< Luka 23 >

1 Sai dukan majalisa suka tashi, suka kai shi gaban Bilatus.
Ils se levèrent en masse, et conduisirent Jésus devant Pilate.
2 Suka fara zarginsa suna cewa, “Mun sami wannan mutum yana rikitar da al’ummarmu. Yana hana a biya haraji ga Kaisar. Yana kuma cewa, shi Kiristi ne, sarki kuma.”
Ils se mirent à l'accuser, disant: «Nous avons trouvé cet homme qui poussait notre nation à la révolte, et qui défendait de payer le tribut à César, se prétendant lui-même Messie, Roi.»
3 Sai Bilatus ya tambayi Yesu ya ce, “Kai ne sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
Pilate l'interrogea, disant: «Tu es le roi des Juifs?» — «Tu le dis, » lui répondit Jésus.
4 Sai Bilatus ya sanar wa manyan firistoci da taron ya ce, “Ni fa, ban sami wani ainihin abin zargi game wannan mutum nan ba.”
Pilate dit aux principaux sacrificateurs et à la foule: «Je ne trouve rien de criminel en cet homme.»
5 Amma suka nace, suna cewa, “Yana tā da hankulan mutane, ko’ina a Yahudiya da koyarwarsa. Ya fara daga Galili, ga shi har ya kai nan.”
Mais ils insistèrent, disant: «Il agite le peuple, en enseignant par toute la Judée, après avoir commencé par la Galilée, et être venu jusqu'ici.»
6 Da Bilatus ya ji haka, sai ya yi tambaya, “Ko shi mutumin Galili ne?”
Pilate, entendant nommer la Galilée, demanda si cet homme était Galiléen;
7 Da ya ji cewa, Yesu yana ƙarƙashin mulkin Hiridus ne, sai ya aika da shi zuwa wurin Hiridus, don a lokacin Hiridus yana Urushalima.
et ayant appris qu'il était de la juridiction d'Hérode, il le renvoya à Hérode, qui était aussi à Jérusalem en ces jours-là.
8 Da Hiridus ya ga Yesu, sai ya yi murna ƙwarai, don tun dā ma yana marmari ya gan shi a kan abin da ya ji game da shi. Ya yi fata ya ga Yesu, yă kuma yi waɗansu ayyukan banmamaki.
Hérode eut une grande joie de voir Jésus, car depuis longtemps il en avait le désir, parce qu'il avait entendu parler de lui, et qu'il espérait le voir faire quelque miracle.
9 Ya yi masa tambayoyi masu yawa, amma Yesu bai ba shi ko amsa ba.
Il lui adressa un grand nombre de questions, mais Jésus ne lui répondit rien.
10 Manyan firistoci da malaman dokoki suna tsaye a wurin, suna kawo zargi masu ƙarfi a kansa.
Or les principaux sacrificateurs et les scribes étaient là, qui l'accusaient avec véhémence;
11 Sai Hiridus da sojojinsa suka wulaƙanta shi, suka yi masa ba’a. Sa’an nan, suka sa masa babban riga, suka mai da shi wurin Bilatus.
mais Hérode avec sa garde le traita avec mépris: il le fit revêtir par dérision d'un magnifique manteau, et le renvoya à Pilate.
12 A ranar, Hiridus da Bilatus suka zama abokan juna, don tun dā ma, su abokan gāba ne.
Le jour même, Pilate et Hérode devinrent amis, d'ennemis qu'ils étaient auparavant.
13 Bilatus ya tara manyan firistoci, da masu mulki, da mutane,
Pilate, ayant assemblé les principaux sacrificateurs, les sénateurs et le peuple, leur dit:
14 ya ce musu, “Kun kawo mini wannan mutum, a matsayin wanda yana zuga mutane su yi tawaye. Na bincike shi a gabanku, ban ga a kan me kuka kawo kararsa ba.
«Vous avez traduit devant moi cet homme, comme excitant le peuple à la révolte, et, après l'avoir interrogé en votre présence, je ne l'ai trouvé coupable d'aucun des crimes dont vous l'accusez.
15 Haka ma Hiridus, shi ya sa ya dawo da shi nan wurinmu. Kamar yadda ku ma kun gani, ba abin da mutumin nan ya yi, da ya isa mutuwa.
Hérode non plus, car je vous ai renvoyés à lui, et, vous le voyez, cet homme n'a rien fait qui mérite la mort.
16 Saboda haka, zan yi masa bulala, in sāke shi.”
Je le relâcherai donc, après l'avoir fait châtier.»
[Or il était obligé à chaque fête de leur relâcher un prisonnier]
18 Suka yi ihu gaba ɗaya suka ce, “A yi gaba da wannan mutum! A sake mana Barabbas!”
Mais ils crièrent tous à la fois: «Fais-le mourir! Relâche-nous Barabbas.»
19 (Barabbas yana kurkuku saboda laifin tā da hankali a birnin, da kuma don kisankai.)
Ce Barabbas avait été mis en prison pour une sédition qui avait eu lieu dans la ville, et pour un meurtre.
