< Luka 16 >

1 Yesu ya ce wa almajiransa, “An yi wani mai arziki wanda aka yi wa manajansa zargin yin banza da dukiyarsa.
Jesu naye cha wamba valutwana vakwe, “Kuvena mukwame wa muhumi avena muyendisi wa misevezi yakwe, mi kuva vihiwa kuti muyendisi wa misevezi ya kwe u kwete ku mu sinyeza iluwo lya kwe.
2 Sai ya kira manajan, ya tambaye shi, ‘Me nake ji haka a kanka? Ka kawo lissafin aikinka, domin ba za ka iya cin gaba da aikinka ba.’
Cwale muhumi cha musupa mi chati kwali, 'Zintu nzi zi nizule kuamana niwe? U nihe chakwizula za musevezi wako, ili kuti kese uzwile havusu ni vuyendisi.'
3 “Sai manajan ya ce cikin tunaninsa, ‘Maigidana zai kore ni daga aiki, me zan yi? Ba ni da ƙarfin noma, kuma ina jin kunyan yin bara.
Muyendisi cha liwambila, 'chiniswanela kupanga chinzi, hakuva mukulwana choni zwisa musevezi? Ka nina ziho za kusha, mi niswava ku mukumbila.
4 Na san abin da zan yi, don mutane su karɓe ni a gidajensu, bayan an kore ni daga aiki a nan.’
Nizi chini swanela ku tenda, ili kuti china zwiswa ha musevezi wangu wa vu yendisi, bantu va ni tambule mu mazuvo avo.
5 “Sai ya kira kowane ɗaya da maigidansa yake bin bashi. Ya tambayi na farkon ya ce, ‘Nawa ne maigidana yake bin ka?’
Cwale muyendisi chasupa zumwi ni zumwi ya vaali kukolota si mwin'a kwe, mi cha vuza we ntazi, 'U kolota vukayi simwin'a ngu? 6.
6 “Ya amsa ya ce, ‘Garwar mai na zaitun guda ɗari tara.’ “Manajan ya ce, ‘Ga takardarka, ka zauna maza ka mai da shi ɗari huɗu.’
Cha wamba, 'Ni kolota makumi ekumi ya byima bya mafuta e oli.' Mi chati kwali, muhinde zikoloti zenu, mwikale kapili, mi muñole makumi akwana yanza.'
7 “Ya kuma tambayi na biyun, ‘Kai fa, nawa ne ake bin ka?’ “Sai ya amsa ya ce, ‘Buhunan alkama dubu.’ “Ya ce, ‘Ga takardarka, ka mai da shi ɗari takwas.’
Cwale muyendisi cha wamba ku zumwi, 'mi vukayi yo kolota?' Chati, 'makumi ekumi a vuyima bwa vuroto.' Chati kwali, 'hinde chikoloti mi u ñole makumi akwana yenza ni to tatwe.
8 “Maigidan kuwa ya yabi manajan nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama’yan duniyan nan suna da wayon yin hulɗa da junansu fiye da’yan haske. (aiōn g165)
Simwin'a kwe cha lumba chikombwa chi sa sepahali kakuti ava sevezi mu kusasepahala. Vaana ve fasi ilyi vena ahulu mukusa sepahala chiva kwete kuseveza ni vantu vavo hita vaana vena mu liseli. (aiōn g165)
9 Ina gaya muku, ku yi amfani da dukiya na wannan duniya, domin ku sami wa kanku abokai. Saboda bayan dukiyar ta ƙare, za a karɓe ku a wuraren zama da sun dawwama. (aiōnios g166)
Ni wamba kwenu, mutende valikani che nzila za mashenyi a sa sepahali, kutendela kuti chi bwamana, va woole ku mitambula mu mazuvo asamani. (aiōnios g166)
10 “Duk wanda ana amincewa da shi cikin ƙaramin abu, ana kuma amincewa da shi cikin babba. Kuma duk marar gaskiya cikin ƙaramin abu, zai zama marar gaskiya cikin babba.
