< Luka 16 >

1 Yesu ya ce wa almajiransa, “An yi wani mai arziki wanda aka yi wa manajansa zargin yin banza da dukiyarsa.
And he spoke a parable to his disciples. There was a certain rich man, who had a steward; and accusations were brought to him of him, that he squandered his property.
2 Sai ya kira manajan, ya tambaye shi, ‘Me nake ji haka a kanka? Ka kawo lissafin aikinka, domin ba za ka iya cin gaba da aikinka ba.’
And his lord called him, and said to him: What is this that I hear of thee? Render to me an account of thy stewardship; for thou canst no longer be my steward.
3 “Sai manajan ya ce cikin tunaninsa, ‘Maigidana zai kore ni daga aiki, me zan yi? Ba ni da ƙarfin noma, kuma ina jin kunyan yin bara.
And the steward said with himself: What shall I do, since my lord is about to take from me the stewardship? To dig, I am unable; and to become a beggar, I am ashamed.
4 Na san abin da zan yi, don mutane su karɓe ni a gidajensu, bayan an kore ni daga aiki a nan.’
I know what to do, that, when I am put out of the stewardship, they may receive me to their houses.
5 “Sai ya kira kowane ɗaya da maigidansa yake bin bashi. Ya tambayi na farkon ya ce, ‘Nawa ne maigidana yake bin ka?’
And he called each one of his lord's debtors; and he said to the first, How much owest thou to my lord?
6 “Ya amsa ya ce, ‘Garwar mai na zaitun guda ɗari tara.’ “Manajan ya ce, ‘Ga takardarka, ka zauna maza ka mai da shi ɗari huɗu.’
And he said to him, One hundred measures of oil. And he said to him: Take thy bill, and sit down quickly, and write Fifty measures.
7 “Ya kuma tambayi na biyun, ‘Kai fa, nawa ne ake bin ka?’ “Sai ya amsa ya ce, ‘Buhunan alkama dubu.’ “Ya ce, ‘Ga takardarka, ka mai da shi ɗari takwas.’
And he said to another: And how much owest thou to my lord? And he said to him, One hundred cors of wheat. And he said to him: Take thy bill, and sit down, and write Eighty cors.
8 “Maigidan kuwa ya yabi manajan nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama’yan duniyan nan suna da wayon yin hulɗa da junansu fiye da’yan haske. (aiōn g165)
And our Lord praised the unrighteous steward, for having acted sagaciously: for the children of this world are more sagacious than the children of light, in this their generation. (aiōn g165)
9 Ina gaya muku, ku yi amfani da dukiya na wannan duniya, domin ku sami wa kanku abokai. Saboda bayan dukiyar ta ƙare, za a karɓe ku a wuraren zama da sun dawwama. (aiōnios g166)
And I also say to you: Make to yourselves friends, with this unrighteous mammon; so that when it is finished, they may receive you to their everlasting tabernacles. (aiōnios g166)
10 “Duk wanda ana amincewa da shi cikin ƙaramin abu, ana kuma amincewa da shi cikin babba. Kuma duk marar gaskiya cikin ƙaramin abu, zai zama marar gaskiya cikin babba.
He that is faithful in the little, is also faithful in the much; and he that is unjust in the little, is also unjust in the much.
11 In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiya ta wannan duniya ba, wa zai amince muku da dukiya ta gaskiya?
If therefore ye have not been faithful in the unrighteous mammon, who will intrust to you the reality?
12 In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiyar wani ba, wa zai ba ku dukiya naku, na kanku?
And if ye have not been found faithful in that which is not yours, who will give to you that which is yours?
13 “Babu wani bawa mai iya bauta wa iyayengiji biyu ba. Ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗayan, ko kuwa ya dāge ga yi wa ɗaya bauta, sa’an nan ya rena ɗayan. Ba za ku iya ku bauta wa Allah tare da bauta wa Mammon (wato, Kuɗi) a lokaci ɗaya ba.”
There is no servant, who can serve two lords. For, either he will hate the one and love the other, or he will honor the one and despise the other. Ye cannot serve God and mammon.
14 Da Farisiyawa masu son kuɗi suka ji wannan duka, sai suka yi wa Yesu tsaki.
And the Pharisees, when they heard all these things, because they loved money, derided him.
15 Ya ce musu, “Ku ne masu mai da kanku marasa laifi a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abu mai daraja a gaban mutane, abin ƙyama ne a gaban Allah.
And Jesus said to them: Ye are such as justify yourselves before men; but God knoweth your heart: for that which is exalted among men, is abominable before God.
