< Luka 18 >

1 Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
He was speaking then (and *ko) a parable to them about it needing always to pray (they *no) and not to lose heart
2 Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
saying; A judge certain there was in a certain city God not fearing and man not respecting.
3 A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
A widow then there was in the city that and she was coming to him saying; do avenge me of the adversary of mine.
4 “An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
And not (he was desiring [to do] *N+kO) for a time. afterward however he said within himself; If even God not I fear (nor *N+kO) man respect,
5 amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
because yet it occasioning me trouble widow this I will avenge her, so that not to end coming she may exhaust me.
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
Said then the Lord; do hear what the judge unrighteous says;
7 Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
And God certainly not (may do *N+kO) the avenging of the elect of Him the [ones] crying out (to *k) (to Him *N+kO) day and night, and (be patient *N+kO) in regard to them?
8 Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
I say to you that He will carry out the avenging of them with speed. Nevertheless the Son of Man having come surely not will He find faith on the earth?
9 Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
He spoke now also to some having trusted in themselves that they are righteous and (despising *NK+o) the others parable this.
10 “Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
Men two went up into the temple to pray, the one a Pharisee and the other a tax collector.
11 Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
The Pharisee having stood toward himself these things was praying; O God, I thank You that not I am (like *NK+o) the rest of the men — swindlers, unrighteous, adulterers — or even like this tax collector.
12 Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
I fast twice in the week, I tithe all things as much as I gain.
13 “Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
(and *ko) (but *no) the tax collector afar off having stood not was willing not even the eyes to lift up to heaven but was striking (into *k) the breast (of him *NK+o) saying: O God, do be merciful to me to the sinner!
14 “Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
I say to you; went down this one justified to the house of him (rather than *k) (compared with *n+o) (that [one]. *N+kO) For everyone who is exalting himself will be humbled, the [one] however humbling himself will be exalted.
15 Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
They were bringing then to Him also the infants that them He may touch; having seen however the disciples (were rebuking *N+kO) them.
16 Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
But Jesus (called *N+kO) them (speaking; *N+kO) do permit the little children to come to Me and not do forbid them; for of such is the kingdom of God.
17 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
Amen I say to you; who[ever] (maybe *N+kO) not shall receive the kingdom of God as a child, certainly not shall enter into it.
18 Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
And asked a certain Him ruler saying; Teacher good, what having done life eternal will I inherit? (aiōnios g166)
19 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
Said then to him Jesus; Why Me you call good? No [one is] good only except one God.
20 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
The commandments You know: Not shall you commit adultery, not shall you murder, not shall you steal, not shall you bear false witness, do honor the father of you and the mother (of you. *k)
21 Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
And he said; These all (I kept *N+kO) from [the] youth (of mine. *ko)
22 Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
Having heard then (these things *k) Jesus said to him; Yet one thing to you is lacking: All as much as you have do sell and do distribute to [the] poor, and you will have treasure in (the *no) (heavens; *N+kO) and come, do follow Me.
23 Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
And having heard these things very sorrowful (he became; *N+kO) he was for rich extremely.
24 Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
Having seen then him Jesus sorrowful became saying; How difficult [for] those riches having [when] into the kingdom of God (they enter. *N+kO)
25 Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
Easier for it is a camel through (an eye of a needle *N+kO) to go than a rich man into the kingdom of God to enter.
26 Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
Said then those having heard; Then who is able to be saved?
27 Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
But He said; The [things] impossible with men possible with God are.
28 Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
Said then Peter; Behold we ourselves (having abandoned *N+kO) ([our] own [things] *N+kO) (and *k) followed You.
29 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
And He said to them; Amen I say to you that no [one] there is who has left house or wife or brothers or parents or children for the sake of the kingdom of God,
30 da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
who (certainly *N+kO) nothing (may receive back *NK+o) manifold more in time this — and in the age which is coming life eternal. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
Having taken aside then the Twelve He said to them; Behold we go up to (Jerusalem, *N+kO) and will be accomplished all things which written through the prophets about the Son of Man;
32 Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
He will be betrayed for to the Gentiles and will be mocked and will be insulted and will be spit upon,
33 za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
And having flogged [Him] they will kill Him, and on the day third He will rise again.
34 Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
And they themselves no [thing] of these things understood, and was declaration this hidden from them, and neither they were knowing the [things] being spoken.
35 Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
It came to pass then in the drawing near by Him to Jericho a blind [man] certain was sitting beside the road (begging. *N+kO)
36 Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
Having heard now a crowd passing along he was asking what (maybe *o) would be this.
37 Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
They told then to him that Jesus of Nazareth is passing by.
38 Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
And he called out saying; Jesus Son of David, do have mercy on me.
39 Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
And those going before were rebuking him that (he may be silent. *N+kO) He himself however much more was crying out; Son of David, do have mercy on me.
40 Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
Having stopped then Jesus commanded him to be brought to Him. When was approaching then he He asked him;
41 “Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
(saying *ko) What to you desire you I may do? And he said; Lord, that I may receive sight.
42 Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
And Jesus said to him; do receive sight: The faith of you has healed you.
43 Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.
And immediately he received sight and was following Him glorifying God. And all the people having seen [it] gave praise to God.

< Luka 18 >