Iye yo sepahala ku zinini mwa sepahale ni ku zikando, mi niya sasepahali mu zinini kasepahali mu zikando.
11 In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiya ta wannan duniya ba, wa zai amince muku da dukiya ta gaskiya?
Haiva kena u va sepahali ku ku sevelisa mashelenyi a fosahele, nje ni yeta kusepe mu chifumu che niti?
12 In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiyar wani ba, wa zai ba ku dukiya naku, na kanku?
Mi haiva kawini ku sepahala mu kusevelisa mashelinyi a vamwi, njeni ya sa kuhe mashelenyi ako u mwine?
13 “Babu wani bawa mai iya bauta wa iyayengiji biyu ba. Ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗayan, ko kuwa ya dāge ga yi wa ɗaya bauta, sa’an nan ya rena ɗayan. Ba za ku iya ku bauta wa Allah tare da bauta wa Mammon (wato, Kuɗi) a lokaci ɗaya ba.”
Ka kwina muhikana yo wola ku seveleza malena vo vele, kusicwalo mwa toye umwi ni kusaka zumwi, mwa kumalele umwi kapa kunyefula zumwi. Ko woli kuseveleza Ereeza ni chifumu.
14 Da Farisiyawa masu son kuɗi suka ji wannan duka, sai suka yi wa Yesu tsaki.
Hanu Vafalisi, va vali kusaka hahulu mashelenyi, va va zuwi zoose inzi, mi chi va museka.
15 Ya ce musu, “Ku ne masu mai da kanku marasa laifi a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abu mai daraja a gaban mutane, abin ƙyama ne a gaban Allah.
Mi chati kuvali, “Mu li shiyamisa mu menso a vantu, kono Ireeza wizi ikulo zenu. Zina zivoneka vulotu mumeeso a vantu kwe Reeza zi fosahele.
16 “An yi shelar Doka da Annabawa har zuwa lokacin Yohanna. Tun daga lokacin nan, bisharar mulkin Allah ne ake wa’azinta, kowa kuma yana ƙoƙarin kutsa kai ya shiga.
Mulao ni vupolofita ziva kuseveza kuleta Johani hasika. Ku zwa iyo nako, inzwii lya muvuso we Reeza li va kutazwa, mi zumwi ni zumwi ava sa kuhambiliza inzila za vo mwateni.
17 Gama ta fi sauƙi sama da ƙasa su shuɗe, da a ce ɗigo guda ɗaya na rubutun, ya fita ya fāɗi daga cikin Doka.
Kono kuhuva kwiwulu ni hansi zi mane isi kuti intaku imwi ya mulao sanzi ivi ni mutendo.
18 “Duk wanda ya saki matarsa ya auri wata mace, zina ne yake yi. Kuma mutumin da ya auri macen da aka sake, zina ne yake yi.
Yense yo kauhana ni mwanakazi wakwe ni kusesa zumwi u chita vushahi, mi yo sesa mwanakazi ya va kanwa kwa mwihyabwe naye utenda vushahi.
19 “An yi wani mutum mai arziki wanda yakan sa tufafi masu ruwan shunayya, da kuma na lallausan lilin, yana kuma cikin rayuwar jin daɗi kullum.
Linu ku vena mukwame ya va humite, ya va kuzwete zi zwato ze pulipera ni line mi mazuva onse ava kulikola chifumu cha kwe.
20 A ƙofar gidansa kuma akan ajiye wani mai bara, mai suna Lazarus, wanda jikinsa duk gyambuna ne.
Mukumbizi ava kusumpwa Lazaro ava lele hamulyango, avali kwizwile zilavi muvili wonse.
21 Shi kuwa yakan yi marmarin cin abin da yakan fāɗi daga tebur na mai arzikin nan. Har karnuka ma sukan zo su lashe gyambunansa.
