< Luka 3 >

1 A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Kaisar Tiberiyus, a lokacin Buntus Bilatus ne gwamnar Yahudiya, Hiridus kuma yana sarautar Galili, ɗan’uwansa Filibus yana sarautar Ituriya da Tarakunitis, Lisaniyas kuma yana sarautar Abiline.
Y mina quinse na año gui tiempo anae si Tiberio Sesat jagobietna, ya si Ponsio Pilato, güiya magalaje guiya Judea; ya si Herodes, güiya magalaje tetrarca guiya Galilea; ya y cheluña as Felipe, güiya magalaje tetrarca guiya Iturea yan y ya tanon Traconite; ya si Lisanias, güiya magalaje tetrarca guiya Abilinia;
2 A lokacin ne Annas da Kayifas suke manyan firistoci. Sai maganar Allah ta zo wa Yohanna, ɗan Zakariya a hamada.
Ya y dangculo na mamale si Annas yan si Caefas, este na tiempo, mato y sinangan Yuus gui as Juan, lajin Sacharias, gui jalomtano.
3 Ya zaga dukan ƙasar da take kewaye da Urdun, yana wa’azin baftismar tuba don gafarar zunubai.
Ya güiya mato gui todo y tano gui oriyan Jordan, jasesetmon y managpang en sinetsot para y maasiin isao.
4 Kamar yadda yake a rubuce a littafin annabi Ishaya. “Muryar mai kira a hamada, ‘Ku shirya wa Ubangiji hanya, ku miƙe hanyoyi dominsa.
Taegüije esta matugue gui leblo ni y sinangan y profeta Isaias, na ilegña: Inagangña ni y umaagang gui jalomtano: Famauleg y chalan y Señot, y cayejonña natutunas.
5 Za a cike kowane kwari, a farfashe kowane dutse da kowane tudu. Za a miƙe hanyoyin da suka karkace, a gyaggyara hanyoyi masu gargaɗa su zama sumul.
Todo y finacañada umanafanbula, yan todo y tano boca yan y manloca na ogso umanafanagpapa; yan y manechong umanafanunas, yan y chalan farangca unamafanyano.
6 Dukan’yan Adam kuwa za su ga ceton Allah!’”
Ya todo y catne ulie y satbasion Yuus.
7 Yohanna ya ce wa taron da suke zuwa domin yă yi musu baftisma, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku, ku guje wa fushin nan mai zuwa?
Enaomina ilegña ni y linajyan taotao na manmato para ufanmatagpange pot güiya: Rasan culebla, jaye jamyo fumanagüe na insuaye y binibo ni y mamamaela?
8 Ku yi ayyukan da suka dace da tuba. Kada ma ku yi tunani za ku iya ce wa kanku, ‘Ai, muna da mahaifinmu Ibrahim.’ Ina gaya muku cewa daga cikin duwatsun nan Allah zai iya tā da’ya’ya wa Ibrahim.
Chile tinegchanmiyo ni y magajet na sinetsot, ya chamiyo insigue di sumasangan nu jamyoja: Guaja tatanmame si Abraham; sa jusanganejamyo na siña, si Yuus güine gui acho janafangajulo y famaguon Abraham.
9 An riga an sa bakin gatari a gindin itatuwa, kuma duk itacen da bai ba da’ya’ya masu kyau ba, za a sare shi a jefa cikin wuta.”
Ya pagoja y gachae gaegueja gui jale y trongcon jayo sija: todo y trongcon jayo na ti mauleg tinegchañija, umautut ya umayute gui guafe.
10 Sai taron suka tambaye shi, suka ce “Me za mu yi ke nan?”
Ya y linajyan taotao mafaesen güe ya ilegñija: Pues jafajam infatinas?
11 Ya amsa ya ce, “Ya kamata, mutumin da yake da riguna biyu, yă raba da wanda ba shi da riga, mai abinci kuma yă yi haka.”
Ya manope, ilegña nu sija: Y guaja dos magaguña, unae y taya iyoña: ya y guaja naña ufatinas taegüijija.
