< Luka 21 >

1 Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
Tout en regardant, il vit des riches qui mettaient leurs offrandes, dans le tronc.
2 Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
Il vit aussi une veuve indigente qui y mit deux leptes,
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
et il dit: «En vérité, je vous le déclare, cette veuve pauvre a donné plus que tous.
4 Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
Car tous ceux-là, pour leurs offrandes, ont puisé dans leur superflu; mais celle-ci a pris sur son indigence, elle a donné tout ce qu'elle possédait, tout ce qu'elle avait pour vivre.»
5 Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
Quelques-uns faisaient remarquer, à propos du Temple, les pierres magnifiques et les offrandes dont il était orné.
6 “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
«Des jours viendront, dit-il, où de ce que vous voyez, il ne restera pas ici pierre sur pierre; tout sera renversé.»
7 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
Alors ils le questionnèrent: «Maître, lui dirent-ils, quand donc ces choses arriveront-elles? et quel sera le signe qu'elles vont avoir lieu?»
8 Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
Il répondit: «Prenez garde de vous laisser séduire; car plusieurs viendront en prenant mon nom, disant: «C'est moi!» et: «Le moment approche!». Ne marchez pas à leur suite.
9 Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
Quand vous entendrez parler de guerres et de révolutions, n'en soyez pas effrayés. Il faut, en effet, que cela arrive d'abord; mais ce ne sera pas tout de suite la fin.»
10 Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
Il continua ainsi: «Se soulèvera nation contre nation, royaume contre royaume;
11 Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
il y aura de vastes tremblements de terre; ici et là des famines, des pestes, d'effrayantes choses et de grands prodiges au ciel.»
12 “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
«Mais, avant tout, on mettra la main sur vous, et l'on vous persécutera. Vous serez livrés aux synagogues, jetés en prison; et, à cause de mon nom, traînés devant des rois et des procurateurs.
13 Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
Cela vous arrivera pour que vous rendiez témoignage.
14 Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
Gravez bien dans vos coeurs que vous n'aurez pas à vous préoccuper de votre défense,
15 Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
car je vous donnerai, moi, un langage et une sagesse auxquels tous vos adversaires ne pourront ni résister ni répliquer.
16 Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
Vous serez livrés par vos pères et vos mères, par vos frères, par vos parents, par vos amis; ils feront mourir nombre d'entre vous;
17 Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
et vous serez en haine à tout le monde à cause de mon nom.
18 Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
Et cependant pas un cheveu de votre tête ne doit périr;
19 Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
c'est par votre patience que vous sauverez vos vies.»
20 “In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
Lorsque vous verrez des armées camper autour de Jérusalem et l'investir, sachez alors qu'approche sa désolation.
21 A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
Que ceux qui seront dans la Judée fuient dans les montagnes, que ceux qui seront au milieu du pays en sortent, que ceux qui seront dans les contrées voisines n'y rentrent pas.
22 Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
Ces jours-là, en effet, seront des jours vengeurs où s'accomplira tout ce qui est écrit.
23 Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
Malheur aux femmes qui seront enceintes et à celles qui allaiteront en ces jours-là! car il y aura sur la terre une calamité immense et une colère contre ce peuple;
24 Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
les hommes tomberont sous le tranchant du glaive, ils seront emmenés captifs dans toutes les nations, Jérusalem sera foulée aux pieds par les païens, jusqu'à ce que les temps des païens soient aussi accomplis.»
25 “Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
«Il y aura des prodiges dans le soleil, dans la lune et dans les étoiles; il y en aura sur la terre: angoisse des peuples jetés dans l'incertitude par le mugissement de la mer et des flots;
26 Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
des hommes expirant de terreur dans l'attente de ce qui va arriver au monde, car les puissances des cieux seront ébranlées.
27 A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
Et c'est alors qu'on verra le Fils de l'homme arrivant, au sein d'une nuée, en puissance et grande gloire.
28 Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
Quand ces choses commenceront à arriver, regardez en haut, levez la tête, parce qu'approchera votre délivrance.»
29 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
Il se servit d'une comparaison: «Voyez le figuier, et tous les arbres.
30 A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
Dès qu'ils commencent à pousser, vous savez de vous-mêmes, en les voyant, que l'été est proche.
31 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
De même quand vous verrez arriver ces choses sachez que le royaume de Dieu est proche.
32 “Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
En vérité, je vous le dis, cette génération ne passera pas que tout cela n'arrive.
33 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
Le ciel et la terre passeront, mais mes paroles ne passeront point.»
34 “Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
«Veillez sur vous-mêmes, de peur que vos coeurs ne s'appesantissent dans la bonne chère, dans les excès de boisson, dans les soucis de ce monde, et que ce jour-là ne vous surprenne inopinément.
35 Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
Car il surviendra comme un filet sur tous ceux qui habitent la surface de la terre.
36 Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
Soyez donc vigilants en tout temps, et priez afin que vous soyez rendus dignes d'échapper à toutes ces choses qui vont arriver et de subsister en présence du Fils de l'homme.»
37 Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
Le jour, il restait au Temple et y enseignait. Mais il allait passer les nuits hors de la ville sur la montagne appelée «Bois d'Oliviers»,
38 Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.
et tout le peuple, de grand matin, venait au Temple pour l'entendre.

< Luka 21 >