20 Sai Bilatus ya sāke yin musu magana don yana so ya saki Yesu.
Pilate, qui désirait relâcher Jésus, les harangua donc de nouveau;
21 Amma sai suka ci gaba da ihu, suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!”
mais ils répondirent par les cris de «crucifie-le! crucifie-le!»
22 Ya sāke ce musu, sau na uku, “Don me? Wane laifi wannan mutum ya yi? Ni dai ban same shi da wani dalilin da ya isa a kashe shi ba. Saboda haka, zan sa a hore shi, sa’an nan in sāke shi.”
Il leur dit pour la troisième fois: «Quel mal a-t-il donc fait? Je n'ai rien trouvé en lui qui mérite la mort; je le relâcherai donc, après l'avoir fait châtier?»
23 Amma suna ihu, suna nacewa, suna cewa, dole a gicciye shi, har ihunsu ya rinjaye shi.
Mais ils insistèrent, demandant à grands cris qu'il fût crucifié, et leurs clameurs et celles des principaux sacrificateurs prévalurent,
24 Sai Bilatus ya biya bukatarsu da ya ji roƙonsu.
et Pilate prononça que ce qu'ils demandaient serait exécuté:
25 Ya saki mutumin da aka jefa a kurkuku saboda tā da hankali, da kisankai, shi wanda suka roƙa. Sa’an nan ya ba da Yesu ga nufinsu.
il leur relâcha celui qui avait été mis en prison pour sédition et pour meurtre, et qu'ils réclamaient; et il leur abandonna Jésus.
26 Sa’ad da suna tafiya da Yesu, sai wani da ake kira Siman, mutumin Sairin, yana zuwa daga ƙauye. Suka kama shi, suka aza masa gicciyen, suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen, ya bi Yesu a baya.
Comme ils l'emmenaient au supplice, ils prirent un nommé Simon, de Cyrène, qui venait des champs, et ils le chargèrent de la croix, pour qu'il la portât derrière Jésus.
27 Mutane da yawa sosai suka bi shi, a cikinsu ma da mata waɗanda suka yi makoki da kuka dominsa.
Or, Jésus était suivi d'une grande foule de peuple, et particulièrement de femmes qui se frappaient la poitrine et pleuraient sur lui.
28 Yesu ya juya, ya ce musu, “’Yan matan Urushalima, kada ku yi kuka saboda ni, amma ku yi kuka saboda kanku, da kuma saboda’ya’yanku.
Il se tourna vers elles, et leur dit: «Filles de Jérusalem, ne pleurez pas sur moi, mais pleurez sur vous-mêmes et sur vos enfants;
29 Gama lokaci yana zuwa da za ku ce, ‘Masu albarka ne bakararru, wato, mata marasa haihuwa, da mahaihuwar da ba su taɓa haihuwa ba, da kuma mama da ba su taɓa shayar da nono ba!’
car les temps viennent où l’on dira: «Heureuses les stériles! Heureux le sein qui n'a point enfanté! Heureuses les mamelles qui n'ont point nourri!»
30 Sa’an nan “‘za su ce wa duwatsu, “Ku fāɗi a kanmu!” Za su ce wa tuddai kuma, “Ku rufe mu!”’
Alors on se mettra à dire aux montagnes: «Tombez sur nous; » et aux collines: «Couvrez-nous; »
31 Gama in mutane suna yin waɗannan abubuwa a lokacin da itace na ɗanye, me zai faru in ya bushe?”
car si l'on fait ces choses au bois vert, que fera-t-on au bois sec?»
32 Tare da shi akwai mutum biyu masu laifi, da aka tafi da su don a gicciye.
Les soldats conduisaient en même temps deux malfaiteurs pour être mis à mort avec lui.
33 Da suka isa wurin da ake kira “Ƙoƙon Kai,” nan suka gicciye shi, tare da masu laifin nan, ɗaya a hannun damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
Quand ils furent arrivés au lieu appelé Calvaire, ils y crucifièrent Jésus, ainsi que les malfaiteurs, l'un à sa droite, l'autre à sa gauche;
34 Yesu ya ce, “Ya Uba ka yi musu gafara, don ba su san abin da suke yi ba.” Suka rarraba tufafinsa ta wurin jefa ƙuri’a.
et Jésus dit: «Père, pardonne-leur, car ils ne savent ce qu'ils font.» Ils se partagèrent ses vêtements en les tirant au sort.
35 Mutanen suka tsaya suna kallo. Har masu mulki ma suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, to, ya ceci kansa in shi ne Kiristi na Allah, Zaɓaɓɓe.”
Le peuple était là qui regardait. Les sénateurs se moquaient et disaient: «Il en a sauvé d'autres, qu'il se sauve lui-même, s'il est le Messie, l'élu de Dieu.»
36 Sojoji su ma, suka zo suka yi masa ba’a. Suka miƙa masa ruwan tsami.
Les soldats aussi, s'approchant pour lui présenter du vinaigre, le raillaient,
37 Suka ce, “In kai ne sarkin Yahudawa, ka ceci kanka mana.”
et disaient: «Si tu es le roi des Juifs, sauve-toi toi-même.»
