< Luka 17 >

1 Yesu ya ce wa almajiransa, “Dole ne a sami abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi, amma kaiton mutumin nan wanda suke zuwa ta wurinsa.
And he said to his disciples, It is necessary for causes of trouble to come about, but unhappy is he by whom they come.
2 Gwamma a ɗaura dutsen niƙa a wuyansa, a jefa shi cikin teku, da ya sa ɗaya daga cikin ƙananan yaran nan ya yi zunubi.
It would be well for him if a great stone was put round his neck and he was dropped into the sea, before he made trouble for any of these little ones.
3 Saboda haka, ku lura da kanku. “In ɗan’uwanka ya yi zunubi, ka kwaɓe shi. In ya tuba, ka gafarta masa.
Give attention to yourselves: if your brother does wrong, say a sharp word to him; and if he has sorrow for his sin, let him have forgiveness.
4 In ya yi maka laifi sau bakwai a rana ɗaya, ya kuma dawo sau bakwai ɗin a wurinka, yana cewa, ‘Na tuba,’ sai ka gafarta masa.”
And if he does you wrong seven times in a day, and seven times comes to you and says, I have regret for what I have done; let him have forgiveness.
5 Sai manzannin suka ce wa Ubangiji, “Ka ƙara mana bangaskiya!”
And the twelve said to the Lord, Make our faith greater.
6 Ya amsa musu ya ce, “In kuna da bangaskiya da take ƙanƙani kamar ƙwayar mustad, kuna iya ce wa wannan itacen durumi, ‘Ka tumɓuke daga nan, ka dasu a cikin teku.’ Zai kuwa yi muku biyayya.
And the Lord said, If your faith was only as great as a grain of mustard seed, you might say to this tree, Be rooted up and planted in the sea; and it would be done.
7 “In ɗaya a cikinku yana da bawa, wanda yake masa noma, ko kiwon tumaki, da dawowar bawan daga gonar, ai, ba zai ce masa, ‘Ka zo nan, ka zauna, ka ci abinci ba’?
But which of you, having a servant who is ploughing or keeping sheep, will say to him, when he comes in from the field, Come now and be seated and have a meal,
8 Ashe, ba zai ce masa, ‘Ka shirya mini abincin yamma, ka shirya ka yi mini hidima domin in ci in sha, bayan haka kana iya ci, ka kuma sha ba’?
Will he not say, Get a meal for me, and make yourself ready and see to my needs till I have had my food and drink; and after that you may have yours?
9 Shin, zai gode wa bawan don yă yi aikin da aka ce ya yi ne?
Does he give praise to the servant because he did what was ordered?
10 Haka ku ma, bayan kun yi duk abin da aka ce muku ku yi, ya kamata ku ce, ‘Mu bayi ne marasa cancanta, mun dai yi aikinmu ne kaɗai.’”
In the same way, when you have done all the things which are given you to do, say, There is no profit in us, for we have only done what we were ordered to do.
11 Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi takan iyakar Samariya da Galili.
And it came about that when they were on the way to Jerusalem he went through Samaria and Galilee.
12 Da zai shiga wani ƙauye, sai maza goma da suke da kuturta suka sadu da shi. Suka tsaya da nesa,
And when he went into a certain small town he came across ten men who were lepers, and they, keeping themselves at a distance,
13 suka yi kira da babbar murya, suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka ji tausayinmu!”
Said, in loud voices, Jesus, Master, have mercy on us.
14 Da ya gan su sai ya ce, “Ku je ku nuna kanku ga firistoci.” Suna kan hanyar tafiya sai suka tsabtacce.
And when he saw them he said, Go, and let the priests see you. And, while they were going, they were made clean.
15 Da ɗayansu ya ga ya warke, sai ya koma, yana yabon Allah da babbar murya.
And one of them, when he saw that he was clean, turning back, gave praise to God in a loud voice;
16 Ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, ya gode masa. Shi kuwa mutumin Samariya ne.
And, falling down on his face at the feet of Jesus, he gave the credit to him; and he was a man of Samaria.
17 Yesu ya yi tambaya ya ce, “Ba duka goma ne aka tsabtacce ba? Ina sauran taran?
And Jesus said, Were there not ten men who were made clean? where are the nine?
