< Luka 21 >

1 Da Yesu ya ɗaga ido, sai ya ga waɗansu masu arziki suna sa baikonsu a ma’ajin haikalin.
And, looking up, he saw the, rich, who were casting their gifts into the treasury, —
2 Ya kuma ga wata gwauruwa matalauciya, ta saka anini biyu.
and he saw a certain poor widow, casting in thither two mites;
3 Sai ya ce, “Gaskiya ina faɗa muku, wacce nan gwauruwa matalauciya ta sa fiye da dukan sauran.
and he said—Of a truth, I say unto you—This destitute widow, more than they all, hath cast in;
4 Dukan mutanen nan sun ba da baikonsu daga cikin arzikinsu ne, amma ita daga cikin talaucinta, ta saka duk abin da take da shi na rayuwa.”
For, all these, out of their superfluity, have cast in among the gifts, but, she, out of her deficiency, all the living that she had, hath cast in.
5 Waɗansu daga cikin almajiransa, suka fara magana a kan yadda aka yi wa haikalin ado da duwatsu masu kyau, da kuma kyautai da aka keɓe wa Allah. Amma Yesu ya ce,
And, certain saying, of the temple—With beautiful stones and offerings, hath it been adorned! he said—
6 “Wannan abin da kuke kallo a nan, lokaci yana zuwa da ba za a bar wani dutse a kan wani dutse ba. Kowannensu, za a rushe shi.”
As to these things, which ye are looking upon, There will come days, in which there will not be left here, stone upon stone, which will not be taken down.
7 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, yaushe waɗannan za su faru? Kuma wace alama za tă nuna cewa suna dab da faruwa?”
And they questioned him, saying—Teacher! when, therefore, will these things be? And, what the sign, when these things shall be about to come to pass?
8 Ya amsa ya ce, “Ku lura, kada ku kuma a ruɗe ku. Gama da yawa za su zo a cikin sunana, suna cewa, ‘Ai, ni ne shi,’ da kuma, ‘Lokaci ya yi kusa.’ Kada ku bi su.
And, he, said—Be taking heed ye be not deceived; for, many, will come upon my name, saying—I, am he, —and—The season, hath drawn near! Do not go after them.
9 Sa’ad da kuka ji labarin yaƙe-yaƙe, da juye juyen mulki, kada ku tsorota. Dole ne waɗannan abubuwa su fara faruwa, amma ƙarshen ba zai zo nan da nan ba.”
But, whensoever ye shall hear of wars and revolutions, be not terrified, —for these things, must needs, come to pass first, but, not immediately, is the end.
10 Sai ya ce musu, “Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki zai tasar wa mulki.
Then, said he unto them—There will rise up, nation against nation, and kingdom against kingdom;
11 Za a yi manyan girgizar ƙasa, da yunwa, da annoba a wurare dabam-dabam, da kuma abubuwa masu bantsoro, da manyan alamu daga sama.
As well great earthquakes, as also, in places, pestilences and famines, will there be, as well objects of terror, as also, from heaven, great signs, will there be.
12 “Amma kafin duk abubuwa nan, za a kama ku a tsananta muku. Za a kai ku majami’u, da kurkuku. Za a kuma kai ku gaban sarakuna da gwamnoni, kuma dukan waɗannan saboda sunana.
And before, all these things, they will thrust upon you their hands, and persecute you, delivering you up into the synagogues and prisons, —when ye have been led away before kings and governors, for the sake of my name;
13 Wannan zai sa ku zama shaidu a gare su.
But it shall turn out to you for a witness.
14 Amma ku yi ƙuduri, wato, ku shirya zuciyarku, a kan ba za ku damu ba kafin lokacin, game da yadda za ku kāre kanku.
Settle, then, in your hearts, not to be studying beforehand, how to make defense;
15 Gama zan ba ku kalmomi, da hikima waɗanda ba ko ɗaya daga cikin maƙiyanku, za su iya tsayayya da ku, ko su ƙaryata.
For, I, will give you a mouth and wisdom, which one-and-all who are setting themselves against, you shall be unable to withstand or gainsay.
16 Har iyayenku, da’yan’uwanku maza, da danginku, da abokanku ma, duk za su bashe ku, su kuma kashe waɗansunku.
But ye will be delivered up, even by parents, and brethren, and kinsfolk, and friends, and they will put to death some from among you;
17 Duk mutane za su ƙi ku saboda ni.
And ye will be hated by all, because of my name:
18 Amma ko gashi ɗaya na kanku, ba zai hallaka ba.
And, a hair of your head, in nowise shall perish, —
19 Ta wurin tsayawa da ƙarfi, za ku sami rai.
By your endurance, shall ye gain your lives for a possession.
20 “In kuka ga mayaƙa sun kewaye Urushalima, za ku sani rushewarta ya yi kusa.
