< Luka 18 >

1 Yesu ya ba wa almajiransa wani misali, don yă koya musu yadda ya kamata su dinga yin addu’a kullum, ban da fasawa.
Каза им една притча за как трябва всякога да се молят, да не отслабват, думайки:
2 Ya ce, “A wani gari, an yi wani alƙali wanda ba ya tsoron Allah, bai kuma kula da mutane ba.
О Знаеш заповедите: "Не прелюбодействувай", "Не убивай"; "Не кради"; "Не лъжесвидетелствувай"; "Почитай баща си и майка си";
3 A garin nan kuma, akwai wata gwauruwa, wadda ta dinga zuwa wurin alƙalin nan, da roƙo cewa, ‘Ka yi mini adalci tsakanina da maƙiyina.’
В същия град имаше и една вдовица, която дохождаше при него и му казваше: Отдай ми правото спрямо противника ми.
4 “An daɗe yana ƙi, amma a ƙarshe ya ce cikin tunaninsa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane ba,
Но той за известно време не искаше. А после си каза: При все, че от Бога не се боя и човеците не зачитам,
5 amma don gwauruwan nan ta dame ni, zan tabbatar cewa ta sami adalci, domin kada tă gajiyar da ni, da yawan zuwanta.’”
пак, понеже тая вдовица ми досажда, ще - отдам правото, да не би да ме измори с безкрайното си дохождане.
6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan, marar gaskiya, ya ce.
И Господ рече: Слушайте що каза неправедният съдия!
7 Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke masa kuka, dare da rana adalci ba? Zai ci gaba da ƙin sauraronsu ne?
А Бог няма ли да отдаде правото на Своите избрани, които викат към Него ден и нощ, ако и да се бави спрямо тях?
8 Ina gaya muku, zai tabbatar sun sami adalci, ban da ɓatan lokaci. Amma sa’ad da Ɗan Mutum ya dawo, zai sami bangaskiya a duniya ke nan?”
Казвам ви, че ще им отдаде правото скоро. Обаче, когато дойде Човешкият Син ще намери ли вяра на земята?
9 Yesu ya kuma faɗi wannan misali ga waɗansu masu taƙama da adalcinsu, kuma suna rena sauran mutane ya ce,
И на някои, които уповаваха на себе си, че са праведни, и презираха другите, каза и тая притча:
10 “Waɗansu mutane biyu sun tafi haikali don yin addu’a. Ɗaya Bafarisiye ne, ɗayan kuma mai karɓar haraji.
Двама души влязоха в храма да се помолят, единият фарисей, а другият бирник.
11 Sai Bafarisiyen ya tashi tsaye, ya yi addu’a game da kansa yana cewa, ‘Allah, na gode maka, saboda ni ba kamar sauran mutane ba ne, wato, mafasa, masu aikata mugunta, masu zina, ko kuma kamar mai karɓar harajin nan.
Фарисеят, като се изправи, молеше се в себе си така: Боже, благодаря Ти, че не съм като другите човеци, грабители, неправедни, прелюбодейци и особено не като тоя бирник.
12 Ina azumi sau biyu a mako, ina ba da zakka daga kowane abin da na samu.’
Постя дваж в седмицата, давам десятък от всичко що придобия.
13 “Amma mai karɓar harajin ya tsaya daga nesa. Bai ma iya ɗaga kansa sama ba, sai ya buga ƙirjinsa, yana cewa, ‘Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi ne.’
А бирникът като стоеше издалеч, не щеше нито очите си да подигне към небето, но удряше се в гърди и казваше: Боже бъди милостив към мене грешника.
14 “Ina gaya muku, wannan mutum ne, ba ɗayan ba, ya koma gida baratacce, babu laifi a gaban Allah. Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
Казвам ви, че този слезе у дома си оправдан, а не онзи; защото всеки, който възвишава себе си, ще се смири, а който смирява себе си, ще се възвиси.
15 Mutane suna kawo jarirai wurin Yesu don yă taɓa su. Da almajiransa suka ga haka, sai suka kwaɓe su.
Донесоха още при Него младенците си, за да се докосне до тях; а учениците, като видяха, смъмриха ги.
16 Amma Yesu ya kira yaran a wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina. Kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
Но Исус ги повика и рече: Оставете дечицата да дойдат при Мене и не ги възпирайте; защото на такива е Божието царство.
17 Gaskiya nake gaya muku, duk wanda ba zai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
Истина ви казвам: Който не приеме като детенце Божието царство, той никак няма да влезе в него.
18 Wani mai mulki ya tambayi Yesu ya ce, “Malam managarci, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
И някой си началник Го попита, казвайки: Благи Учителю, какво да сторя, за да наследя вечен живот? (aiōnios g166)
19 Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake kira na managarci? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
А Исус му рече: Защо Ме наричаш благ? Никой не е благ, освен един Бог.
20 Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
Знаеш заповедите: "Не убивай"; "Не кради"; "Не лъжесвидетелствувай"; "Почитай баща си и майка си";
21 Mutumin ya ce, “Ai, tun ina ƙarami, na kiyaye duka waɗannan.”
а той каза: Всичко това съм опазил от младостта си.
