< Luka 20 >

1 Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
Un de ces jours-là, comme Jésus enseignait le peuple dans le temple, et qu'il annonçait la bonne nouvelle, les Princes des prêtres et les Scribes survinrent avec les Anciens,
2 Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
et lui dirent: " Dites-nous par quelle autorité vous faites ces choses, ou qui vous a donné cette autorité? "
3 Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
Jésus leur répondit: " Moi aussi je vous ferai une question. Répondez-moi.
4 baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
Le baptême de Jean était-il du ciel, ou des hommes? "
5 Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
Mais ils faisaient entre eux cette réflexion: " Si nous répondons: Du ciel, il nous dira: Pourquoi n'avez-vous pas cru en lui?
6 Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
Et si nous répondons: Des hommes, tout le peuple nous lapidera, car il est persuadé que Jean était un prophète. "
7 Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
Ils lui répondirent donc qu'ils ne savaient d'où il était.
8 Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
" Et Moi, leur dit Jésus, je ne vous dis pas non plus par quelle autorité je fais ces choses. "
9 Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya.
Alors il se mit à dire au peuple cette parabole: " Un homme planta une vigne, et la loua à des vignerons; puis il s'en alla pour un temps assez long en pays étranger.
10 A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin’ya’yan inabin. Amma’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi.
La saison étant venue, il envoya un serviteur aux vignerons, afin qu'ils lui donnassent du produit de la vigne. Mais eux, l'ayant battu, le renvoyèrent les mains vides.
11 Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi.
Il envoya encore un autre serviteur; mais, l'ayant aussi battu et traité indignement, ils le renvoyèrent les mains vides.
12 Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.
Il en envoya un troisième; mais, lui aussi, les vignerons le blessèrent et le jetèrent dehors.
13 “Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’
Alors le maître de la vigne se dit: Que ferai-je? J'enverrai mon fils bien-aimé; peut-être qu'en le voyant ils auront pour lui du respect.
14 “Amma da’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’
Mais lorsque les vignerons le virent, ils se dirent entre eux: Celui-ci est l'héritier, tuons-le, afin que l'héritage soit à nous.
15 Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi. “To, me mai gonar inabin zai yi da su?
Et l'ayant jeté hors de la vigne, ils le tuèrent. Que leur fera donc le maître de la vigne?
16 Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.” Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”
Il viendra et exterminera ces vignerons, et donnera sa vigne à d'autres. " Ce qu'ayant entendu, ils dirent: " A Dieu ne plaise! "
17 Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’
Mais, fixant le regard sur eux, Jésus dit: " Qu'est-ce donc que cette parole de l'Ecriture: La pierre qu'ont rejetée ceux qui bâtissaient est devenue la pierre angulaire?
18 Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”
Quiconque tombera sur cette pierre sera brisé; et celui sur qui elle tombera, sera écrasé. "
19 Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.
Les Princes des prêtres et les Scribes cherchèrent à se saisir de lui à l'heure même; mais la crainte du peuple les retint, car ils comprenaient bien que c'était pour eux que Jésus avait dit cette parabole.
20 Sai suka sa masa ido, suka aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko.
Ils ne le perdirent donc pas de vue, et lui envoyèrent des gens apostés qui feignaient d'être justes, pour le surprendre dans ses paroles, afin de le livrer à l'autorité et au pouvoir du gouverneur.
21 Sai’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya.
Ces gens l'interrogèrent en ces termes: " Maître, nous savons que vous parlez et enseignez avec droiture, et sans faire acception de personne, mais que vous enseignez la voie de Dieu dans la vérité.
22 Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
Nous est-il permis, ou non, de payer le tribut à César? "
23 Ya gane makircinsu, sai ya ce musu,
Jésus, connaissant leur fourberie, leur dit: " Pourquoi me tentez-vous?
24 “Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?” Suka amsa, “Na Kaisar.”
Montrez-moi un denier. De qui porte-t-il l'effigie et le nom? " Ils lui répondirent: " De César. "
25 Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
Et il leur dit: " Rendez donc à César ce qui est à César, et à Dieu ce qui est à Dieu. "
26 Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.
Ainsi ils ne purent le prendre en défaut sur aucune parole devant le peuple; et admirant sa réponse, ils gardèrent le silence.
27 Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
Quelques-uns des Sadducéens, qui nient la résurrection, s'approchèrent alors et l'interrogèrent:
28 “Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.’
" Maître, lui dirent-ils, Moïse nous a donné cette loi: Si un homme, ayant une femme, meurt sans laisser d'enfants, que son frère prenne sa femme, et suscite des enfants à son frère.
29 To, an yi waɗansu’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba’ya’ya.
Or, il y avait sept frères; le premier prit une femme et mourut sans enfants.
30 Na biyun,
Le second prit sa femme, et mourut aussi sans enfants.
31 da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu’ya’ya.
Le troisième la prit ensuite, et de même tous les sept, et ils moururent sans laisser d'enfants.
32 A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
Après eux tous, la femme mourut aussi.
33 Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
Duquel donc, au temps de la résurrection, sera-t-elle la femme, car elle l'a été de tous les sept? "
34 Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn g165)
Jésus leur dit: " Les enfants de ce siècle se marient et sont donnés en mariage; (aiōn g165)
35 amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn g165)
mais ceux qui ont été trouvés dignes d'avoir part au siècle à venir et à la résurrection des morts, ne prennent point de femme et n'ont point de mari; (aiōn g165)
36 Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su’ya’yan Allah ne, tun da su’ya’yan tashin matattu ne.
aussi bien ne peuvent-ils plus mourir, puisqu'ils sont en comme les anges, et qu'ils sont fils de Dieu, étant fils de la résurrection.
37 Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
Mais que les morts ressuscitent, c'est ce que Moïse lui-même a fait connaître dans le passage du Buisson, lorsqu'il nomme le Seigneur: Le Dieu d'Abraham, le Dieu d'Isaac et le Dieu de Jacob.
38 Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
Or il n'est pas Dieu des morts, mais des vivants; car tous sont vivants devant lui. "
39 Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
Quelques-uns des Scribes, prenant la parole, lui dirent: " Maître, vous avez bien parlé. "
40 Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.
Et ils n'osaient plus lui poser aucune question.
41 Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’
Jésus leur dit: " Comment dit-on que le Christ est fils de David?
42 Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
David lui-même dit dans le livre des Psaumes: Le Seigneur a dit à mon Seigneur: Asseyez-vous à ma droite,
43 sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
jusqu'à ce que je fasse de vos ennemis l'escabeau de vos pieds. —
44 Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”
David l'appelle donc Seigneur; comment peut-il être son fils? "
45 Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa,
Tandis que tout le peuple l'écoutait, il dit à ses disciples:
46 “Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa.
" Gardez-vous des Scribes, qui se plaisent à se promener en longues robes; qui aiment à être salués dans les places publiques, à occuper les premiers sièges dans les synagogues et les premières places dans les festins:
47 Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”
ces gens qui dévorent les maisons des veuves, et font pour l'apparence de longues prières, subiront une condamnation plus sévère. "

< Luka 20 >