Mi avali kuhala kulya vungululwa vu vali kuwa hentafule ya muhumi, mi kuzwaho, vambwa va vali kukomba zilavi zakwe.
22 “Ana nan, sai mai baran ya mutu, kuma mala’iku suka ɗauke shi zuwa gefen Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi.
Ku vezi kuva kuti mukumbizi chafwa, mi avezi ku hindwa mangeloi ku mutwala kwimbali ya Abrahama. Muhumi naye chafwa mi cha zikwa,
23 A cikin jahannama ta wuta, inda yana shan azaba, ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim can nesa, da kuma Lazarus a gefensa. (Hadēs g86)
mi mu lyangalilo, na sukulukite, cha kotola menso mi cha vona Abrahama nena vutavule ni Lazaro nena ha chizuva chakwe. (Hadēs g86)
24 Sai ya yi masa kira ya ce, ‘Baba, Ibrahim, ka ji tausayina, ka aiki Lazarus ya sa ɗan yatsarsa a ruwa, ya ɗiga mini a harshe saboda in ji sanyi, domin ina shan azaba cikin wannan wuta.’
Cha lila mi chati, Tayo Abrahama, uni zuwile kusasama, mi tumine Lazaro, kuti a tompe munwe wakwe mu menzi mi nja tontoze lulimi lwangu, kakuti ni hile maswe mowu mulilo.
25 “Amma Ibrahim ya ce, ‘Ka tuna fa ɗana, a lokacin da kake duniya, ka sami abubuwa masu kyau naka, Lazarus kuwa ya sami munanan abubuwa. Amma yanzu ya sami ta’aziyya a nan, kai kuwa kana shan azaba.
Kono Abrahama chati, 'mwan'a ngu, u hupule kuti muvuhalo bwako uva tambuli zako zilotu, mi Lazaro mwinzila iswana ava ku tavela zintu zivilala, kono hanu cho kwete kusengwa sengwa kunu, mi iwe wina mumanyando.
26 Ban da wannan duka ma, tsakaninmu da kai, akwai wani babban rami da aka yi, yadda waɗanda suke son ƙetarewa daga nan zuwa wurinku, ba za su iya ba, kuma ba mai iya ƙetarewa daga wurinku zuwa wurinmu.’
Mi kuzwaho zintu zoose, chigodi chikando chivavi mukati, ili kuti avo vasaka kuluta kuzwa kunu kwiza kwako kese vawole, mi kakwina yese awole kuzwa uko kwiza kwetu.'
27 “Ya amsa ya ce, ‘To, ina roƙonka, ya uba, ka aiki Lazarus zuwa gidan mahaifina,
Muhumi chati, ni ku kumbila, Tayo Abrahama, kuti umuni tumine kuzuvo ya tayo
28 gama ina da’yan’uwana biyar maza. Bari yă ba su gargaɗi, don kada su ma su zo wurin nan mai azaba.’
kakuti nina vanche vava swisu va tenda yanza - kutendela kuti akava kalimele, kutiya kuti navo chiveza mwe chi chivaka cha masukuluka.'
29 “Ibrahim ya amsa ya ce, ‘Suna da Musa da Annabawa, ai, sai su saurare su.’
Kono Abrahama chati, veena Mushe ni vapolofita; mu vasiye va tekeleze ku vali.'
30 “Sai ya ce, ‘A’a, ya uba, Ibrahim, in dai wani ya tashi daga matattu ya je wurinsu, za su tuba.’
Muhumi che tava chati, 'Nanta, Tayo Abrahama, kono haiva zumwi na yenda kuvali kuvafwile, mu va lichiule.'
31 “Amma ya ce masa, ‘In ba su saurari Musa da Annabawa ba, kai, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su saurare shi ba.’”
Kono Abrahama chati kwali, 'Haiba ni vasa tekelezi kwa Mushe ni vapolofita, kese vaole kuzumina ni haiva vafwile kuti va vuke.'”

< Luka 16 >