< Luka 19 >

1 Yesu ya shiga Yeriko, yana ratsa ta cikinta.
And Jesus entered and passed through Jericho.
2 Akwai wani mutum a garin, mai suna Zakka. Shi shugaban masu karɓar haraji ne, mai arziki kuma.
And, behold, there was a man named Zacchaeus, who was the chief among the tax collectors, and he was rich.
3 Ya so yă ga ko wane ne Yesu, amma saboda taron, bai iya ba, domin shi gajere ne.
And he sought to see Jesus who he was; and could not for the crowd, because he was little of stature.
4 Saboda haka, ya yi gaba da gudu, kuma ya hau itacen sikamo, don yă gan shi, tun da Yesu zai bi wannan hanyar ne.
And he ran before, and climbed up upon a sycamore tree to see him: for he was to pass that way.
5 Da Yesu ya iso wurin, sai ya ɗaga ido sama, ya ce masa, “Zakka, ka yi maza ka sauka. Ni kam, dole in sauka a gidanka yau.”
And when Jesus came to the place, he looked up, and saw him, and said to him, Zacchaeus, make haste, and come down; for to day I must abide at thy house.
6 Sai ya sauka nan da nan, ya karɓe shi da murna.
And he made haste, and came down, and received him joyfully.
7 Dukan mutane suka ga haka, kuma suka fara gunaguni, suka ce, “Ya je don yă zama baƙon ‘mai zunubi.’”
And when they saw it, they all murmured, saying, That he was gone to be guest with a man that is a sinner.
8 Amma Zakka ya tashi a tsaye, ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji! Nan take, rabin dukiyar da nake da shi, na ba wa matalauta. In kuma na taɓa cutan wani, a kan wani abu, zan mayar da shi ninki huɗu.”
And Zacchaeus stood, and said to the Lord; Behold, Lord, the half of my goods I give to the poor; and if I have taken any thing from any man by false accusation, I restore him fourfold.
9 Sai Yesu ya ce masa, “Yau, ceto ya zo gidan nan, domin wannan mutum shi ma ɗan Ibrahim ne.
And Jesus said to him, This day is salvation come to this house, because he also is a son of Abraham.
10 Saboda Ɗan Mutum ya zo ne, domin yă nemi abin da ya ɓata, yă cece shi kuma.”
For the Son of man is come to seek and to save that which was lost.
11 Yayinda suna cikin sauraron wannan, sai ya ci gaba da gaya musu wani misali, domin ya yi kusa da Urushalima, kuma mutanen suna tsammani mulkin Allah zai bayyana, nan da nan.
And as they heard these things, he added and spoke a parable, because he was near to Jerusalem, and because they thought that the kingdom of God should immediately appear.
12 Ya ce, “Wani mutum mai martaba ya tafi wata ƙasa mai nisa don a naɗa shi sarki sa’an nan ya dawo.
He said therefore, A certain nobleman went into a far country to receive for himself a kingdom, and to return.
13 Saboda haka ya kira bayinsa goma ya ba su mina goma. Ya ce, ‘Ku yi kasuwanci da kuɗin nan, sai na dawo.’
And he called his ten servants, and delivered them ten pounds, and said to them, Occupy till I come.
14 “Amma talakawansa suka ƙi shi, sai suka aikar da wakilai bayansa, domin su ce, ‘Ba mu son wannan mutum ya zama sarkinmu.’
But his citizens hated him, and sent a message after him, saying, We will not have this man to reign over us.
15 “Duk da haka, aka naɗa shi sarki, sa’an nan ya dawo gida. Sai ya aika aka kira bayin da ya ba su kuɗin, don yă san ribar da suka samu.
And it came to pass, that when he had returned, having received the kingdom, then he commanded these servants to be called to him, to whom he had given the money, that he might know how much every man had gained by trading.
16 “Na fari ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar goma.’
Then came the first, saying, Lord, thy pound hath gained ten pounds.
17 “Maigidan ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawana mai kirki! Tun da ka yi aminci a kan abu ƙanƙani, ka yi riƙon birane goma.’
And he said to him, Well, thou good servant: because thou hast been faithful in a very little, have thou authority over ten cities.
18 “Na biyun ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, minarka ya sami ribar biyar.’
And the second came, saying, Lord, thy pound hath gained five pounds.
19 “Maigidansa ya ce, ‘Kai ka yi riƙon birane biyar.’
And he said likewise to him, Be thou also over five cities.
20 “Sai wani bawan ya zo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ga minarka. Na ɓoye shi a wani ɗan tsumma.
And another came, saying, Lord, behold, here is thy pound, which I have kept laid up in a napkin:
21 Na ji tsoronka, don kai mai wuyan sha’ani ne. Kakan ɗauki abin da ba ka ajiye ba, kakan kuma yi girbin abin da ba ka shuka ba.’
For I feared thee, because thou art an austere man: thou takest up what thou didst not lay down, and reapest what thou didst not sow.
22 “Sai maigidansa, ya amsa ya ce, ‘Zan hukunta ka a kan kalmominka, kai mugun bawa! Ashe, ka san cewa ni mai wuyan sha’ani ne, nakan ɗauka abin da ban ajiye ba, ina kuma girbin abin da ban shuka ba?
And he saith to him, Out of thy own mouth will I judge thee, thou wicked servant. Thou knewest that I was an austere man, taking up what I laid not down, and reaping what I did not sow:
23 Don me ba ka sa kuɗina a wajen ajiya, don in na dawo, in sami riba a kai ba?’
Why then gavest thou not my money into the bank, that at my coming I might have required my own with interest?
24 “Sai ya ce wa waɗanda suke tsaye a wajen, ‘Ku karɓi minarsa ku ba wa wanda yake da mina goma.’