16 “An yi shelar Doka da Annabawa har zuwa lokacin Yohanna. Tun daga lokacin nan, bisharar mulkin Allah ne ake wa’azinta, kowa kuma yana ƙoƙarin kutsa kai ya shiga.
The law and the prophets were until John: since then, the kingdom of God is proclaimed, and every one presseth it to enter in.
17 Gama ta fi sauƙi sama da ƙasa su shuɗe, da a ce ɗigo guda ɗaya na rubutun, ya fita ya fāɗi daga cikin Doka.
And it is easier for heaven and earth to pass away, than for one letter to pass from the law.
18 “Duk wanda ya saki matarsa ya auri wata mace, zina ne yake yi. Kuma mutumin da ya auri macen da aka sake, zina ne yake yi.
Whoever putteth away his wife, and taketh another, committeth adultery; and whoever taketh her that is put away, committeth adultery.
19 “An yi wani mutum mai arziki wanda yakan sa tufafi masu ruwan shunayya, da kuma na lallausan lilin, yana kuma cikin rayuwar jin daɗi kullum.
And there was a certain rich man, who was clothed in fine linen and scarlet, and passed every day in splendid luxury.
20 A ƙofar gidansa kuma akan ajiye wani mai bara, mai suna Lazarus, wanda jikinsa duk gyambuna ne.
And there was a certain poor man, whose name was Lazarus; and he was laid at the gate of the rich man, smitten with ulcers.
21 Shi kuwa yakan yi marmarin cin abin da yakan fāɗi daga tebur na mai arzikin nan. Har karnuka ma sukan zo su lashe gyambunansa.
And he desired to fill his belly with the fragments that fell from the rich man's table: and the dogs also came and licked his ulcers.
22 “Ana nan, sai mai baran ya mutu, kuma mala’iku suka ɗauke shi zuwa gefen Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi.
And so it was, that the poor man died; and angels transported him to Abraham's bosom. The rich man also died, and was buried.
23 A cikin jahannama ta wuta, inda yana shan azaba, ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim can nesa, da kuma Lazarus a gefensa. (Hadēs g86)
And being tormented in hell, he raised his eyes from afar off, and saw Abraham, and Lazarus in his bosom. (Hadēs g86)
24 Sai ya yi masa kira ya ce, ‘Baba, Ibrahim, ka ji tausayina, ka aiki Lazarus ya sa ɗan yatsarsa a ruwa, ya ɗiga mini a harshe saboda in ji sanyi, domin ina shan azaba cikin wannan wuta.’
And he called with a loud voice, and said: Abraham, my father, have pity on me; and send Lazarus, that he may dip the tip of his finger in water, and moisten my tongue; for, lo, I am tormented in this flame.
25 “Amma Ibrahim ya ce, ‘Ka tuna fa ɗana, a lokacin da kake duniya, ka sami abubuwa masu kyau naka, Lazarus kuwa ya sami munanan abubuwa. Amma yanzu ya sami ta’aziyya a nan, kai kuwa kana shan azaba.
And Abraham said to him: My son, remember, that thou receivedst thy good things in thy lifetime, and Lazarus his evil things: and now, behold he is here at rest, and thou art tormented.
26 Ban da wannan duka ma, tsakaninmu da kai, akwai wani babban rami da aka yi, yadda waɗanda suke son ƙetarewa daga nan zuwa wurinku, ba za su iya ba, kuma ba mai iya ƙetarewa daga wurinku zuwa wurinmu.’
And with all these, there is a great barrier between us and you; so that they who would pass from here to you, cannot; neither can they pass from there to us
27 “Ya amsa ya ce, ‘To, ina roƙonka, ya uba, ka aiki Lazarus zuwa gidan mahaifina,
He said to him: I pray thee, therefore, my father, that thou wouldst send him to my father's house;
28 gama ina da’yan’uwana biyar maza. Bari yă ba su gargaɗi, don kada su ma su zo wurin nan mai azaba.’
for I have five brothers; that he may go and protest to them; lest they also come to this place of torment.
29 “Ibrahim ya amsa ya ce, ‘Suna da Musa da Annabawa, ai, sai su saurare su.’
Abraham said to him: They have Moses and the prophets, let them hear them.
30 “Sai ya ce, ‘A’a, ya uba, Ibrahim, in dai wani ya tashi daga matattu ya je wurinsu, za su tuba.’
But he said to him: No, my father Abraham: but if one shall go to them from the dead, they will repent.
31 “Amma ya ce masa, ‘In ba su saurari Musa da Annabawa ba, kai, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su saurare shi ba.’”
Abraham said to him: If they hear not Moses and the prophets, they will not believe, though one should rise from the dead.

< Luka 16 >