< Luka 20 >

1 Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
And it came to pass on one of those days, as he was teaching the people in the temple, and preaching the good news, the chief priests and the scholars with the elders stood near.
2 Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
And they spoke, saying to him, Tell us, by what authority are thou doing these things? Or who is he who gave thee this authority?
3 Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
And having answered, he said to them, I also will ask you one word, and ye tell me.
4 baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
The immersion of John, was it from heaven or from men?
5 Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
And they reasoned with themselves, saying, If we should say, From heaven, he will say, Why did ye not believe him?
6 Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
But if we say, From men, all the people will stone us, for they are convinced John is a prophet.
7 Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
And they replied not to know from where.
8 Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
And Jesus said to them, Neither do I tell you by what authority I do these things.
9 Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya.
And he began to speak this parable to the people. A man planted a vineyard, and leased it to farmers, and went abroad for a considerable time.
10 A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin’ya’yan inabin. Amma’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi.
And at the season he sent a bondman to the farmers, so that they would give him from the fruit of the vineyard. But having beaten him, the farmers sent him away empty.
11 Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi.
And he proceeded to send another bondman. And they, having beaten and shamefully treated, sent him also away empty.
12 Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.
And he proceeded to send a third. And they also having wounded this man, cast him out.
13 “Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’
And the lord of the vineyard said, What shall I do? I will send my beloved son. Perhaps they will be made ashamed after seeing this man.
14 “Amma da’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’
But when the farmers saw him, they deliberated among themselves, saying, This is the heir. Come, let us kill him, so that the inheritance may become ours.
15 Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi. “To, me mai gonar inabin zai yi da su?
And having cast him outside of the vineyard, they killed him. What therefore will the lord of the vineyard do to them?
16 Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.” Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”
He will come and destroy these farmers, and will give the vineyard to others. And having heard it, they said, May it not happen!
17 Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa, “‘Dutsen da magina suka ƙi, shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’
But having looked upon them, he said, What then is this that is written, The stone that those who build rejected, this became the head of the corner?
18 Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”
Every man who falls on that stone will be broken, but on whomever it may fall, it will grind him to dust.
19 Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.
And the chief priests and the scholars sought to throw hands on him in the same hour. And they were afraid, for they knew that he spoke this parable against them.
20 Sai suka sa masa ido, suka aiki’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko.
And having watched him, they sent forth insidious men pretending themselves to be righteous, so that they might take hold of his word, in order to deliver him up to the rule and to the authority of the governor.
21 Sai’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya.
And they questioned him, saying, Teacher, we know that thou speak and teach rightly, and thou do not accept a personage, but teach the way of God in truth,
22 Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”
Is it permitted for us to give tribute to Caesar or not?
23 Ya gane makircinsu, sai ya ce musu,
But having perceived their craftiness, he said to them, Why do ye try me?
24 “Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?” Suka amsa, “Na Kaisar.”
Display to me a denarius. Whose image and inscription has it? And having answered, they said, Caesar's.
25 Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”
And he said to them, Then render the things of Caesar to Caesar, and the things of God to God.
26 Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.
And they were unable to lay hold of his word before the people. And having marveled at his answer, they were silent.
27 Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa,
And some of the Sadducees having approached, those who say there is no resurrection, they questioned him,
28 “Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa’ya’ya.’
saying, Teacher, Moses wrote to us, if any brother dies, having a wife, and this man dies childless, that his brother should take his wife, and raise up seed to his brother.
29 To, an yi waɗansu’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba’ya’ya.
There were therefore seven brothers. And the first having taken a wife, died childless.
30 Na biyun,
And the second took the woman, and this man died childless.
31 da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu’ya’ya.
And the third likewise took her, and likewise also the seven; they left behind no children, and died.
32 A ƙarshe, ita macen ma ta mutu.
And last of all the woman also died.
33 Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”
In the resurrection therefore whose wife of them does she become? For the seven had her as wife.
34 Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, (aiōn g165)
And having answered, Jesus said to them, The sons of this age marry, and are given in marriage, (aiōn g165)
35 amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. (aiōn g165)
but those who are considered worthy to attain to that age, and the resurrection from the dead, neither marry, nor are given in marriage. (aiōn g165)
36 Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su’ya’yan Allah ne, tun da su’ya’yan tashin matattu ne.
For neither can they die any more, for they are like the agents, and are sons of God, being sons of the resurrection.
37 Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’
But that the dead are raised, even Moses showed at the Bush when he calls the Lord, the God of Abraham, and the God of Isaac, and the God of Jacob.
38 Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”
Now he is not God of the dead, but of the living, for all live to him.
39 Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!”
And some of the scholars having answered, they said, Teacher, thou said well.
40 Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.
For they no longer dared to question him anything.
41 Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’
And he said to them, How do they say the Christ is David's son?
42 Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura, “‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a hannun damana,
Even David himself says in the book of Psalms, The Lord said to my Lord, Sit thou at my right hand,
43 sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka.”’
until I will place thine enemies a footstool of thy feet.
44 Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”
David therefore calls him Lord, and how is he his son?
45 Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa,
And while all the people were listening, he said to his disciples,
46 “Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa.
Beware of the scholars, who desire to walk around in long robes, and love greetings in the marketplaces, and chief seats in the synagogues, and places of honor at the feasts,
47 Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”
who devour widows' houses, and in pretence make long prayers. These will receive greater damnation.

< Luka 20 >