< Luka 18 >

1 Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
Сказав же й приповість їм про те, що треба по всяк час молитись, а не внивати,
2 Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
глаголючи: Один суддя був у якомусь городі, й Бога ж бояв ся, і чоловіка не соромив ся.
3 A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
Вдовиця ж була одна у городі тім, і прийшла до него, кажучи: Пометись за мене над противником моїм.
4 “An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
І не хотїв довго, потім же каже в собі: Хоч і Бога не боюсь, і чоловіка не соромлюсь,
5 amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
то, що докучав менї вдова ся, помщусь за неї, щоб, без перестану ходячи, не докучала менї.
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
Рече ж Господь: Слухайте, що суддя неправедний каже!
7 Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
Бог же чи не помстив ся б за вибраних своїх, що голосять до Него день і ніч, хоч довго терпить про них?
8 Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
Глаголю вам, що помстить ся за них незабаром. Тільки ж Син чоловічий прийшовши, чи знайде віру на землї?
9 Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
Сказав же й до инших, що вповали на себе, що вони праведні, та гордували другими, приповість сю:
10 “Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
Два чоловіки ввійшли в церкву помолитись: один Фарисей, а другий митник.
11 Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
фарисей, ставши, так у собі молив ся: Боже, дякую Тобі, що я не такий, як инші люде, здирщики, неправедні, перелюбні, або як оцей митник.
12 Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
Я пощу два рази на тиждень, і даю десятину з усього, що придбаю.
13 “Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
А митник, оддалеки ставши, не хотів і очей до неба звести, а бив у груди себе, кажучи: Боже, милостивий будь менї грішному.
14 “Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
Глаголю вам: пійшов сей до дому свого оправданий більш, нїж той; бо кожен, хто несеть ся вгору, принизить ся; хто ж принижуєть ся, пійде вгору.
15 Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
Приносили ж йому й дїтей, щоб до них приторкнувсь; бачивши ж ученики, заказували їм.
16 Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
Ісус же, покликавши їх, рече: Пустіть дїток приходити до мене й не боронїть їм; таких бо царство Боже.
17 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
Істино глаголю вам: Хто не прийме царства Божого, як дитина, не ввійде в него.
18 Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
І питав Його один старшина, кажучи: Учителю благий, що робивши життв вічне насліджу. (aiōnios g166)
19 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
Рече ж йому Ісус: Чого мене звеш благим? нїхто не благий, тільки один Бог.
20 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
Заповіді знаєш: Не чини перелюбу, Не вбивай. Не кради. Не сьвідкуй криво, Поважай батька твого й матїр твою.
21 Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
Він же каже: Се все хоронив я з малку мого.
22 Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
Почувши ж се Ісус, рече йому: Ще одного тобі недостає: усе, що маєш, продай та й роздай убогим, і мати меш скарб на небі; та й приходь ійди слїдом за мною.
23 Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
Він же, почувши се, став вельми сумний, був бо дуже багатий.
24 Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
Побачивши ж його Ісус, що вельми сумний став, рече: Як тяжко багацтва маючи увійти в царство Боже!
25 Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
Легше бо верблюдові кріз ушко голки пройти, нїж багатому в царство Боже ввійти.
26 Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
Казали ж ті, що чули: То хто ж може спастись?
27 Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
Він же рече: Неможливе у людей - можливе у Бога.
28 Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
Каже ж Петр: Ось ми покинули все, та й пійшли слїдом за Тобою.
29 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
Він же рече їм: Істино, істино глаголю вам: Що нема нікого, хто покинув господу, або родителїв, або братів, або жінку, або дїти задля царства Божого,
30 da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
та й не приняв багато більше часу сього, а в віку будучому життв вічне. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
Узявши ж дванайцятьох, рече до них: Оце йдемо в Єрусалим, і станеть ся все, що написано через, пророків, Синові чоловічому.
32 Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
Буде бо виданий поганам, і насьміхатимуть ся з Него, й зневажати муть Його, й плювати муть на Него,
33 za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
і бивши убють Його; а третього дня воскресне.
34 Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
А вони нїчого того не зрозуміли; й було слово се закрите від них, і не розуміли глаголаного.
35 Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
Стало ся ж, як наближав ся до Єрихона, один слїпий сидів при дорозї просячи;
36 Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
чувши ж, що народ йде мимо, спитав, що б се було.
37 Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
Сказали ж йому, що Ісус Назарянин іде мимо.
38 Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
І покликнув, кажучи: Ісусе, сину Давидів, помилуй мене.
39 Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
А ті, що йшли попереду, сварили на него, щоб мовчав; він же ще більш кричав: Сину Давидів, помилуй мене.
40 Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
Ставши ж Ісус, звелїв його привести до себе; як же наближив ся він, спитав його,
41 “Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
глаголючи: Що хочеш, щоб вробив тобі? Він же каже: Господи, щоб я прозрів.
42 Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
А Ісус рече йому: Прозри: віра твоя спасла тебе.
43 Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.
І зараз прозрів, та й пійшов слїдом за Ним, прославляючи Бога; і ввесь народ, побачивши се, оддав хвалу Богові.

< Luka 18 >