< Luka 23 >

1 Sai dukan majalisa suka tashi, suka kai shi gaban Bilatus.
E, levantando-se toda a multidão deles, o levaram a Pilatos.
2 Suka fara zarginsa suna cewa, “Mun sami wannan mutum yana rikitar da al’ummarmu. Yana hana a biya haraji ga Kaisar. Yana kuma cewa, shi Kiristi ne, sarki kuma.”
E começaram a accusa-lo, dizendo: Havemos achado este, que perverte a nação, e proibe dar o tributo a Cesar, dizendo que ele mesmo é Cristo, o rei
3 Sai Bilatus ya tambayi Yesu ya ce, “Kai ne sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
E Pilatos perguntou-lhe, dizendo: Tu és o Rei dos judeus? E ele, respondendo, disse-lhe: Tu o dizes.
4 Sai Bilatus ya sanar wa manyan firistoci da taron ya ce, “Ni fa, ban sami wani ainihin abin zargi game wannan mutum nan ba.”
E disse Pilatos aos principais dos sacerdotes, e à multidão: Não acho culpa alguma neste homem.
5 Amma suka nace, suna cewa, “Yana tā da hankulan mutane, ko’ina a Yahudiya da koyarwarsa. Ya fara daga Galili, ga shi har ya kai nan.”
Mas eles insistiam cada vez mais, dizendo: Alvoroça o povo, ensinando por toda a Judeia, começando desde Galiléia até aqui.
6 Da Bilatus ya ji haka, sai ya yi tambaya, “Ko shi mutumin Galili ne?”
Então Pilatos, ouvindo falar da Galiléia, perguntou se aquele homem era galileu.
7 Da ya ji cewa, Yesu yana ƙarƙashin mulkin Hiridus ne, sai ya aika da shi zuwa wurin Hiridus, don a lokacin Hiridus yana Urushalima.
E, entendendo que era da jurisdição de Herodes, remeteu-o a Herodes, que também naqueles dias estava em Jerusalém.
8 Da Hiridus ya ga Yesu, sai ya yi murna ƙwarai, don tun dā ma yana marmari ya gan shi a kan abin da ya ji game da shi. Ya yi fata ya ga Yesu, yă kuma yi waɗansu ayyukan banmamaki.
E Herodes, quando viu a Jesus, alegrou-se muito; porque havia muito que desejava vê-lo, por ter ouvido dele muitas coisas; e esperava que lhe veria fazer algum sinal;
9 Ya yi masa tambayoyi masu yawa, amma Yesu bai ba shi ko amsa ba.
E interrogava-o em muitas palavras, porém ele nada lhe respondia.
10 Manyan firistoci da malaman dokoki suna tsaye a wurin, suna kawo zargi masu ƙarfi a kansa.
E estavam os principais dos sacerdotes, e os escribas, acusando-o com grande veemência.
11 Sai Hiridus da sojojinsa suka wulaƙanta shi, suka yi masa ba’a. Sa’an nan, suka sa masa babban riga, suka mai da shi wurin Bilatus.
E Herodes, com os seus soldados, desprezando-o, e escarnecendo dele, vestiu-o de uma roupa resplandecente e tornou a envia-lo a Pilatos.
12 A ranar, Hiridus da Bilatus suka zama abokan juna, don tun dā ma, su abokan gāba ne.
E no mesmo dia Pilatos e Herodes entre si se fizeram amigos; porque de antes andavam em inimizade um com o outro.
13 Bilatus ya tara manyan firistoci, da masu mulki, da mutane,
E, convocando Pilatos os principais dos sacerdotes, e os magistrados, e o povo, disse-lhes:
14 ya ce musu, “Kun kawo mini wannan mutum, a matsayin wanda yana zuga mutane su yi tawaye. Na bincike shi a gabanku, ban ga a kan me kuka kawo kararsa ba.
Haveis-me apresentado este homem como pervertedor do povo; e eis que, examinando-o na vossa presença, nenhuma culpa, das de que o acusaes, acho neste homem.
15 Haka ma Hiridus, shi ya sa ya dawo da shi nan wurinmu. Kamar yadda ku ma kun gani, ba abin da mutumin nan ya yi, da ya isa mutuwa.
Nem mesmo Herodes, porque a ele vos remeti, e eis que não tem feito coisa alguma digna de morte.
16 Saboda haka, zan yi masa bulala, in sāke shi.”
Castiga-lo-ei pois, e solta-lo-ei.
E era-lhe necessário soltar-lhes um pela festa.
18 Suka yi ihu gaba ɗaya suka ce, “A yi gaba da wannan mutum! A sake mana Barabbas!”
Porém toda a multidão clamou à uma, dizendo: fora daqui com este, e solta-nos Barrabás:
19 (Barabbas yana kurkuku saboda laifin tā da hankali a birnin, da kuma don kisankai.)
O qual fôra lançado na prisão por causa de uma sedição feita na cidade, e de um homicídio.
