< Luka 3 >

1 A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Kaisar Tiberiyus, a lokacin Buntus Bilatus ne gwamnar Yahudiya, Hiridus kuma yana sarautar Galili, ɗan’uwansa Filibus yana sarautar Ituriya da Tarakunitis, Lisaniyas kuma yana sarautar Abiline.
En l'an quinze du règne de Tibère César, — Ponce-Pilate étant procurateur de la Judée, — Hérode, tétrarque de la Galilée, —Philippe, son frère, tétrarque de l'Iturée et des terres de la Trachonite, — Lysanias, tétrarque de l'Abilène, —
2 A lokacin ne Annas da Kayifas suke manyan firistoci. Sai maganar Allah ta zo wa Yohanna, ɗan Zakariya a hamada.
sous le pontificat de Banne et de Kaïphe, la parole de Dieu fut adressée à Jean, fils de Zaccharie, dans le désert.
3 Ya zaga dukan ƙasar da take kewaye da Urdun, yana wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
Et Jean s'en alla dans toute la région du Jourdain, prêchant un baptême de repentance pour la rémission des péchés,
4 Kamar yadda yake a rubuce a littafin annabi Ishaya. “Muryar mai kira a hamada, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.
ainsi que cela est écrit au livre des paroles du prophète Ésaïe: «Une voix crie dans le désert: Préparez la voie du Seigneur, Aplanissez ses sentiers;
5 Za a cike kowane kwari, a farfashe kowane dutse da kowane tudu. Za a miƙe hanyoyin da suka karkace, a gyaggyara hanyoyi masu gargaɗa su zama sumul.
Toute vallée sera comblée; Toute montagne et toute colline seront abaissées; Les voies tortueuses seront changées en droits chemins; Et les voies rocailleuses en routes unies;
6 Dukan’yan Adam kuwa za su ga ceton Allah!’”
Et toute chair verra le salut de Dieu»
7 Yohanna ya ce wa taron da suke zuwa domin yă yi musu baftisma, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku, ku guje wa fushin nan mai zuwa?
Aux foules qui accouraient pour être baptisées par lui, il disait: «Engeance de vipères, qui vous a appris à fuir la colère à venir?
8 Ku yi ayyukan da suka dace da tuba. Kada ma ku yi tunani za ku iya ce wa kanku, ‘Ai, muna da mahaifinmu Ibrahim.’ Ina gaya muku cewa daga cikin duwatsun nan Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim.
Produisez donc des fruits dignes de la repentance, et n'allez pas dire en vous-mêmes: Nous avons pour père Abraham; car je vous le dis, Dieu peut faire surgir, des pierres que voici, des enfants à Abraham.
9 An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.”
Déjà la cognée touche la racine des arbres. Tout arbre donc qui ne produit pas de bon fruit, sera coupé et jeté au feu.» —
10 Sai taron suka tambaye shi, suka ce “Me za mu yi ke nan?”
«Qu'avons-nous à faire?» lui demandèrent alors les multitudes.
11 Ya amsa ya ce, “Ya kamata, mutumin da yake da riguna biyu, yă raba da wanda ba shi da riga, mai abinci kuma yă yi haka.”
Il leur répondit par ces paroles: «Que celui qui possède deux tuniques en donne une à celui qui n'en a pas et que celui qui a des aliments pour se nourrir fasse de même.»
12 Masu karɓar haraji ma suka zo, domin a yi musu baftisma. Suka yi tambaya, suka ce “Malam, me ya kamata mu yi?”
Des publicains vinrent pour être baptisés et lui dirent aussi: «Maître, qu'avons-nous à faire?» —
13 Ya ce musu, “Kada ku karɓa fiye da abin da aka ce a karɓa.”
«N'exigez rien de plus, leur répondit-il, que ce qui vous a été prescrit.»
14 Sai waɗansu sojoji suka tambaye shi, “Mu fa? Me ya kamata mu yi?” Sai ya amsa ya ce, “Kada ku ƙwace kuɗin mutane, kada kuma ku yi shaidar ƙarya. Ku yi haƙuri da abin da ake biyanku.”
Des soldats aussi le questionnèrent: «Et nous, qu'avons-nous à faire?» A eux il dit: «Ne faites violence à personne; ne faites tort à personne; contentez-vous de votre paye.»
15 Mutane suka zuba ido, suna kuma tunani a zuciyarsu, ko Yohanna ne Kiristi wanda ake sauraron zuwansa.
Le peuple était en suspens; et chacun se demandait, dans le secret de son coeur, si Jean n'était pas peut-être le Christ.
16 Yohanna ya amsa musu duka ya ce, “Ina muku baftisma da ruwa. Amma wani wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban ma isa in kunce igiyar takalmansa ba. Shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da wuta kuma.
Pour répondre à tous, Jean dit: «Moi, je vous baptise d'eau; mais il va venir celui qui est plus puissant que moi; je ne suis pas même digne de délier la courroie de ses sandales; lui, vous baptisera avec l'Esprit saint et le feu.
17 Matankaɗinsa yana a hannunsa don yă tankaɗe sussukarsa ya kuma tattara alkama cikin rumbunsa, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
Il a le van dans la main pour nettoyer son aire et rassembler le froment dans son grenier; mais la paille il la brûlera au feu inextinguible.»
