< Luka 20 >

1 Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
E aconteceu num daqueles dias que, estando ele ensinando o povo no templo, e anunciando o evangelho, sobrevieram os principais dos sacerdotes e os escribas com os anciãos,
2 Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
E falaram-lhe, dizendo: Dize-nos, com que autoridade fazes estas coisas? Ou, quem é que te deu esta autoridade?
3 Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
E, respondendo ele, disse-lhes: também eu vos farei uma pergunta: dizei-me pois:
4 baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
O batismo de João era do céu ou dos homens?
5 Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
E eles arrazoavam entre si, dizendo: Se dissermos: Do céu, ele nos dirá: Então porque o não crestes?
6 Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
E se dissermos: Dos homens; todo o povo nos apedrejará, pois tem por certo que João era profeta.
7 Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
E responderam que não sabiam de onde era.
8 Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
E Jesus lhes disse: Nem tão pouco eu vos digo com que autoridade faço estas coisas.
9 Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya.
E começou a dizer ao povo esta parábola: Um certo homem plantou uma vinha, e arrendou-a a uns lavradores, e partiu para fora da terra por muito tempo;
10 A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin’ya’yan inabin. Amma’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi.
E a seu tempo mandou um servo aos lavradores, para que lhe dessem dos frutos da vinha; mas os lavradores, espancando-o, mandaram-no vazio.
11 Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi.
E tornou ainda a mandar outro servo; mas eles, espancando também a este, e afrontando-o, mandaram-no vazio.
12 Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.
E tornou ainda a mandar terceiro; mas eles, ferindo também a este, o expulsaram.
13 “Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’
E disse o senhor da vinha: Que farei? Mandarei o meu filho amado; talvez que, vendo-o, o respeitem.
14 “Amma da’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’
Mas, vendo-o os lavradores, arrazoaram entre si, dizendo: Este é o herdeiro; vinde, matemo-lo, para que a herdade seja nossa.
15 Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi. “To, me mai gonar inabin zai yi da su?
E, lançando-o fora da vinha, o mataram. Que lhes fará pois o senhor da vinha?
16 Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.” Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”
Irá, e destruirá estes lavradores, e dará a outros a vinha. E, ouvindo eles isto, disseram: Assim não seja!
17 Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’
Mas ele, olhando para eles, disse: Que é isto pois que está escrito? A pedra, que os edificadores reprovaram, essa foi feita cabeça da esquina.
18 Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”
Qualquer que cair sobre aquela pedra será quebrantado, e aquele sobre quem ela cair será feito em pedaços.
19 Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.
E os principais dos sacerdotes e os escribas procuravam lançar mão dele naquela mesma hora; mas temeram o povo; porque entenderam que contra eles dissera esta parábola.
20 Sai suka sa masa ido, suka aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko.
E, trazendo-o debaixo de olho, mandaram espias, que se fingissem justos, para o apanhar em alguma palavra, e entrega-lo à jurisdição e poder do presidente.
21 Sai’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya.
E perguntaram-lhe, dizendo: Mestre, nós sabemos que falas e ensinas bem e retamente, e que não atentas para a aparência da pessoa, mas ensinas com verdade o caminho de Deus:
22 Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
É-nos lícito dar tributo a Cesar ou não?
23 Ya gane makircinsu, sai ya ce musu,
E, entendendo ele a sua astúcia, disse-lhes: Porque me tentais?
24 “Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?” Suka amsa, “Na Kaisar.”
Mostrai-me uma moeda. De quem tem a imagem e a inscrição? E, respondendo eles, disseram: De Cesar.
25 Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
Disse-lhes então: dai pois a Cesar o que é de Cesar, e a Deus o que é de Deus.
26 Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.
E não puderam apanha-lo em palavra alguma diante do povo; e, maravilhados da sua resposta, calaram-se.
27 Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
E, chegando-se alguns dos saduceus, que dizem não haver ressurreição, perguntaram-lhe,
28 “Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.’
Dizendo: Mestre, Moisés escreveu-nos que, se o irmão de algum falecer, tendo mulher, e não deixar filhos, o irmão dele tome a mulher, e suscite posteridade a seu irmão.
29 To, an yi waɗansu’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba’ya’ya.
Houve pois sete irmãos, e o primeiro tomou mulher, e morreu sem filhos;
30 Na biyun,
E o segundo tomou-a, e também este morreu sem filhos;
31 da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu’ya’ya.
E o terceiro tomou-a, e igualmente também os sete: e morreram, e não deixaram filhos.
32 A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
E por último, depois de todos, morreu também a mulher.
33 Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
Portanto, na ressurreição, de qual deles será a mulher, pois que os sete a tiveram por mulher?
34 Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn g165)
E, respondendo Jesus, disse-lhes: Os filhos deste século casam-se, e dão-se em casamento; (aiōn g165)
35 amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn g165)
Mas os que forem havidos por dignos de alcançar aquele século, e a ressurreição dos mortos, nem hão de casar, nem ser dados em casamento; (aiōn g165)
36 Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su’ya’yan Allah ne, tun da su’ya’yan tashin matattu ne.
Porque não podem mais morrer; pois são iguaes aos anjos, e são filhos de Deus, visto que são filhos da ressurreição.
37 Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
E que os mortos hão de resuscitar também o mostrou Moisés junto da sarça, quando chama ao Senhor Deus de Abraão, e Deus de Isaac, e Deus de Jacob.
38 Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
Ora Deus não é Deus de mortos, porém de vivos; porque para ele vivem todos.
39 Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
E, respondendo alguns dos escribas, disseram: Mestre, disseste bem.
40 Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.
E não ousavam perguntar-lhe mais coisa alguma.
41 Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’
E ele lhes disse: Como dizem que o Cristo é filho de David?
42 Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
Dizendo o mesmo David no livro dos salmos: Disse o Senhor ao meu Senhor: Assenta-te à minha direita,
43 sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
Até que eu ponha os teus inimigos por escabelo de teus pés.
44 Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”
De sorte que David lhe chama Senhor; e como é seu filho?
45 Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa,
E, ouvindo-o todo o povo, disse Jesus aos seus discípulos:
46 “Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa.
Guardai-vos dos escribas, que querem andar com vestidos compridos; e amam as saudações nas praças, e as principais cadeiras nas sinagogas, e os primeiros lugares nos banquetes;
47 Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”
Que devoram as casas das viúvas, fazendo, como pretexto, largas orações. Estes receberão maior condenação.

< Luka 20 >