But whensoever ye shall see Jerusalem, encompassed by armies, then, know, that her desolation hath drawn near.
21 A lokacin nan, bari waɗanda suke Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. Bari waɗanda suke cikin birnin kuma su fita, bari kuma waɗanda suke ƙauye kada su shiga birnin.
Then they who are in Judaea, let them flee into the mountains, and they who are in her midst, let them go forth, —and they who are in the fields, let them not enter into her;
22 Gama wannan shi ne lokacin hukunci, saboda a cika duk abin da aka rubuta.
For, days of avenging, are, these, for all the things written to be fulfilled.
23 Zai zama abin kaito ga mata masu ciki, da mata masu renon’ya’ya, a waɗancan kwanakin! Za a yi baƙin ciki mai tsanani a ƙasar, da kuma fushi mai tsanani a kan mutanen nan.
Alas! for the women with child, and for them who are giving suck, in those days; for there will be great distress upon the land, and anger against this people.
24 Za a kashe su da takobi, a kuma ɗauke su’yan kurkuku, zuwa dukan al’ummai. Al’ummai za su tattaka Urushalima, har sai lokacin Al’ummai ya cika.
And they will fall by the edge of the sword, and be carried away captive into all the nations, and, Jerusalem, shall be trodden down by the nations, until the seasons of the nations shall be fulfilled [and shall be].
25 “Za a yi alamu a cikin rana, da cikin wata, da cikin taurari. A duniya, al’ummai za su yi baƙin ciki, su kuma rikice don tsoro, saboda ruri da kuma tafasar teku.
And there will he signs in sun, and moon, and stars, and, on the earth, anguish of nations in embarrassment—sea and surge resounding, —
26 Mutane za su suma don tsoro, za su kuma yi fargaba, a kan abin da yake zuwa a bisan duniya, gama za a girgiza duniyar taurarin sararin sama.
Men fainting, from fear and expectation of the things overtaking the inhabited earth. For, the powers of the heavens, will be shaken.
27 A lokacin ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin girgije, da iko, da ɗaukaka mai girma.
And, then, will they see the Son of Man—coming in a cloud, with great power and glory.
28 Sa’ad da waɗannan abubuwa sun fara faruwa, ku tashi tsaye, ku ɗaga kawunanku, domin fansarku yana matsowa kusa.”
And, when these things are beginning to come to pass, unbend and lift up your heads, because that, your redemption, is drawing near.
29 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa.
And he spake a parable unto them: See the fig-tree, and all the trees, —
30 A duk lokacin da sun fara fitar da ganye, za ku gani da kanku, ku san cewa, damina ta yi kusa.
Whensoever they have already budded, seeing it, of yourselves, ye observe that, already near, is, the summer:
31 Haka ma, in kuka ga waɗannan abubuwa suna faruwa, ku sani mulkin Allah ya yi kusa.
Thus, ye also, whensoever ye shall see, these, things coming to pass, observe ye, that, near, is the kingdom of God!
32 “Gaskiya nake gaya muku, ba shakka, wannan zamani ba zai shuɗe ba, sai dukan waɗannan abubuwa sun cika.
Verily, I say unto you—In nowise shall this generation pass away, until, all things, shall happen:
33 Sama da ƙasa za su shuɗe, amma kalmomina ba za su taɓa shuɗewa ba.
Heaven and earth, will pass away, but, my word, in nowise will pass away.
34 “Ku lura fa don kada son jin daɗi na banza, da shaye-shaye, da damuwa na rayuwa su rinjayi zuciyarku, har ranar ta auko muku ba tsammani kamar tarko.
But be taking heed unto yourselves, lest once your hearts be made heavy—with debauch and drunkenness and anxieties about livelihood, and that day come upon you suddenly,
35 Gama za tă zo a kan kowa da yake kan dukan duniya.
as a snare, —For it will come in by surprise, upon all them that are dwelling on the face of all the earth.
36 Ku yi tsaro kullum, ku yi addu’a don ku iya kuɓuta daga dukan waɗannan abubuwa da suke kusan faruwa, don ku iya tsayawa a gaban Ɗan Mutum.”
But be watching in every season, making supplication, that ye may gain full vigour, to escape all these things that are about to be coming to pass, and to stand before the Son of Man.
37 Kowace rana, Yesu yakan je haikalin ya yi koyarwa, da kowace yamma kuma, ya je ya kwana a kan tudun da ake kira Dutsen Zaitun.
And he was, by day, in the temple, teaching; but, by night, going forth, he was lodging in the mount which is called the Mount of Olives.
38 Da sassafe kuma, dukan mutanen suka zo haikalin, don su saurare shi.
And, all the people, were coming at day-break unto him, in the temple, to be hearkening unto him.

< Luka 21 >