< Luka 18 >

1 Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
Sade han ock en liknelse till dem derom, att man skall alltid bedja, och icke förtröttas;
2 Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
Sägandes: En domare var uti en stad, den icke fruktade Gud, och ej heller hade försyn för några mennisko;
3 A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
Så var i samma stad en enka; hon kom till honom, och sade: Hjelp mig ifrå min trätobroder.
4 “An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
Och han ville icke till någon tid. Sedan sade han vid sig: Ändock jag icke fruktar Gud, ej heller hafver försyn för någon mennisko;
5 amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
Dock, fördenskull att denna enkan öfverfaller mig så svåra, måste jag fly henne rätt, att hon icke skall komma på det sista, och ropa på mig.
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
Och sade Herren: Hörer här, hvad den orätta domaren säger.
7 Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
Skulle ock icke Gud hämnas sina utkorade, som ropa till honom dag och natt; skulle han hafva tålamod dermed?
8 Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
Jag säger eder, att han skall hämnas dem snarliga. Dock likväl, då menniskones Son kommer, månn han skall finna tro på jordene?
9 Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
Sade han ock till somliga, som tröste på sig sjelfva, att de voro rättfärdige, och försmådde andra, denna liknelsen:
10 “Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
Två män gingo upp i templet till att bedja; den ene en Pharisee, och den andre en Publican.
11 Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
Phariseen stod och bad så vid sig sjelf: Jag tackar dig Gud, att jag är icke såsom andra menniskor, röfvare, orättfärdige, horkarlar, eller ock såsom denne Publicanen.
12 Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
Jag fastar två resor i veckone, och gifver tiond af allt det jag äger.
13 “Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
Och Publicanen stod långt ifrån, och ville icke lyfta sin ögon upp till himmelen; utan slog sig för sitt bröst, och sade: Gud, miskunda dig öfver mig syndare.
14 “Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
Jag säger eder: Denne gick dädan hem igen rättfärdigad, mer än den andre; ty den sig upphöjer, han varder förnedrad; och den sig förnedrar, han varder upphöjd.
15 Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
Så båro de ock barn till honom, att han skulle taga på dem; då hans Lärjungar det sågo, näpste de dem.
16 Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
Men Jesus kallade dem till sig, och sade: Låter barnen komma till mig, och förmener dem icke; ty sådana hörer Guds rike till.
17 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
Sannerliga säger jag eder: Hvilken som icke tager Guds rike som ett barn, han skall icke komma derin.
18 Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
Och frågade honom en öfverste, sägandes: Gode Mästar, hvad skall jag göra, att jag må få evinnerligit lif? (aiōnios g166)
19 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
Sade Jesus till honom: Hvi kallar du mig godan? Ingen är god, utan allena Gud.
20 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
Budorden vetst du: Du skall icke bedrifva hor; du skall icke dräpa; du skall icke stjäla; du skall icke säga falskt vittnesbörd; du skall ära din fader och dina moder.
21 Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
Då sade han: Allt detta hafver jag hållit af min ungdom.
22 Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
Då Jesus det hörde, sade han till honom: Än fattas dig ett; sälj bort allt det du hafver, och skift emellan de fattiga, och du skall få en skatt i himmelen; och kom, och följ mig.
23 Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
Då han det hörde, vardt han storliga bedröfvad; ty han var ganska rik.
24 Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
Då Jesus såg honom vara mägta bedröfvad, sade han: O! med huru stor plats komma de i Guds rike, som penningar hafva;
25 Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
Ty snarare kan en camel gå igenom ett nålsöga, än en riker komma in i Guds rike.
26 Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
Då sade de som det hörde: Ho kan då varda salig?
27 Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
Men han sade: Det omöjeligit är för menniskom, det är möjeligit för Gud.
28 Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
Då sade Petrus: Si, vi hafve all ting öfvergifvit, och följt dig.
29 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
Sade han till dem: Sannerliga säger jag eder; ingen är den som hafver öfvergifvit hus, eller föräldrar, eller bröder, eller hustru, eller barn, för Guds rikes skull;
30 da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
Den icke skall igenfå mycket mer i denna tiden, och i tillkommande verld evinnerligit lif. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
Då tog Jesus till sig de tolf, och sade till dem: Si, vi gåm upp till Jerusalem, och all ting skola fullbordad varda, som skrifven äro af Propheterna om menniskones Son.
32 Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
Ty han skall öfverantvardas Hedningom, och begabbas, och försmädas, och bespottas.
33 za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
Och sedan de hafva hudflängt honom, skola de döda honom; och tredje dagen skall han uppstå igen.
34 Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
Men de förstodo der intet af, och talet var dem så fördoldt, att de icke förstodo hvad som sades.
35 Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
Så hände sig, att när han kom in mot Jericho, satt en blinder vid vägen, och tiggde.
36 Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
Och när han hörde folket framgå, frågade han hvad det var?
37 Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
Då sade de till honom, att Jesus af Nazareth gick der fram.
38 Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Då ropade han, och sade: Jesu, Davids Son, varkunna dig öfver mig.
39 Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Men de, som föregingo, näpste honom, att han skulle tiga; men han ropade dessmer: Davids Son, varkunna dig öfver mig.
40 Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
Då stadnade Jesus, och böd leda honom till sig. Då han kom fram, frågade han honom,
41 “Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
Sägandes: Hvad vill du, att jag skall göra dig? Då sade han: Herre, att jag måtte få min syn.
42 Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
Och Jesus sade till honom: Haf din syn; din tro hafver frälst dig.
43 Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.
Och straxt fick han sin syn igen, och följde honom, prisandes Gud. Och allt folket, som detta sågo, lofvade Gud.

< Luka 18 >