< Luka 19 >

1 Yesu ya shiga Yeriko, yana ratsa ta cikinta.
I kad uðe u Jerihon i prolažaše kroza nj,
2 Akwai wani mutum a garin, mai suna Zakka. Shi shugaban masu karɓar haraji ne, mai arziki kuma.
I gle, èovjek po imenu Zakhej, koji bješe starješina carinièki, i bješe bogat,
3 Ya so yă ga ko wane ne Yesu, amma saboda taron, bai iya ba, domin shi gajere ne.
I iskaše da vidi Isusa da ga pozna; i ne mogaše od naroda, jer bješe maloga rasta;
4 Saboda haka, ya yi gaba da gudu, kuma ya hau itacen sikamo, don yă gan shi, tun da Yesu zai bi wannan hanyar ne.
I potrèavši naprijed, pope se na dud da ga vidi; jer mu je onuda trebalo proæi.
5 Da Yesu ya iso wurin, sai ya ɗaga ido sama, ya ce masa, “Zakka, ka yi maza ka sauka. Ni kam, dole in sauka a gidanka yau.”
I kad doðe Isus na ono mjesto, pogledavši gore vidje ga, i reèe mu: Zakheju! siði brzo; jer mi danas valja biti u tvojoj kuæi.
6 Sai ya sauka nan da nan, ya karɓe shi da murna.
I siðe brzo; i primi ga radujuæi se.
7 Dukan mutane suka ga haka, kuma suka fara gunaguni, suka ce, “Ya je don yă zama baƙon ‘mai zunubi.’”
I svi, kad vidješe, vikahu na njega govoreæi da grješnome èovjeku doðe u kuæu.
8 Amma Zakka ya tashi a tsaye, ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji! Nan take, rabin dukiyar da nake da shi, na ba wa matalauta. In kuma na taɓa cutan wani, a kan wani abu, zan mayar da shi ninki huɗu.”
A Zakhej stade i reèe Gospodu: Gospode! evo pola imanja svojega daæu siromasima, i ako sam koga zanio vratiæu onoliko èetvoro.
9 Sai Yesu ya ce masa, “Yau, ceto ya zo gidan nan, domin wannan mutum shi ma ɗan Ibrahim ne.
A Isus mu reèe: danas doðe spasenije kuæi ovoj; jer je i ovo sin Avraamov.
10 Saboda Ɗan Mutum ya zo ne, domin yă nemi abin da ya ɓata, yă cece shi kuma.”
Jer je sin èovjeèij došao da naðe i spase što je izgubljeno.
11 Yayinda suna cikin sauraron wannan, sai ya ci gaba da gaya musu wani misali, domin ya yi kusa da Urushalima, kuma mutanen suna tsammani mulkin Allah zai bayyana, nan da nan.
A kad oni to slušahu nastavi kazivati prièu; jer bješe blizu Jerusalima, i mišljahu da æe se odmah javiti carstvo Božije.
12 Ya ce, “Wani mutum mai martaba ya tafi wata ƙasa mai nisa don a naɗa shi sarki sa’an nan ya dawo.
Reèe dakle: jedan èovjek od dobra roda otide u daljnu zemlju da primi sebi carstvo, i da se vrati.
13 Saboda haka ya kira bayinsa goma ya ba su mina goma. Ya ce, ‘Ku yi kasuwanci da kuɗin nan, sai na dawo.’
Dozvavši pak deset svojijeh sluga dade im deset kesa, i reèe im: trgujte dok se ja vratim.
14 “Amma talakawansa suka ƙi shi, sai suka aikar da wakilai bayansa, domin su ce, ‘Ba mu son wannan mutum ya zama sarkinmu.’
I graðani njegovi mržahu na njega, i poslaše za njim poslanike govoreæi: neæemo da on caruje nad nama.
15 “Duk da haka, aka naɗa shi sarki, sa’an nan ya dawo gida. Sai ya aika aka kira bayin da ya ba su kuɗin, don yă san ribar da suka samu.
I kad se on vrati, pošto primi carstvo, reèe da dozovu one sluge kojima dade srebro, da vidi šta je koji dobio.
16 “Na fari ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar goma.’
Tada doðe prvi govoreæi: gospodaru! kesa tvoja donese deset kesa.
17 “Maigidan ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawana mai kirki! Tun da ka yi aminci a kan abu ƙanƙani, ka yi riƙon birane goma.’
I reèe mu: dobro, dobri slugo; kad si mi u malom bio vjeran evo ti vlast nad deset gradova.
18 “Na biyun ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar biyar.’
I doðe drugi govoreæi: gospodaru! kesa tvoja donese pet kesa.
19 “Maigidansa ya ce, ‘Kai ka yi riƙon birane biyar.’
A on reèe i onome: i ti budi nad pet gradova.
20 “Sai wani bawan ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ga minarka. Na ɓoye shi a wani ɗan tsumma.
I treæi doðe govoreæi: gospodaru! evo tvoja kesa koju sam zavezao u ubrus i èuvao.
21 Na ji tsoronka, don kai mai wuyan sha’ani ne. Kakan ɗauki abin da ba ka ajiye ba, kakan kuma yi girbin abin da ba ka shuka ba.’
Jer sam se bojao tebe: jer si èovjek tvrd: uzimaš što nijesi ostavio, i žnješ što nijesi sijao.
22 “Sai maigidansa, ya amsa ya ce, ‘Zan hukunta ka a kan kalmominka, kai mugun bawa! Ashe, ka san cewa ni mai wuyan sha’ani ne, nakan ɗauka abin da ban ajiye ba, ina kuma girbin abin da ban shuka ba?