38 Bisa da shi kuma akwai rubutun da ya ce, Wannan shi ne Sarkin Yahudawa.
Il y avait même une inscription au-dessus de sa tête, portant: «Celui-ci est le Roi des Juifs.»
39 Ɗaya daga cikin masu laifin da aka gicciye a wurin ya zazzage shi ya ce, “Shin, ba kai ne Kiristi ba? To, ka ceci kanka, ka kuma cece mu mana!”
L'un des malfaiteurs pendus à la croix, l'injuriait, disant: «N'es-tu pas le Messie? Sauve-toi toi-même, et nous avec toi.»
40 Amma ɗayan mai laifi ya kwaɓe shi ya ce, “Ba ka da tsoron Allah ne, wai saboda kana ƙarƙashin hukunci ɗaya tare da shi?
Mais l'autre le reprenait: «N'as-tu point de crainte de Dieu, toi qui subis le même jugement?
41 Horonmu, daidai aka yi mana, sakamakon abin da muka yi ne. Amma wannan mutum, bai yi wani laifi ba.”
Pour nous, c'est justice; car nous recevons la peine que nos crimes ont méritée; mais lui, il n'a rien fait de mal.»
42 Sai ya ce, “Yesu, ka tuna da ni sa’ad da ka shiga mulkinka.”
Et il dit à Jésus: «Souviens-toi de moi, quand tu seras dans ton règne.»
43 Yesu ya amsa, ya ce masa, “Gaskiya nake faɗa maka, yau ɗin nan, za ka kasance tare da ni, a mulkina a sama.”
Et Jésus répondit: «Je te dis en vérité, qu'aujourd'hui même tu seras avec moi dans le paradis.»
44 Yanzu kuwa wajen sa’a ta shida ne, kuma duhu ya rufe ko’ina a ƙasar, har zuwa sa’a ta tara,
Il était déjà environ la sixième heure, quand des ténèbres se répandirent sur tout le pays jusqu’à la neuvième heure.
45 domin rana ta daina haskakawa. Labulen da yake cikin haikali kuma ya yage kashi biyu.
Le soleil pâlit; le voile du temple se déchira par le milieu;
46 Yesu ya yi kira da babbar murya ya ce, “Ya Uba, na danƙa ruhuna a hannunka.” Da ya faɗi haka, sai ya ja numfashi na ƙarshe.
et Jésus s'écria d'une voix forte: «Père, je remets mon esprit entre tes mains.» En prononçant ces mots, il expira.
47 Da jarumin ya ga abin da ya faru, sai ya yabi Allah ya ce, “Gaskiya, wannan mutum mai adalci ne.”
Le centurion, témoin de ces événements, donna gloire à Dieu, disant: «Assurément cet homme était juste; »
48 Da dukan mutanen da suka taru, domin shaidar waɗannan abubuwa, suka ga abin da ya faru, sai suka buga ƙirjinsu suka tafi.
et les foules que ce spectacle avait attirées, voyant ce qui s'était passé, s'en retournaient toutes en se frappant la poitrine.
49 Amma dukan mutanen da suka san Yesu, tare da mata da suka bi shi daga Galili, suka tsaya daga nesa suna kallon abubuwan nan.
Mais tous ceux qui connaissaient Jésus, et les femmes qui l'avaient suivi de Galilée, se tenaient là, à l'écart, regardant ce qui se passait.
50 Akwai wani mutum mai suna Yusuf, ɗan Majalisa, wanda shi nagari ne, mai adalci,
Il y avait un sénateur, nommé Joseph, homme droit et juste,
51 shi dā ma bai yarda da shawararsu, da kuma abin da suka yi ba. Shi daga Arimateya ne wani garin Yahudiya. Yana kuma jiran zuwa mulkin Allah.
qui ne s'était associé ni au dessein, ni aux actes des autres sénateurs; il était originaire d'Arimathée. ville des Juifs, et il attendait le royaume de Dieu.
52 Sai ya je wurin Bilatus ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
Il se rendit auprès de Pilate et lui demanda le corps de Jésus.
53 Sai ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi a cikin zanen lilin, ya sa shi a wani kabari da aka fafe a cikin dutse, wadda ba a taɓa sa kowa ba.
Il le descendit de la croix, l'enveloppa d'un linceul, et le déposa dans un sépulcre taillé dans le roc, où personne n'avait encore été mis.
54 An yi haka ne a Ranar Shirye-shirye, ranar Asabbaci kuma yana dab da farawa.
C'était le jour de la préparation, et le sabbat allait commencer.
55 Matan da suka zo tare da Yesu, daga Galili suka bi Yusuf suka ga kabarin, da kuma yadda aka ajiye jikin.
Les femmes qui étaient venues de la Galilée avec Jésus, ayant accompagné Joseph, virent le sépulcre et la manière dont le corps de Jésus y fut placé,
56 Sa’an nan, suka koma gida, suka shirya kayan ƙanshi da turare. Amma suka huta a ranar Asabbaci don kiyaye doka.
puis, s'en étant retournées, elles préparèrent des aromates et des parfums.

< Luka 23 >