo no seu celleiro, porém queimará a palha com fogo que nunca se apaga.
18 Da kalmomi masu yawa Yohanna ya yi wa mutane gargaɗi, ya kuma yi musu wa’azin bishara.
E assim, admoestando, muitas outras coisas tambem annunciava ao povo.
19 Amma da Yohanna ya tsawata wa Hiridus mai mulki saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa, da kuma dukan sauran mugayen abubuwan da ya yi,
Sendo, porém, o tetrarcha Herodes reprehendido por elle por causa de Herodias, mulher de seu irmão Philippe, e por todas as maldades que Herodes tinha feito,
20 Hiridus dai ya ƙara ɓata al’amarin. Ya sa a kulle Yohanna a kurkuku.
Accrescentou a todas as outras ainda esta, de encerrar João n'um carcere.
21 Sa’ad da ake wa dukan mutane baftisma, sai aka yi wa Yesu shi ma. Da yana cikin addu’a, sai sama ya buɗe,
E aconteceu que, como todo o povo fosse baptizado, e sendo baptizado tambem Jesus, e orando, abriu-se o céu,
22 Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauko masa a wata siffa, kamar kurciya. Sai murya ta fito daga sama, ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, kai ne kuma kana faranta mini zuciya ƙwarai.”
E o Espirito Sancto desceu sobre elle em forma corporea, como uma pomba; e ouviu-se uma voz do céu, que dizia: Tu és o meu filho amado, em ti me tenho comprazido.
23 To, Yesu kansa yana da shekaru kusan talatin da haihuwa sa’ad da ya fara aikinsa. An ɗauka shi ɗan Yusuf ne, ɗan Heli,
E o mesmo Jesus começava a ser de quasi trinta annos, sendo (como se cuidava) filho de José, e José de Heli,
24 ɗan Mattat, ɗan Lawi, ɗan Melki, ɗan Yannai, ɗan Yusuf,
e Heli de Matthat, e Matthat de Levi, e Levi de Melchi, e Melchi de Joanna, e Joanna de José,
25 ɗan Mattatiyas, ɗan Amos, ɗan Nahum, ɗan Esli, ɗan Naggai,
e José de Mattathias, e Mattathias de Amós, e Amós de Naum, e Naum de Essi, e Essi de Naggai,
26 ɗan Ma’at, ɗan Mattatiyas, ɗan Semeyin, ɗan Yosek, ɗan Yoda,
e Naggai de Maath, e Maath de Mattathias, e Mattathias de Semei, e Semei de José, e José de Juda,
27 ɗan Yowanan, ɗan Resa, ɗan Zerubbabel, ɗan Sheyaltiyel, ɗan Neri,
e Juda de Johanna, e Johanna de Rhesa, e Rhesa de Zorobabel, e Zorobabel de Salathiel, e Salathiel de Neri,
28 ɗan Melki, ɗan Addi, ɗan Kosam, ɗan Elmadam, ɗan Er,
e Neri de Melchi, e Melchi de Addi, e Addi de Cozam, e Cozam de Elmodam, e Elmodam de Er,
29 ɗan Yoshuwa, ɗan Eliyezer, ɗan Yorim, ɗan Mattat, ɗan Lawi,
e Er de José, e José de Eliezer, e Eliezer de Jorim, e Jorim de Matthat, e Matthat de Levi,
30 ɗan Simeyon, ɗan Yahuda, ɗan Yusuf, ɗan Yonam, ɗan Eliyakim,
e Levi de Simeon, e Simeon de Juda, e Juda de José, e José de Jonan, e Jonan de Eliakim,
31 ɗan Meleya, ɗan Menna, ɗan Mattata, ɗan Natan, ɗan Dawuda,
e Eliakim de Melea, e Melea de Mainan, e Mainan de Matthata, e Matthata de Nathan, e Nathan de David,
32 ɗan Yesse, ɗan Obed, ɗan Bowaz, ɗan Salmon, ɗan Nashon,
e David de Jesse, e Jesse de Obed, e Obed de Booz, e Booz de Salmon, e Salmon de Naasson,
33 ɗan Amminadab, ɗan Ram, ɗan Hezron, ɗan Ferez, ɗan Yahuda,
e Naasson de Aminadab, e Aminadab de Arão, e Arão de Esrom, e Esrom de Fares, e Fares de Juda,
34 ɗan Yaƙub, ɗan Ishaku, ɗan Ibrahim, ɗan Tera, ɗan Nahor,
e Juda de Jacob, e Jacob de Isaac, e Isaac de Abrahão, e Abrahão de Thare, e Thare de Nachor,
35 ɗan Serug, ɗan Reyu, ɗan Feleg, ɗan Eber, ɗan Sala,
e Nachor de Saruch, e Saruch de Ragau, e Ragau de Faleg, e Faleg de Heber, e Heber de Sala,
36 ɗan Kainan, ɗan Arfakshad, ɗan Shem, ɗan Nuhu, ɗan Lamek,
e Sala de Cainan, e Cainan de Arfaxad, e Arfaxad de Sem, e Sem de Noé, e Noé de Lamech,
37 ɗan Metusela, ɗan Enok, ɗan Yared, ɗan Mahalalel, ɗan Kainan,
e Lamech de Mathusala, e Mathusala de Henoch, e Henoch de Jared, e Jared de Maleleel, e Maleleel de Cainan,
38 ɗan Enosh, ɗan Shitu, ɗan Adamu, ɗan Allah.
e Cainan de Henos, e Henos de Seth, e Seth de Adão, e Adão de Deus.

< Luka 3 >