And he said to them that stood by, Take from him the pound, and give it to him that hath ten pounds.
25 “Suka ce, ‘Ranka yă daɗe, ai, yana da guda goma ko!’
( And they said to him, Lord, he hath ten pounds.)
26 “Ya amsa ya ce, ‘Ina gaya muku, duk wanda yake da abu, za a ƙara masa. Amma wanda ba shi da shi kuwa, ko abin da yake da shi ma, za a karɓe.
For I say to you, That to every one who hath shall be given; and from him that hath not, even what he hath shall be taken away from him.
27 Amma waɗannan abokan gābana, waɗanda ba su so in zama sarkinsu ba, ku kawo su nan, ku karkashe su, a gabana.’”
But those my enemies, who would not that I should reign over them, bring here, and slay them before me.
28 Bayan Yesu ya yi wannan magana, sai ya yi gaba zuwa Urushalima.
And when he had thus spoken, he went before, going up to Jerusalem.
29 Da ya kai kusa da Betfaji da Betani, a tudun da ake kira Dutsen Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, ya ce musu,
And it came to pass, when he had come near to Bethphage and Bethany, at the mount called the mount of Olives, he sent two of his disciples,
30 “Ku je ƙauyen da yake gaba da ku. Da kuna shiga, za ku tarar da wani ɗan jaki, wadda ba wanda ya taɓa hawa, a daure a wurin. Ku kunce shi ku kawo nan.
Saying, Go ye into the village opposite you; in which at your entering ye shall find a colt tied, on which yet never man sat: loose him, and bring him here.
31 In wani ya tambaye ku, ‘Don me kuke kunce shi?’ Ku ce masa, ‘Ubangiji yana bukatarsa.’”
And if any man shall ask you, Why do ye loose him? thus shall ye say to him, Because the Lord hath need of him.
32 Waɗanda aka aika su yi gaba suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya gaya musu.
And they that were sent went, and found even as he had said to them.
33 Suna cikin kunce ɗan jakin, sai masu ɗan jakin suka ce musu, “Don me kuke kunce shi?”
And as they were loosing the colt, its owners said to them, Why loose ye the colt?
34 Suka amsa suka ce, “Ubangiji ne na bukatarsa.”
And they said, The Lord hath need of him.
35 Suka kawo shi wurin Yesu. Suka sa rigunarsu a kan ɗan jakin, sa’an nan suka sa Yesu a kai.
And they brought him to Jesus: and they cast their garments upon the colt, and they set Jesus on it.
36 Yana cikin tafiya, sai mutane suka shimfiɗa rigunarsu a kan hanya.
And as he went, they spread their clothes in the way.
37 Da ya yi kusa da wurin da hanyar ta gangara zuwa Dutsen Zaitun, sai dukan taron almajirai suka fara yabon Allah, da muryoyi masu ƙarfi, da murna, saboda dukan ayyukan banmamaki da suka gani. Suna cewa,
And when he had come near, even now at the descent of the mount of Olives, the whole multitude of the disciples began to rejoice and praise God with a loud voice for all the mighty works that they had seen;
38 “Mai albarka ne sarki wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji!” “Salama ta kasance a sama, da ɗaukaka kuma a can cikin sama!”
Saying, Blessed be the King that cometh in the name of the Lord: peace in heaven, and glory in the highest.
39 Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce wa Yesu, “Malam, ka kwaɓi almajiranka!”
And some of the Pharisees from among the multitude said to him, Master, rebuke thy disciples.
40 Ya amsa ya ce, “Ina gaya muku, ko da sun yi shiru, duwatsu za su fara kirari.”
And he answered and said to them, I tell you that, if these should hold their peace, the stones would immediately cry out.
41 Da ya yi kusa da Urushalima, ya kuma ga birnin, sai ya yi kuka a kanta,
And when he had come near, he beheld the city, and wept over it,
42 kuma ya ce, “In ke, ko ke ɗin ma, dā ma kin san abin da zai kawo miki salama a wannan rana, amma yanzu an ɓoye shi daga idanunki.
Saying, If thou hadst known, even thou, at least in this thy day, the things which belong to thy peace! but now they are hid from thy eyes.
43 Ranakun za su auko miki, a lokacin da abokan gābanki za su gina bango gāba da ke, su kuma kewaye inda kike, za su kuma tsare kowane gefenki, su sa ke a tsakiya.
For the days shall come upon thee, that thy enemies shall cast a trench about thee, and surround thee, and keep thee in on every side,
44 Za su fyaɗa ke a ƙasa, ke da’ya’yan da suke cikin katanganki. Ba za su bar wani dutse a kan wani ba, saboda ba ki gane da lokacin da Allah zai ziyarce ki ba.”
And shall lay thee even with the ground, and thy children within thee; and they shall not leave in thee one stone upon another; because thou knewest not the time of thy visitation.
45 Sai ya shiga filin haikali, ya fara korar masu sayar da kaya.
And he went into the temple, and began to cast out them that sold in it, and them that bought;
46 Ya ce musu, “A rubuce, yake cewa, ‘Gidana, zai zama gidan addu’a,’amma ga shi kun mai da shi ‘kogon’yan fashi.’”
Saying to them, It is written, My house is the house of prayer: but ye have made it a den of thieves.
47 Kowace rana, ya yi ta koyarwa a haikalin. Amma manyan firistoci, da malaman dokoki, da shugabannin mutane, suna ƙoƙarin kashe shi.
And he taught daily in the temple. But the chief priests and the scribes and the chief of the people sought to destroy him,
48 Amma ba su sami hanyar yin haka ba, domin kalmominsa sun kama hankalin dukan mutanen.
And could not find what they might do: for all the people were very attentive to hear him.

< Luka 19 >