22 Da Yesu ya ji haka, sai ya ce masa, “Akwai abu ɗaya har yanzu da ya rage maka. Ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, sa’an nan za ka sami dukiya a sama. Bayan haka, ka zo ka bi ni.”
Исус, като го чу, рече му: Едно още ти не достига. Продай все що имаш и раздай на сиромасите и ще имаш съкровище на небето; дойди и Ме следвай!
23 Da jin haka, sai ya ɓata rai, domin shi mai arziki ne sosai.
Но той, като чу това, наскърби се много, защото беше твърде богат.
24 Yesu ya kalle shi ya ce, “Yana da wuya fa, masu arziki su shiga mulkin Allah!
И Исус като го видя, каза: Колко мъчно ще влязат в Божието царство ония, които имат богатство!
25 Tabbatacce, zai fi sauƙi raƙumi ya shiga ta kafar allura, da mai arziki ya shiga mulkin Allah.”
Защото по-лесно е камила да мине през иглени уши, отколкото богат да влезе в Божието царство.
26 Waɗanda suka ji wannan suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai iya samun ceto?”
А ония, които чуха това рекоха: Тогава кой може да се спаси?
27 Yesu ya amsa ya ce, “Abin da ba ya yiwuwa ga mutane, mai yiwuwa ne ga Allah.”
А Той каза: Невъзможното за човеците за Бога е възможно.
28 Sai Bitrus ya ce, masa, “To, ga shi mun bar kome da muke da shi, don mu bi ka!”
А Петър рече: Ето, ние оставихме своето и Те последвахме.
29 Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, ba wanda ya bar gida, ko mata, ko’yan’uwa maza, ko iyaye, ko yara, saboda mulkin Allah,
А Той им рече: Истина ви казвам, няма никой, който да е оставил къща или жена, или братя, или родители, или чада, заради Божието царство,
30 da zai kāsa samun riɓi mai yawa, a wannan zamani, ya kuma sami rai madawwami a zamani mai zuwa.” (aiōn g165, aiōnios g166)
който да не получи многократно повече в сегашно време, а в идещия свят вечен живот. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Sai ya kai Sha Biyun gefe ɗaya, ya ce musu, “Za mu Urushalima, kuma dukan abin da annabawa suka rubuta a kan Ɗan Mutum zai cika.
И като взе дванадесетте при Себе Си, рече им: Ето, възлизаме в Ерусалим и ще се изпълни в Човешкия Син всичко, що е писано чрез пророците.
32 Za a ba da shi ga Al’ummai, za su yi masa ba’a, su zage shi, su tofa masa miyau,
Защото ще бъде предаден на езичниците, които ще Му се поругаят и безсрамно ще Го оскърбят, и ще Го заплюят,
33 za su yi masa bulala, su kuma kashe shi. A rana ta uku kuma zai tashi.”
и, когато Го бият, ще Го убият; и на третия ден ще възкръсне.
34 Almajiran ba su gane da ko ɗaya daga cikin wannan ba. An ɓoye musu ma’anarsa, kuma ba su gane da abin da yake magana a kai ba.
Но те не разбираха нищо от това; и тая дума беше скрита за тях, и не разбираха това, което се казваше.
35 Da Yesu ya yi kusa da Yeriko, akwai wani makaho da yake zaune a gefen hanya, yana bara.
А когато Той се приближаваше до Ерихон, един слепец седеше край пътя да проси.
36 Da ya ji taron suna wucewa, sai ya yi tambaya ko mene ne ke faruwa.
И като чу, че минава народ, попита какво е това.
37 Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne ke wucewa.”
И казаха му, че Исус назарянинът минава.
38 Sai ya yi kira ya ce, “Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
Тогава той извика, казвайки: Исусе, сине Давидов, смили се за мене!
39 Mutane da suke gaba suka kwaɓe shi, suka ce masa ya yi shiru. Amma sai ya ƙara ɗaga murya, yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
А тия, които вървяха отпред го смъмриха, за да млъкне; но той още повече викаше: Сине Давидов, смили се за мене!
40 Sai Yesu ya tsaya, ya ba da umarni a kawo mutumin wurinsa. Da ya zo kusa, Yesu ya tambaye shi ya ce,
И тъй, Исус се спря и заповяда да Му го доведат. И като се приближи, попита го:
41 “Me kake so in yi maka?” Sai ya amsa ya ce, “Ubangiji, ina so in sami ganin gari.”
Какво искаш да ти сторя? А той каза: Господи, да прогледам,
42 Yesu ya ce masa, “Ka sami ganin garinka; bangaskiyarka ta warkar da kai.”
Исус му рече: Прогледай; твоята вяра те изцели.
43 Nan da nan, ya sami ganin garinsa, kuma ya bi Yesu, yana yabon Allah. Da dukan mutane suka ga wannan, sai su ma suka yabi Allah.
И той веднага прогледа, и тръгна след Него, като славеше Бога. И всичките люде, като видяха това, въздадоха хвала на Бога.

< Luka 18 >