< Luka 18 >

1 Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
Hange wekaaila mpyani netakewe kulompa daima, alekekuta etamaa.
2 Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
Akamitambula, “Aokole mulamuli pakesale fulani, hange shanga aumwogopile Itunda nukuaheshimu eantu.
3 A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
Aukole mujane pakesale nekanso, nung'wenso aewimuhanga nkua yeedu, nukutambula, “Nzaelye mpate ehakiane numupenzani wane.
4 “An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
Kumatungo edu shangaaukole tayali kumusaidila, lakini baada amatungo akatambula munkolo akwe, ataitule unene shanganumwogopile Itunda ang'wi kumuheshimu umuntu,
5 amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
lakini kunsoko umujane uyu ukunsumbula nukumusaidela wapate ehaki akwe, waleke kunkatalya kwa kunezela mala kwa mala.”
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
Kuite umukulu wekalunga, “Tegeelyi nautambue nuanso umulamuli nuanso nedhalimu.
7 Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
Ite Itunda shanga ukuleta ehaki kwateule akwe neakumukela mung'we nuutiku? Ite nuanso shaukiumelyane kung'wao?
8 Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
Kumuila kina ukuleta ehaki kung'wa kwakukaya. Lakini ematungo nuzie ung'wana wang'wa Adamu, ite ukuuhangane uhueli muunkumbigulu?”
9 Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
Uu wikaaela mpyani eye kuantu baadhi hange niiona eenso kina akete ehaki nukuazalau eantu niangiza.
10 “Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
Antu abeele anankie kulongola mihekalu kusali: ung'wi Farisayo ung'wi mutoza ushuru.
11 Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
Ufarisayo wekimeka nukulompa aya migulya lakwe ung'wenso, Itunda kusongeelya kunsoko unene singa kipyani neantu niangiza kuita eahegelya, antu nishanga aaminifu, agoolyi, ang'wi anga yuyu umutoza ushulu.
12 Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
Nefunga mahiku abeele kuwiki. Neepumya ezaka mumapato ane ehi nenepata.
13 “Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
Lakini nuanso umutoza ushulu, aewimekile kule, shanga auwezilye ata ukuhumbula emiho akwe kilunde, akakuanga kekua kakwe wekalunga, Itunda ngoze unene nimunya milandu.”
14 “Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
Kumuila, umuntu nuanso ausukile kito akize uaeeigwe etai kukela umuya, kunsoko uyu nuikulya wisimigwa, lakini uyu nuisimya wehumbulwa.
15 Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
Eantu amuletee eana ao neadabu, kuite ahume kuaamba, lakini eamanyisigwa akwe naaine nanso, akaagilya.
16 Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
Lakini u Yesu wakaitanga kung'wakwe wekalunga, “Aleki ana nianino aze kitalane, wala lekikuagilya. Kundogoelyo utemi wang'wi Tunda waantu anga nianso.
17 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
Amini kumuila umuntu wehi nishanga ukusengelya utemi wang'wi Tunda anga ana neanino shangaukingela.”
18 Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
Mutawa ung'wi aumukoilye, wikalunga, 'Mwalimu namuza ntende ule nuusale upanga wakale nakale? (aiōnios g166)
19 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
U Yesu wikamuila, “Kuneke ukunintanga numuza? Kutile umuntu numuza, ila Itunda wing'wene du.
20 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
Umamanyilene emalago-lekakugoolya, lekakubulaga, lekakia, lekakutambula uteele, aheshimu ebaba ako numama ako.
21 Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
Umutawala nuanso wekalunga, “Imakani ayaite numaambile kupuma uhumba wane.
22 Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
U Yesu naewigule nanso wikaaila, “Upungukewe nekentu king'wi. Lazima ugulye ehi nukete aagawele awa niagila, nuewe ukutuwa nehazina kilunde kuite nzuu, uuntyate.
23 Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
Lakini umugole naewigulye nanso wekapata kenyauai lukulu, kunsoko ae mugole lukulu.
24 Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
Hange u Yesu wikamugoza nauambilwe ikenyauai ikulu wikalunga, 'Kuule neekatula ikaku eagole kingela ku utemi wang'wi Tunda!
25 Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
Kundogoelyo itotu ikulu kungamea kukela mitundu la sindano, kukela eugole kingela utemi wang'wi Tunda.”
26 Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
Awa naeigulye nanso, ekalunga, “Nyenyu gwa, nuekaweza kuokolewa?
27 Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
U Yesu wikasukilya, “Imakani neshangaawezekanile kwa anadamu kung'wi Tunda awezekanile.”
28 Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
U Petelo wikalunga, “Uu usese kaleka kila ekentu nakakutyata uewe.”
29 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
Hange u Yesu wikaaila, hueli kumuela kina kutile muntu nulekile enyumba ang'wi musungu, ang'wi munyandugu ang'wi aleli, ang'wi ana, kunsoko autemi wang'wi Tunda,
30 da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
kuite shanga ukupokela nedu kukela muunkumbigulu uwu, numuunkumbigulu uwu nuuzile upanga wakale na kale. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
Baada akuilingela awa nekumi na mbele, wikaaila, goza, kuunankela kulongoe ku Yerusalemu, ne makani ehi naandekilwe neanyakedagu kuhusu ung'wana wang'wa Adamu akukamileka.
32 Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
Kundogoelyo ukuambwa mumekono amataifa akumudhiki nukumutenda ejeuri, nukumutyela emate.
33 za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
Baada akumukua iiboko akumubulaga nuluhiku lakatatu ukiiuka.”
34 Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
Shanga ealengile imakani nanso, nulukani ulu ite aelupihilwe kung'wao, hange shangaaealengile emakani naatambuwe.
35 Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
Ikatula u Yesu naauhugie ku Yeriko, muntu ung'wi mupoku aewikie mumpelompelo abalabala aeukulompa ugunwa,
36 Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
naewigule umilundo wa antu ukeile akakolya ntuni niipumie.
37 Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
Eekamuila kina u Yesu nua Nazareti ukeile.
38 Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Kuite umupoku wekalela kululi, wikalunga, Yesu, ng'wana wang'wa Daudi nehulumele.” Awa naakugenda ekamukenela umupoku nuanso, ekamuela kilaga.
39 Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Uugwa awo naza atongee, akamukenda ite wakilage, kuiti u ng'wenso ai ukiile ikilo nangahu kitunta u luli Ee, ng'wana wang'wa Daudi unkendepe.
40 Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
U Yesu wikimeka akaamulu umuntu nuanso waletwe pang'wa akwe. Hange umupoku nuanso nauhumbie, U Yesu wikamukolya,
41 “Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
“Utakile nukutendele ntuni? Akalunga, “Bwana ntakile kuona.”
42 Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
U Yesu wikamuila, “Upegwe kuona. Uhueli wako wakukomya.”
43 Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.
Uu wekapegwa kuona, akamutyata u Yesu nukumukulya Itunda. Naaine ileile eantu ehi akamukulya Itunda.

< Luka 18 >