12 Masu karɓar haraji ma suka zo, domin a yi musu baftisma. Suka yi tambaya, suka ce “Malam, me ya kamata mu yi?”
Ya manmato locue y publicano sija para ufanmatatagpange, ya ilegñija: Maestro jafa infatinasjam?
13 Ya ce musu, “Kada ku karɓa fiye da abin da aka ce a karɓa.”
Ya ilegña nu sija: Chamiyo gumagagao mas ni y esta jamyo manmatago.
14 Sai waɗansu sojoji suka tambaye shi, “Mu fa? Me ya kamata mu yi?” Sai ya amsa ya ce, “Kada ku ƙwace kuɗin mutane, kada kuma ku yi shaidar ƙarya. Ku yi haƙuri da abin da ake biyanku.”
Ya mafaesen güe locue nu y sendalo sija, ilegñija: Ya jame, jafajam infatinas? Ya mansinangane: Chamiyo mumatratrata ni jaye ni infanmanchiguit, ya magof jamyo nu y apasmiyo.
15 Mutane suka zuba ido, suna kuma tunani a zuciyarsu, ko Yohanna ne Kiristi wanda ake sauraron zuwansa.
Ya y taotao sija jananangga ya manmanjajajaso todo sija as Juan gui corasonñija, cao güiya si Jesucristo.
16 Yohanna ya amsa musu duka ya ce, “Ina muku baftisma da ruwa. Amma wani wanda ya fi ni iko yana zuwa, ban ma isa in kunce igiyar takalmansa ba. Shi zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki da wuta kuma.
Manope si Juan ya ilegña nu todosija: Guajo magajet managpapange jamyo an janom; lao mamamaela uno na mas gaeninasiña qui guajo, ya ti siña yo manmerese na jupula y coreas y sapatosña: güiya managpapange an Espiritu Santo yan guafe.
17 Matankaɗinsa yana a hannunsa don yă tankaɗe sussukarsa ya kuma tattara alkama cikin rumbunsa, amma zai ƙone yayin da wutar da ba a iya kashewa.”
Ya abanicuña gaegueja gui canaeña para unagasgas y guinecoña, ya janafandaña y trigo gui camalenña; lao usonggue y ngasan gui guafe ni ti siña upuno.
18 Da kalmomi masu yawa Yohanna ya yi wa mutane gargaɗi, ya kuma yi musu wa’azin bishara.
Ya mamagat megae na sinangan ya japredica y taotao sija ni ibangelio.
19 Amma da Yohanna ya tsawata wa Hiridus mai mulki saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa, da kuma dukan sauran mugayen abubuwan da ya yi,
Lao si Herodes, ayo magalaje tetrarca, linalatde as Juan, pot si Herodias, asaguan y cheluña as Felipe, yan pot todo y tinaelaye sija ni jafatinas si Herodes,
20 Hiridus dai ya ƙara ɓata al’amarin. Ya sa a kulle Yohanna a kurkuku.
Ya jafatinas este mas taelaye qui todo, ya maponggle si Juan gui catset.
21 Sa’ad da ake wa dukan mutane baftisma, sai aka yi wa Yesu shi ma. Da yana cikin addu’a, sai sama ya buɗe,
Ya susede, anae todo y taotao manmatagpange, si Jesus locue matagpange; ya anae manaetaegüe, mababa y langet;
22 Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauko masa a wata siffa, kamar kurciya. Sai murya ta fito daga sama, ta ce, “Kai ne Ɗana, wanda nake ƙauna, kai ne kuma kana faranta mini zuciya ƙwarai.”
Ya tumunog gui jiloña y Espiritu Santo na gaejechuraña calang paluma, ya mato un inagang guine y langet na ilegña: Jago y lajijo ni juguaeya; iyajago nae gaegue minagofjo.
