< Luka 18 >

1 Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
Il leur proposait aussi cette parabole, sur ce qu’il faut toujours prier, et ne se lasser jamais.
2 Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
Il y avait, disait-il, dans une certaine ville un juge qui ne craignait point Dieu, et ne se souciait point des hommes.
3 A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
Or il y avait une veuve dans cette même ville, et elle venait à lui, disant: Faites-moi justice de mon adversaire.
4 “An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
Et il ne le voulut pas pendant longtemps. Mais ensuite il dit en lui-même: Quoique je ne craigne point Dieu et ne me soucie point des hommes,
5 amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
Cependant, parce que cette femme m’importune, je lui ferai justice, de peur qu’à la fin elle ne vienne me faire quelque affront.
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
Le Seigneur ajouta: Entendez ce que dit le juge d’iniquité:
7 Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
Et Dieu ne vengera pas ses élus, qui crient vers lui jour et nuit, et il usera de délai pour eux?
8 Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
Je vous dis qu’il les vengera bientôt. Mais quand le Fils de l’homme viendra, pensez-vous qu’il trouve de la foi sur la terre?
9 Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
Il dit encore cette parabole pour quelques-uns qui se confiaient en eux-mêmes comme étant justes, et méprisaient les autres:
10 “Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
Deux hommes montèrent au temple pour prier; un pharisien et un publicain.
11 Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
Le pharisien, se tenant en avant, priait ainsi en lui-même: Ô Dieu, je vous rends grâces de ce que je ne suis pas comme le reste des hommes, qui sont voleurs, injustes, adultères; ni même comme ce publicain.
12 Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
Je jeune deux fois la semaine; je paie la dîme de tout ce que je possède.
13 “Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
Et le publicain, se tenant éloigné, n’osait pas même lever les yeux au ciel; mais il frappait sa poitrine, disant: Ô Dieu, ayez pitié de moi qui suis un pécheur.
14 “Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
Je vous le dis, celui-ci s en retourna justifié dans sa maison, et non pas l’autre: car quiconque s’exalte sera humilié, et quiconque s’humilie sera exalté.
15 Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
On lui portait aussi les petits enfants, pour qu’il les touchât. Ce que les disciples voyant, ils les rebutaient.
16 Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
Mais Jésus les appelant, dit: Laissez les enfants venir à moi, et ne les empêchez point; car à de tels est le royaume de Dieu.
17 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
En vérité je vous le dis: Quiconque ne recevra point comme un enfant le royaume de Dieu, n’y entrera point.
18 Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
Un des principaux l’interrogea, disant: Bon maître, que ferai-je pour posséder la vie éternelle? (aiōnios g166)
19 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
Jésus lui dit: Pourquoi m’appelles-tu bon? Nul n’est bon que Dieu seul.
20 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
Tu connais les commandements: Tu ne tueras point: Tu ne commettras point d’adultère: Tu ne porteras point faux témoignage: Honore ton père et ta mère.
21 Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
Il répondit: J’ai observé tout cela depuis ma jeunesse.
22 Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
Ce qu’entendant, Jésus lui dit: Une chose encore te manque: vends tout ce que tu as et donne-le aux pauvres, et tu auras un trésor dans le ciel: viens alors, et suis-moi.
23 Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
Mais lui, ces paroles entendues, fut contristé, parce qu’il était fort riche.
24 Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
Or Jésus le voyant devenir triste, dit: Que ceux qui ont les richesses entreront difficilement dans le royaume de Dieu!
25 Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
Il est plus facile à un chameau de passer par le chas d’une aiguille, qu’à un riche d’entrer dans le royaume de Dieu.
26 Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
Ceux qui l’écoutaient demandèrent: Et qui peut donc être sauvé?
27 Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
Il leur répondit: Ce qui est impossible aux hommes est possible à Dieu.
28 Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
Alors Pierre dit: Et nous, voici que nous avons tout quitté pour vous suivre.
29 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
Jésus leur répliqua: En vérité, je vous le dis, il n’est personne qui ait quitté ou maison, ou parents, ou frères, ou femme, ou enfants, à cause du royaume de Dieu,
30 da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
Qui ne reçoive beaucoup plus en ce temps même, et, dans le siècle à venir, la vie éternelle. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
Ensuite Jésus prit à parties douze et leur dit: Voici que nous montons à Jérusalem, et que s’accomplira tout ce qui a été écrit par les prophètes touchant le Fils de l’homme;
32 Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
Car il sera livré aux gentils, et raillé, et flagellé, et couvert de crachats;
33 za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
Et après qu’ils l’auront flagellé, ils le feront mourir, et le troisième jour, il ressuscitera.
34 Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
Mais les apôtres ne comprirent rien de ces choses, et cette parole leur était cachée; ainsi ils ne comprenaient point ce qui leur était dit.
35 Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
Or il arriva, lorsqu’il approchait de Jéricho, qu’un aveugle était assis au bord du chemin, mendiant.
36 Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
Et entendant la foule qui suivait le chemin, il demanda ce que c’était.
37 Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
On lui dit que Jésus de Nazareth passait.
38 Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Alors il cria, disant: Jésus, fils de David, ayez pitié de moi!
39 Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Ceux qui allaient devant, le gourmandaient pour qu’il se tût. Mais il criait beaucoup plus encore: Fils de David, ayez pitié de moi!
40 Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
Or Jésus s’arrêtant, ordonna qu’on le lui amenât. Et quand il se fut approché, il l’interrogea,
41 “Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
Disant: Que veux-tu que je te fasse? Il répondit: Seigneur, que je voie.
42 Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
Et Jésus lui dit: Vois; ta foi t’a sauvé.
43 Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.
Et aussitôt il vit, et il le suivait glorifiant Dieu. Et tout le peuple, voyant cela, donna louange à Dieu.

< Luka 18 >