< Luka 21 >

1 Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
And having looked up, he saw those who did cast their gifts to the treasury — rich men,
2 Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
and he saw also a certain poor widow casting there two mites,
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
and he said, 'Truly I say to you, that this poor widow did cast in more than all;
4 Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
for all these out of their superabundance did cast into the gifts to God, but this one out of her want, all the living that she had, did cast in.'
5 Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
And certain saying about the temple, that with goodly stones and devoted things it hath been adorned, he said,
6 “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
'These things that ye behold — days will come, in which there shall not be left a stone upon a stone, that shall not be thrown down.'
7 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
And they questioned him, saying, 'Teacher, when, then, shall these things be? and what [is] the sign when these things may be about to happen?'
8 Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
And he said, 'See — ye may not be led astray, for many shall come in my name, saying — I am [he], and the time hath come nigh; go not on then after them;
9 Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
and when ye may hear of wars and uprisings, be not terrified, for it behoveth these things to happen first, but the end [is] not immediately.'
10 Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
Then said he to them, 'Nation shall rise against nation, and kingdom against kingdom,
11 Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
great shakings also in every place, and famines, and pestilences, there shall be; fearful things also, and great signs from heaven there shall be;
12 “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
and before all these, they shall lay on you their hands, and persecute, delivering up to synagogues and prisons, being brought before kings and governors for my name's sake;
13 Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
and it shall become to you for a testimony.
14 Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
'Settle, then, to your hearts, not to meditate beforehand to reply,
15 Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
for I will give to you a mouth and wisdom that all your opposers shall not be able to refute or resist.
16 Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
'And ye shall be delivered up also by parents, and brothers, and kindred, and friends, and they shall put of you to death;
17 Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
and ye shall be hated by all because of my name —
18 Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
and a hair out of your head shall not perish;
19 Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
in your patience possess ye your souls.
20 “In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
'And when ye may see Jerusalem surrounded by encampments, then know that come nigh did her desolation;
21 A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
then those in Judea, let them flee to the mountains; and those in her midst, let them depart out; and those in the countries, let them not come in to her;
22 Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
because these are days of vengeance, to fulfil all things that have been written.
23 Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
'And woe to those with child, and to those giving suck, in those days; for there shall be great distress on the land, and wrath on this people;
24 Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
and they shall fall by the mouth of the sword, and shall be led captive to all the nations, and Jerusalem shall be trodden down by nations, till the times of nations be fulfilled.
25 “Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
'And there shall be signs in sun, and moon, and stars, and on the land [is] distress of nations with perplexity, sea and billow roaring;
26 Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
men fainting at heart from fear, and expectation of the things coming on the world, for the powers of the heavens shall be shaken.
27 A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
'And then they shall see the Son of Man, coming in a cloud, with power and much glory;
28 Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
and these things beginning to happen bend yourselves back, and lift up your heads, because your redemption doth draw nigh.'
29 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
And he spake a simile to them: 'See the fig-tree, and all the trees,
30 A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
when they may now cast forth, having seen, of yourselves ye know that now is the summer nigh;
31 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
so also ye, when ye may see these things happening, ye know that near is the reign of God;
32 “Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
verily I say to you — This generation may not pass away till all may have come to pass;
33 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
the heaven and the earth shall pass away, but my words may not pass away.
34 “Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
'And take heed to yourselves, lest your hearts may be weighed down with surfeiting, and drunkenness, and anxieties of life, and suddenly that day may come on you,
35 Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
for as a snare it shall come on all those dwelling on the face of all the land,
36 Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
watch ye, then, in every season, praying that ye may be accounted worthy to escape all these things that are about to come to pass, and to stand before the Son of Man.'
37 Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
And he was during the days in the temple teaching, and during the nights, going forth, he was lodging at the mount called of Olives;
38 Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.
and all the people were coming early unto him in the temple to hear him.

< Luka 21 >