23 To, Yesu kansa yana da shekaru kusan talatin da haihuwa sa’ad da ya fara aikinsa. An ɗauka shi ɗan Yusuf ne, ɗan Heli,
Ya si Jesus namaesa anae jatutujon sumetnon, güiya treinta años, ya güiya lajin José (calang jinason taotao), nu y lajin Eli,
24 ɗan Mattat, ɗan Lawi, ɗan Melki, ɗan Yannai, ɗan Yusuf,
Nu y lajin Matat nu y lajin Levi, nu y lajin Metqui, nu y lajin Jané, nu y lajin José,
25 ɗan Mattatiyas, ɗan Amos, ɗan Nahum, ɗan Esli, ɗan Naggai,
Nu y lajin Matatias nu y lajin Amos, nu y lajin Nalum, nu y lajin Eslí, nu y lajin Nagé,
26 ɗan Ma’at, ɗan Mattatiyas, ɗan Semeyin, ɗan Yosek, ɗan Yoda,
Nu y lajin Maat, nu y lajin Matatias, nu y lajin Simei, nu y lajin José, nu y lajin Juda,
27 ɗan Yowanan, ɗan Resa, ɗan Zerubbabel, ɗan Sheyaltiyel, ɗan Neri,
Nu y lajin Joana, nu y lajin Resa, nu y lajin Sorobabel, nu y lajin Salatiel, nu y lajin Neri,
28 ɗan Melki, ɗan Addi, ɗan Kosam, ɗan Elmadam, ɗan Er,
Nu y lajin Metqui, nu y lajin Adí, nu y lajin Cosam, nu y lajin Elmodan, nu y lajin Er,
29 ɗan Yoshuwa, ɗan Eliyezer, ɗan Yorim, ɗan Mattat, ɗan Lawi,
Nu y lajin Jesus, nu y lajin Elieser, nu y lajin Jorim, nu y lajin Mata, nu y lajin Levi,
30 ɗan Simeyon, ɗan Yahuda, ɗan Yusuf, ɗan Yonam, ɗan Eliyakim,
Nu y lajin Simeon, nu y lajin Juda, nu y lajin José, nu y lajin Jonan, nu y lajin Eliaquim,
31 ɗan Meleya, ɗan Menna, ɗan Mattata, ɗan Natan, ɗan Dawuda,
Nu y lajin Melea, nu y lajin Mena, nu y lajin Matata, nu y lajin Natan, nu y lajin David,
32 ɗan Yesse, ɗan Obed, ɗan Bowaz, ɗan Salmon, ɗan Nashon,
Nu y lajin Jesse, nu y lajin Obed, nu y lajin Boos, nu y lajin Salmon, nu y lajin Naason,
33 ɗan Amminadab, ɗan Ram, ɗan Hezron, ɗan Ferez, ɗan Yahuda,
Nu y lajin Aminadab, nu y lajin Aram, nu y lajin Esrom, nu y lajin Fares, nu y lajin Juda,
34 ɗan Yaƙub, ɗan Ishaku, ɗan Ibrahim, ɗan Tera, ɗan Nahor,
Nu y lajin Jacob, nu y lajin Ysaac, nu y lajin Abraham, nu y lajin Taré, nu y lajin Nacor,
35 ɗan Serug, ɗan Reyu, ɗan Feleg, ɗan Eber, ɗan Sala,
Nu y lajin Serug, nu y lajin Ragau, nu y lajin Peleg, nu y lajin Heber, nu y lajin Sela,
36 ɗan Kainan, ɗan Arfakshad, ɗan Shem, ɗan Nuhu, ɗan Lamek,
Nu y lajin Cainan, nu y lajin Arfaxat, nu y lajin Sem, nu y lajin Noe, nu y lajin Lameg,
37 ɗan Metusela, ɗan Enok, ɗan Yared, ɗan Mahalalel, ɗan Kainan,
Nu y lajin Matusalem, nu y lajin Enog, nu y lajin Jared, nu y lajin Mahalaleel, nu y lajin Cainan,
38 ɗan Enosh, ɗan Shitu, ɗan Adamu, ɗan Allah.
Nu y lajin Enos, nu y lajin Set, nu y lajin Adam, nu y lajin Yuus.

< Luka 3 >