A gospodar mu reèe: po tvojijem æu ti rijeèima suditi, zli slugo! znao si da sam ja tvrd èovjek, uzimam što nijesam ostavio, i žnjem što nijesam sijao:
23 Don me ba ka sa kuɗina a wajen ajiya, don in na dawo, in sami riba a kai ba?’
Pa zašto nijesi dao mojega srebra trgovcima, i ja došavši primio bih ga s dobitkom?
24 “Sai ya ce wa waɗanda suke tsaye a wajen, ‘Ku karɓi minarsa ku ba wa wanda yake da mina goma.’
I reèe onima što stajahu pred njim: uzmite od njega kesu i podajte onome što ima deset kesa.
25 “Suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ai, yana da guda goma ko!’
I rekoše mu: gospodaru! on ima deset kesa.
26 “Ya amsa ya ce, ‘Ina gaya muku, duk wanda yake da abu, za a ƙara masa. Amma wanda ba shi da shi kuwa, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe.
A on im odgovori: jer vam kažem da æe se svakome koji ima dati; a od onoga koji nema uzeæe se od njega i ono što ima.
27 Amma waɗannan abokan gābana, waɗanda ba su so in zama sarkinsu ba, ku kawo su nan, ku karkashe su, a gabana.’”
A one moje neprijatelje koji nijesu htjeli da ja budem car nad njima, dovedite amo, i isijecite preda mnom.
28 Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
I kazavši ovo poðe naprijed, i iðaše gore u Jerusalim.
29 Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
I kad se približi Vitfazi i Vitaniji kod gore koja se zvaše Maslinska, posla dva od uèenika svojijeh
30 “Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
Govoreæi: idite u to selo prema vama, i kad uðete u njega naæi æete magare privezano na koje nikakav èovjek nikad nije usjedao; odriješite ga i dovedite.
31 In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke kunce shi?’ Ku ce masa, ‘Ubangiji yana bukatarsa.’”
I ako vas ko upita: zašto driješite? ovako mu kažite: ono Gospodu treba.
32 Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
A kad otidoše poslani, naðoše kao što im kaza.
33 Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
A kad oni driješahu magare rekoše im gospodari od njega: zašto driješite magare?
34 Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
A oni rekoše: ono Gospodu treba.
35 Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
I dovedoše ga k Isusu, i baciše haljine svoje na magare, i posadiše Isusa.
36 Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
A kad iðaše, prostirahu haljine svoje po putu.
37 Da ya yi kusa da wurin da hanyar ta gangara zuwa Dutsen Zaitun, sai dukan taron almajirai suka fara yabon Allah, da muryoyi masu ƙarfi, da murna, saboda dukan ayyukan banmamaki da suka gani. Suna cewa,
A kad se približi veæ da siðe s gore Maslinske, poèe sve mnoštvo uèenika u radosti hvaliti Boga iza glasa za sva èudesa što su vidjeli,
38 “Mai albarka ne sarki wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Salama ta kasance a sama, da ɗaukaka kuma a can cikin sama!”
Govoreæi: blagosloven car koji ide u ime Gospodnje! mir na nebu i slava na visini!
39 Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce wa Yesu, “Malam, ka kwaɓi almajiranka!”
I neki fariseji iz naroda rekoše mu: uèitelju! zaprijeti uèenicima svojijem.
40 Ya amsa ya ce, “Ina gaya muku, ko da sun yi shiru, duwatsu za su fara kirari.”
I odgovarajuæi reèe im: kažem vam: ako oni uæute, kamenje æe povikati.
41 Da ya yi kusa da Urushalima, ya kuma ga birnin, sai ya yi kuka a kanta,
I kad se približi, ugleda grad i zaplaka za njim
42 kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
Govoreæi: kad bi i ti znao u ovaj tvoj dan što je za mir tvoj! ali je sad sakriveno od oèiju tvojijeh.
43 Ranakun za su auko miki, a lokacin da abokan gābanki za su gina bango gāba da ke, su kuma kewaye inda kike, za su kuma tsare kowane gefenki, su sa ke a tsakiya.
Jer æe doæi dani na tebe, i okružiæe te neprijatelji tvoji opkopima, i opkoliæe te, i obuzeæe te sa sviju strana;
44 Za su fyaɗa ke a ƙasa, ke da’ya’yan da suke cikin katanganki. Ba za su bar wani dutse a kan wani ba, saboda ba ki gane da lokacin da Allah zai ziyarce ki ba.”
I razbiæe tebe i djecu tvoju u tebi, i neæe ostaviti u tebi kamena na kamenu, zato što nijesi poznao vremena u kojemu si pohoðen.
45 Sai ya shiga filin haikali, ya fara korar masu sayar da kaya.
I ušavši u crkvu stade izgoniti one što prodavahu u njoj i kupovahu,
46 Ya ce musu, “A rubuce, yake cewa, ‘Gidana, zai zama gidan addu’a,’amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
Govoreæi im: u pismu stoji: dom moj dom je molitve, a vi naèiniste od njega peæinu hajduèku.
47 Kowace rana, ya yi ta koyarwa a haikalin. Amma manyan firistoci, da malaman dokoki, da shugabannin mutane, suna ƙoƙarin kashe shi.
I uèaše svaki dan u crkvi. A glavari sveštenièki i književnici i starješine narodne gledahu da ga pogube.
48 Amma ba su sami hanyar yin haka ba, domin kalmominsa sun kama hankalin dukan mutanen.
I ne nalažahu šta bi mu uèinili; jer sav narod iðaše za njim, i slušahu ga.

< Luka 19 >