20 Sai Bilatus ya sāke yin musu magana don yana so ya saki Yesu.
Falou pois outra vez Pilatos, querendo soltar a Jesus.
21 Amma sai suka ci gaba da ihu, suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!”
Mas eles clamavam em contrário, dizendo: Crucifica-o, crucifica-o.
22 Ya sāke ce musu, sau na uku, “Don me? Wane laifi wannan mutum ya yi? Ni dai ban same shi da wani dalilin da ya isa a kashe shi ba. Saboda haka, zan sa a hore shi, sa’an nan in sāke shi.”
Então ele, pela terceira vez, lhes disse: Pois que mal fez este? Não acho nele culpa alguma de morte. castiga-lo-ei pois, e solta-lo-ei.
23 Amma suna ihu, suna nacewa, suna cewa, dole a gicciye shi, har ihunsu ya rinjaye shi.
Mas eles instavam com grandes gritos, pedindo que fosse crucificado. E os seus gritos, e os dos principais dos sacerdotes, redobravam.
24 Sai Bilatus ya biya bukatarsu da ya ji roƙonsu.
Então Pilatos julgou que devia fazer o que eles pediam.
25 Ya saki mutumin da aka jefa a kurkuku saboda tā da hankali, da kisankai, shi wanda suka roƙa. Sa’an nan ya ba da Yesu ga nufinsu.
E soltou-lhes o que fôra lançado na prisão por uma sedição e homicídio, que era o que pediam; porém entregou Jesus à vontade deles.
26 Sa’ad da suna tafiya da Yesu, sai wani da ake kira Siman, mutumin Sairin, yana zuwa daga ƙauye. Suka kama shi, suka aza masa gicciyen, suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen, ya bi Yesu a baya.
E, quando o iam levando, tomaram um certo Simão, Cireneu, que vinha do campo, e puseram-lhe a cruz às costas, para que a levasse após Jesus.
27 Mutane da yawa sosai suka bi shi, a cikinsu ma da mata waɗanda suka yi makoki da kuka dominsa.
E seguia-o grande multidão de povo e de mulheres, as quais batiam nos peitos, e o lamentavam.
28 Yesu ya juya, ya ce musu, “’Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka saboda ni, amma ku yi kuka saboda kanku, da kuma saboda’ya’yanku.
Porém Jesus, voltando-se para elas, disse: Filhas de Jerusalém, não choreis por mim, chorai antes por vós mesmas, e por vossos filhos.
29 Gama lokaci yana zuwa da za ku ce, ‘Masu albarka ne bakararru, wato, mata marasa haihuwa, da mahaihuwar da ba su taɓa haihuwa ba, da kuma mama da ba su taɓa shayar da nono ba!’
Porque eis que hão de vir dias em que dirão: bem-aventuradas as estéreis, e os ventres que não geraram, e os peitos que não criaram!
30 Sa’an nan “‘za su ce wa duwatsu, “Ku fāɗi a kanmu!” Za su ce wa tuddai kuma, “Ku rufe mu!”’
Então começarão a dizer aos montes: caí sobre nós, e aos outeiros: Cobri-nos.
31 Gama in mutane suna yin waɗannan abubuwa a lokacin da itace na ɗanye, me zai faru in ya bushe?”
Porque, se ao madeiro verde fazem isto, que se fará ao seco?
32 Tare da shi akwai mutum biyu masu laifi, da aka tafi da su don a gicciye.
E também conduziram outros dois, que eram malfeitores, para com ele serem mortos.
33 Da suka isa wurin da ake kira “Ƙoƙon Kai,” nan suka gicciye shi, tare da masu laifin nan, ɗaya a hannun damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
E, quando chegaram ao lugar chamado a Caveira, ali o crucificaram, e aos malfeitores, um à direita e outro à esquerda.
34 Yesu ya ce, “Ya Uba ka yi musu gafara, don ba su san abin da suke yi ba.” Suka rarraba tufafinsa ta wurin jefa ƙuri’a.
E dizia Jesus: Pai, perdôa-lhes, porque não sabem o que fazem. E, repartindo os seus vestidos, lançaram sortes.
35 Mutanen suka tsaya suna kallo. Har masu mulki ma suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, to, ya ceci kansa in shi ne Kiristi na Allah, Zaɓaɓɓe.”
E o povo estava olhando; e juntamente com eles também os príncipes zombavam dele, dizendo: Aos outros salvou, salve-se a si mesmo, se este é o Cristo, o escolhido de Deus.
36 Sojoji su ma, suka zo suka yi masa ba’a. Suka miƙa masa ruwan tsami.
E também os soldados o escarneciam, chegando-se a ele, e apresentando-lhe vinagre,
37 Suka ce, “In kai ne sarkin Yahudawa, ka ceci kanka mana.”
E dizendo: Se tu és o Rei dos judeus, salva-te a ti mesmo.