18 Da kalmomi masu yawa Yohanna ya yi wa mutane gargaɗi, ya kuma yi musu wa’azin bishara.
C'est ainsi qu'il annonçait la Bonne Nouvelle au peuples par des exhortations nombreuses et variées.
19 Amma da Yohanna ya tsawata wa Hiridus mai mulki saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa, da kuma dukan sauran mugayen abubuwan da ya yi,
Le tétrarque Hérode, cependant, ayant été repris par lui tant au sujet d'Hérodiade, femme de son frère, qu'au sujet des mille crimes qu'il avait commis,
20 Hiridus dai ya ƙara ɓata al’amarin. Ya sa a kulle Yohanna a kurkuku.
ajouta encore celui-ci à tous les autres: il fit jeter Jean en prison.
21 Sa’ad da ake wa dukan mutane baftisma, sai aka yi wa Yesu shi ma. Da yana cikin addu’a, sai sama ya buɗe,
Or tout le peuple ayant reçu le baptême, et Jésus aussi ayant été baptisé, il advint que le ciel s'ouvrit, pendant qu'il priait,
22 Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauko masa a wata siffa, kamar kurciya. Sai murya ta fito daga sama, ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, kai ne kuma kana faranta mini zuciya ƙwarai.”
et que l'Esprit saint descendit sur lui sous une forme corporelle, sous la figure d'une colombe; et une voix vint du ciel: «Tu es mon Fils bien-aimé, en toi je me complais.»
23 To, Yesu kansa yana da shekaru kusan talatin da haihuwa sa’ad da ya fara aikinsa. An ɗauka shi ɗan Yusuf ne, ɗan Heli,
Jésus, en ce commencement, avait environ trente ans et passait pour être le fils de Joseph, Fils d'Héli,
24 ɗan Mattat, ɗan Lawi, ɗan Melki, ɗan Yannai, ɗan Yusuf,
Fils de Maththath, Fils de Lévi, Fils de Melchi, Fils de Jannaï, Fils de Joseph,
25 ɗan Mattatiyas, ɗan Amos, ɗan Nahum, ɗan Esli, ɗan Naggai,
Fils de Mattathias, Fils d'Amos, Fils de Naoum, Fils d'Eslei, Fils de Nangaï,
26 ɗan Ma’at, ɗan Mattatiyas, ɗan Semeyin, ɗan Yosek, ɗan Yoda,
Fils de Maath, Fils de Mattathias, Fils de Semeein, Fils de Josech, Fils de Joda,
27 ɗan Yowanan, ɗan Resa, ɗan Zerubbabel, ɗan Sheyaltiyel, ɗan Neri,
Fils de Joanan, Fils de Rèsa, Fils de Zorobabel, Fils de Salathiel, Fils de Nèrei,
28 ɗan Melki, ɗan Addi, ɗan Kosam, ɗan Elmadam, ɗan Er,
Fils de Melchei, Fils d'Addei, Fils de Kosam, Fils de Elmadam, Fils de Hèr,
29 ɗan Yoshuwa, ɗan Eliyezer, ɗan Yorim, ɗan Mattat, ɗan Lawi,
Fils de Jésus, Fils d'Éliézer, Fils de Jorem, Fils de Maththath, Fils de Lévi,
30 ɗan Simeyon, ɗan Yahuda, ɗan Yusuf, ɗan Yonam, ɗan Eliyakim,
Fils de Siméon, Fils de Judas, Fils de Joseph, Fils de Jonam, Fils d'Éliakim, Fils de Méléa,
31 ɗan Meleya, ɗan Menna, ɗan Mattata, ɗan Natan, ɗan Dawuda,
Fils de Menna, Fils de Mattatha, Fils de Natham, Fils de David,
32 ɗan Yesse, ɗan Obed, ɗan Bowaz, ɗan Salmon, ɗan Nashon,
Fils de Jessaï, Fils de Jobed, Fils de Boos, Fils de Sala, Fils de Naasson,
33 ɗan Amminadab, ɗan Ram, ɗan Hezron, ɗan Ferez, ɗan Yahuda,
Fils d'Aminadab, Fils d'Admein, Fils d'Ami, Fils d'Esrom, Fils de Pharès, Fils de Judas,
34 ɗan Yaƙub, ɗan Ishaku, ɗan Ibrahim, ɗan Tera, ɗan Nahor,
Fils de Jacob, Fils d'Isaac, Fils d'Abraham, Fils de Unira, Fils de Nachor, Fils de Serouch,
35 ɗan Serug, ɗan Reyu, ɗan Feleg, ɗan Eber, ɗan Sala,
Fils de Ragau, Fils de Phalek, Fils de Eber, Fils de Sala,
36 ɗan Kainan, ɗan Arfakshad, ɗan Shem, ɗan Nuhu, ɗan Lamek,
Fils de Kainam, Fils d'Arphaxad, Fils de Sein, Fils de Noé, Fils de Lamech,
37 ɗan Metusela, ɗan Enok, ɗan Yared, ɗan Mahalalel, ɗan Kainan,
Fils de Mathousalem. Fils d'Enoch, Fils de Jaret, Fils de Meleleèl, Fils de Kainam
38 ɗan Enosh, ɗan Shitu, ɗan Adamu, ɗan Allah.
Fils d'Enos, Fils de Seth, Fils d'Adam, Fils de Dieu.

< Luka 3 >