18 Ba wanda ya dawo don yă yabi Allah, sai dai wannan baƙon?”
Have not any of them come back to give glory to God, but only this one from a strange land?
19 Sai ya ce masa, “Tashi, ka yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
And he said to him, Get up, and go on your way; your faith has made you well.
20 Wata rana, Farisiyawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai zo, Yesu ya amsa ya ce, “Ai, mulkin Allah ba takan zo ta wurin yin kallon ku ba.
And when the Pharisees put questions to him about when the kingdom of God would come, he gave them an answer and said, The kingdom of God will not come through observation:
21 Mutane kuma ba za su ce, ‘Ga shi nan,’ ko kuma, ‘Ga shi can’ ba, domin mulkin Allah yana cikinku ne.”
And men will not say, See, it is here! or, There! for the kingdom of God is among you.
22 Sai ya ce wa almajiransa, “Lokaci yana zuwa da za ku yi marmarin ganin rana ɗaya cikin ranakun Ɗan Mutum, amma ba za ku gani ba.
And he said to his disciples, The time will come when you will have a great desire to see one of the days of the Son of man, but you will not see it.
23 Mutane za su ce muku, ‘Ga shi can!’ Ko kuma, ‘Ga shi nan!’ Kada ku yi hanzarin binsu.
And if they say to you, See, it is there! or, It is here! do not go away, or go after them.
24 Gama Ɗan Mutum, a cikin ranarsa, zai zama kamar walƙiya da take walƙawa, da take kuma haskaka sararin sama, daga wannan kusurwa zuwa wancan kusurwa.
For as in a thunderstorm the bright light is seen from one end of the sky to the other, so will the Son of man be when his time comes.
25 Amma da fari, dole yă sha wahaloli masu yawa, kuma mutanen zamanin nan su ƙi shi.
But first, he will have to undergo much and be put on one side by this generation.
26 “Daidai kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a zamanin Ɗan Mutum.
And as it was in the days of Noah, so will it be in the day of the Son of man.
27 Mutane suna ci, suna sha, suna aurayya, ana kuma ba da su ga aure, har ranar da Nuhu ya shiga jirgin. Sa’an nan ambaliyar ruwan ya sauka, ya hallaka su duka.
They were feasting and taking wives and getting married, till the day of the overflowing of the waters, when Noah went into the ark, and they all came to destruction.
28 “Haka ma aka yi a zamanin Lot. Mutane suna ci, suna sha, suna saya, suna sayarwa, suna shuki, suna kuma gine-gine.
In the same way, in the days of Lot; they were feasting and trading, they were planting and building;
29 Amma a ranar da Lot ya bar Sodom, sai aka yi ruwan wuta da farar wuta daga sama, aka hallaka su duka.
But on the day when Lot went out of Sodom, fire came down from heaven and destruction came on them all.
30 “Daidai haka zai zama, a ranar da Ɗan Mutum zai bayyana.
So will it be in the day of the revelation of the Son of man.
31 A ranan nan, kada wanda yake kan rufin gidansa ya sauka don yă kwashe dukiyarsa da take cikin gidan. Haka ma duk wanda yake gona, kada yă koma don wani abu.
On that day, if anyone is on the roof of the house, and his goods are in the house, let him not go down to take them away; and let him who is in the field not go back to his house.
32 Ku tuna fa da matar Lot!
Keep in mind Lot's wife.
33 Duk wanda yake so ya ceci ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai cece shi.
If anyone makes an attempt to keep his life, it will be taken from him, but if anyone gives up his life, he will keep it.
34 Ina gaya muku, a daren nan, mutane biyu za su kasance a gado ɗaya, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.
I say to you, In that night there will be two men sleeping in one bed, and one will be taken away and the other let go.
35 Mata biyu za su kasance suna niƙan hatsi tare, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.”
Two women will be crushing grain together; one will be taken away and the other let go.
37 Suka tambaya, suka ce, “A ina ne, ya Ubangiji?” Ya ce musu, “Ai, inda gawa take, nan ne ungulai za su taru.”
And they, answering him, said, Where, Lord? And he said to them, Where the body is, there will the eagles come together.

< Luka 17 >