38 Bisa da shi kuma akwai rubutun da ya ce, Wannan shi ne Sarkin Yahudawa.
E também por cima dele estava um título, escrito em letras gregas, romanas, e hebraicas: ESTE É O REI DOS judeus.
39 Ɗaya daga cikin masu laifin da aka gicciye a wurin ya zazzage shi ya ce, “Shin, ba kai ne Kiristi ba? To, ka ceci kanka, ka kuma cece mu mana!”
E um dos malfeitores que estavam pendurados blasfemava dele, dizendo: Se tu és o Cristo, salva-te a ti mesmo, e a nós.
40 Amma ɗayan mai laifi ya kwaɓe shi ya ce, “Ba ka da tsoron Allah ne, wai saboda kana ƙarƙashin hukunci ɗaya tare da shi?
Respondendo, porém, o outro, repreendia-o, dizendo: Tu nem ainda temes a Deus, estando na mesma condenação?
41 Horonmu, daidai aka yi mana, sakamakon abin da muka yi ne. Amma wannan mutum, bai yi wani laifi ba.”
E nós, na verdade, com justiça, porque recebemos o que os nossos feitos mereciam; mas este nenhum mal fez.
42 Sai ya ce, “Yesu, ka tuna da ni sa’ad da ka shiga mulkinka.”
E disse a Jesus: Senhor, lembra-te de mim, quando entrares no teu reino.
43 Yesu ya amsa, ya ce masa, “Gaskiya nake faɗa maka, yau ɗin nan, za ka kasance tare da ni, a mulkina a sama.”
E disse-lhe Jesus: Em verdade te digo que hoje estarás comigo no paraíso.
44 Yanzu kuwa wajen sa’a ta shida ne, kuma duhu ya rufe ko’ina a ƙasar, har zuwa sa’a ta tara,
E era já quase a hora sexta, e houve trevas em toda a terra até a hora nona.
45 domin rana ta daina haskakawa. Labulen da yake cikin haikali kuma ya yage kashi biyu.
E o sol escureceu, e rasgou-se ao meio o véu do templo.
46 Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ya Uba, na danƙa ruhuna a hannunka.” Da ya faɗi haka, sai ya ja numfashi na ƙarshe.
E, clamando Jesus com grande voz, disse: Pai, nas tuas mãos entrego o meu espírito. E, havendo dito isto, expirou.
47 Da jarumin ya ga abin da ya faru, sai ya yabi Allah ya ce, “Gaskiya, wannan mutum mai adalci ne.”
E o centurião, vendo o que tinha acontecido, deu glória a Deus, dizendo: Na verdade, este homem era justo.
48 Da dukan mutanen da suka taru, domin shaidar waɗannan abubuwa, suka ga abin da ya faru, sai suka buga ƙirjinsu suka tafi.
E toda a multidão que se ajuntara a este espetáculo, vendo o que havia acontecido, voltava batendo nos peitos.
49 Amma dukan mutanen da suka san Yesu, tare da mata da suka bi shi daga Galili, suka tsaya daga nesa suna kallon abubuwan nan.
E todos os seus conhecidos, e as mulheres que juntamente o haviam seguido desde a Galilea, estavam de longe vendo estas coisas.
50 Akwai wani mutum mai suna Yusuf, ɗan Majalisa, wanda shi nagari ne, mai adalci,
E eis que um varão por nome José, senador, homem de bem e justo,
51 shi dā ma bai yarda da shawararsu, da kuma abin da suka yi ba. Shi daga Arimateya ne wani garin Yahudiya. Yana kuma jiran zuwa mulkin Allah.
Que não tinha consentido no seu conselho, nem em seus feitos, de Arimathea, cidade dos judeus, e que também esperava o reino de Deus:
52 Sai ya je wurin Bilatus ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
Este, chegando a Pilatos, pediu o corpo de Jesus;
53 Sai ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi a cikin zanen lilin, ya sa shi a wani kabari da aka fafe a cikin dutse, wadda ba a taɓa sa kowa ba.
E, havendo-o tirado, envolveu-o num lençol, e pô-lo num sepulcro lavrado numa penha, onde ninguém ainda havia sido posto.
54 An yi haka ne a Ranar Shirye-shirye, ranar Asabbaci kuma yana dab da farawa.
E era o dia da preparação, e amanhecia o sábado.
55 Matan da suka zo tare da Yesu, daga Galili suka bi Yusuf suka ga kabarin, da kuma yadda aka ajiye jikin.
E também as mulheres, que tinham saído com ele da Galilea, o seguiram, e viram o sepulcro, e como foi posto o seu corpo.
56 Sa’an nan, suka koma gida, suka shirya kayan ƙanshi da turare. Amma suka huta a ranar Asabbaci don kiyaye doka.
E, voltando elas, prepararam especiarias e unguentos; e no sábado repousaram, conforme o mandamento.

< Luka 23 >