< Luka 21 >

1 Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
وقتی عیسی در معبد ایستاده بود و به اطراف نگاه می‌کرد، ثروتمندانی را دید که هدایای خود را در صندوق بِیت‌المال می‌ریختند.
2 Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
در همان حال بیوه‌زن فقیری نیز آمد و دو سکۀ ناچیز در صندوق انداخت.
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
عیسی فرمود: «در واقع این بیوه‌زن فقیر بیشتر از تمام آن ثروتمندان هدیه داده است.
4 Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
چون آنها قسمت کوچکی از آنچه را که احتیاج نداشتند دادند، ولی این زن فقیر هر چه داشت داد.»
5 Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
در این هنگام بعضی از شاگردان عیسی از سنگهای زیبایی که در بنای خانۀ خدا به کار رفته بود و از هدایای گرانبهایی که مردم وقف کرده بودند، تعریف می‌کردند. اما عیسی به ایشان فرمود:
6 “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
«روزی فرا می‌رسد که تمام این چیزهایی که می‌بینید، سنگی بر سنگی دیگر باقی نخواهد ماند، بلکه همه زیر و رو خواهد شد.»
7 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
ایشان با تعجب گفتند: «استاد، این وقایع در چه زمانی روی خواهد داد؟ نشانۀ نزدیک شدن آنها چیست؟»
8 Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
عیسی در جواب فرمود: «مواظب باشید کسی شما را گمراه نکند. زیرا بسیاری به نام من آمده، خواهند گفت،”من مسیح هستم“و”زمان موعود فرا رسیده است“. اما باور نکنید.
9 Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
و هنگامی که خبر جنگها و آشوبها را بشنوید، پریشان نشوید زیرا باید اول چنین وقایعی اتفاق بیفتد، اما به این زودی دنیا به آخر نخواهد رسید.»
10 Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
سپس ادامه داد: «قومها و ممالک به هم اعلان جنگ خواهند داد.
11 Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
در جاهای مختلف دنیا، زمین لرزه‌های عظیم، قحطی‌ها و بیماریهای مسری پدید خواهد آمد و در آسمان نیز چیزهای عجیب و هولناک دیده خواهد شد.
12 “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
«اما قبل از این وقایع، دوره آزار و جفا و شکنجه پیش خواهد آمد. شما را به خاطر نام من، به کنیسه‌ها و زندانها خواهند سپرد، و به حضور پادشاهان و والیان خواهند کشاند.
13 Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
اما این فرصتی خواهد بود تا دربارۀ من شهادت دهید.
14 Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
پس پیشاپیش نگران نباشید که چگونه از خود دفاع کنید،
15 Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
زیرا به شما خواهم آموخت که چه بگویید، به طوری که هیچ‌یک از دشمنانتان، یارای پاسخگویی و ایستادگی در مقابل شما را نخواهند داشت!
16 Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
پدر و مادر و برادران و بستگان و دوستانتان به شما خیانت خواهند کرد و شما را تسلیم دشمن خواهند کرد؛ و برخی از شما کشته خواهید شد؛
17 Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
تمام مردم دنیا به خاطر نام من از شما متنفر خواهند شد.
18 Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
اما مویی از سر شما گُم نخواهد شد!
19 Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
اگر تا به آخر تحمل کنید، جانهای خود را نجات خواهید داد.
20 “In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
«اما هرگاه دیدید که اورشلیم به محاصره دشمن درآمده، بدانید که زمان نابودی آن فرا رسیده است.
21 A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
آنگاه کسانی که در یهودیه هستند، به تپه‌های اطراف فرار کنند و آنانی که در اورشلیم هستند از شهر بیرون بروند و کسانی که در بیرون شهر هستند، به شهر باز نگردند.
22 Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
زیرا آن زمان، هنگام مجازات خواهد بود، روزهایی که تمام هشدارهای انبیا تحقق خواهند یافت.
23 Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
وای به حال زنانی که در آن زمان آبستن باشند یا کودک شیرخوار داشته باشند. زیرا این قوم دچار مصیبت سختی شده، خشم و غضب خدا بر آنان عارض خواهد شد؛
24 Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
ایشان به دم شمشیر خواهند افتاد و یا اسیر شده، به سرزمینهای بیگانه تبعید خواهند گشت. اورشلیم نیز به دست بیگانگان افتاده، پایمال خواهد شد تا زمانی که دوره تسلط بیگانگان به پایان رسد.
25 “Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
«آنگاه در آسمان اتفاقات عجیبی خواهد افتاد و در خورشید و ماه و ستارگان، علائم هولناکی دیده خواهد شد. بر روی زمین، قومها از غرش دریاها و خروش امواج آن، آشفته و پریشان خواهند شد.
26 Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
بسیاری از تصور سرنوشت هولناکی که در انتظار دنیاست، ضعف خواهند کرد؛ زیرا نیروهایی که زمین را نگاه داشته‌اند، به لرزه در خواهند آمد.
27 A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
آنگاه تمام مردم روی زمین پسر انسان را خواهند دید که در ابری، با قدرت و شکوه عظیم می‌آید.
28 Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
پس وقتی این رویدادها آغاز می‌شوند، بایستید و به بالا نگاه کنید، زیرا نجات شما نزدیک است!»
29 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
سپس این مثل را برایشان زد: «درخت انجیر یا سایر درختان را بنگرید.
30 A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
وقتی شکوفه می‌کنند، بی‌آنکه کسی به شما بگوید، می‌فهمید تابستان نزدیک است.
31 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
همین‌طور نیز وقتی تمام این نشانه‌ها را ببینید، بدانید که به‌زودی ملکوت خدا آغاز خواهد شد.
32 “Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
«براستی به شما می‌گویم که تا این چیزها اتفاق نیفتد، این نسل از میان نخواهد رفت.
33 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
آسمان و زمین از بین خواهند رفت، اما کلام من هرگز زایل نخواهد شد.
34 “Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
«پس مراقب باشید! نگذارید پرخوری، میگساری و غم و غصه‌های زندگی، دلتان را سنگین سازد و آن روز مانند دامی شما را غافلگیر کند.
35 Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
زیرا آن روز بر همۀ مردم جهان خواهد آمد.
36 Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
پس هر لحظه مراقب باشید و همیشه دعا کنید تا از این رویدادهای وحشتناک در امان بوده، در حضور پسر انسان بایستید.»
37 Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
به این ترتیب، او هر روز در معبد به تعلیم مردم می‌پرداخت و هنگام عصر نیز از شهر خارج شده، شب را در کوه زیتون به صبح می‌رساند.
38 Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.
مردم نیز از صبح زود برای شنیدن سخنانش در معبد جمع می‌شدند.

< Luka 21 >