< Luka 14 >

1 Wata ranar Asabbaci, da Yesu ya shiga gidan wani sanannen Bafarisiye don cin abinci, sai mutane suka zuba masa ido da kyau.
And it came to pass, on his going into the house of a certain one of the chiefs of the Pharisees, on a sabbath, to eat bread, that they were watching him,
2 A nan a gabansa kuwa akwai wani mutum mai ciwon kumburin ƙafa da hannu.
and lo, there was a certain dropsical man before him;
3 Sai Yesu ya tambayi masanan dokoki da Farisiyawa ya ce, “Daidai ne bisa ga doka, a yi warkarwa a ranar Asabbaci, ko babu?”
and Jesus answering spake to the lawyers and Pharisees, saying, 'Is it lawful on the sabbath-day to heal?'
4 Amma ba su ce kome ba. Sai ya riƙe mutumin, ya warkar da shi, sa’an nan ya sallame shi.
and they were silent, and having taken hold of [him], he healed him, and let [him] go;
5 Sai ya tambaye, su ya ce, “In wani a cikinku yana da ɗa, ko bijimi da ya faɗa a rijiya a ranar Asabbaci, ba za ku cire shi nan da nan ba?”
and answering them he said, 'Of which of you shall an ass or ox fall into a pit, and he will not immediately draw it up on the sabbath-day?'
6 Suka rasa abin faɗi.
and they were not able to answer him again unto these things.
7 Da ya lura da yadda baƙi suna zaɓan wuraren zama masu bangirma a tebur, sai ya faɗa musu wannan misali, ya ce;
And he spake a simile unto those called, marking how they were choosing out the first couches, saying unto them,
8 “In wani ya gayyace ka bikin aure, kada ka zaɓi wurin zama mai bangirma, don wataƙila akwai wani da ya fi ka girma, da aka gayyata.
'When thou mayest be called by any one to marriage-feasts, thou mayest not recline on the first couch, lest a more honourable than thou may have been called by him,
9 In kuwa haka ne, wanda ya gayyace duk biyunku, zai zo ya ce maka, ‘Ka ba wa mutumin nan wurin zamanka.’ Ka ga, an ƙasƙantar da kai, kuma dole ka ɗauki wuri mafi ƙasƙanci.
and he who did call thee and him having come shall say to thee, Give to this one place, and then thou mayest begin with shame to occupy the last place.
10 Amma in an gayyace ka, ɗauki wuri mafi ƙasƙanci, don in wanda ya gayyace ka ya zo, zai ce maka, ‘Ka hawo nan aboki a wuri mafi girma.’ Wannan zai ɗaukaka ka a gaban dukan’yan’uwanka baƙi.
'But, when thou mayest be called, having gone on, recline in the last place, that when he who called thee may come, he may say to thee, Friend, come up higher; then thou shalt have glory before those reclining with thee;
11 Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Shi wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
because every one who is exalting himself shall be humbled, and he who is humbling himself shall be exalted.'
12 Sai Yesu ya ce wa wanda ya gayyace shi, “Lokacin da ka shirya biki ko liyafa, kada ka gayyaci abokanka, ko’yan’uwanka, ko danginka, ko kuma maƙwabtanka masu arziki, gama in ka yi haka, suna iya gayyatarka, su biya maka alherin da ka yi musu.
And he said also to him who did call him, 'When thou mayest make a dinner or a supper, be not calling thy friends, nor thy brethren, nor thy kindred, nor rich neighbours, lest they may also call thee again, and a recompense may come to thee;
13 Amma lokacin da ka kira biki, ka gayyaci matalauta, da guragu, da shanyayyu, da makafi.
but when thou mayest make a feast, be calling poor, maimed, lame, blind,
14 Ta haka, za ka sami albarka. Ko da yake ba za su iya biyan ka ba, za a biya ka a ranar tashin masu adalci daga matattu.”
and happy thou shalt be, because they have not to recompense thee, for it shall be recompensed to thee in the rising again of the righteous.'
15 Da jin haka, sai wani da yake tare da shi a tebur ɗin, ya ce wa Yesu, “Mai albarka ne wanda zai ci abinci a bikin nan a mulkin Allah.”
And one of those reclining with him, having heard these things, said to him, 'Happy [is] he who shall eat bread in the reign of God;'
16 Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum yana shirya wani babban biki, ya kuma gayyaci baƙi da yawa.
and he said to him, 'A certain man made a great supper, and called many,
17 Da lokacin bikin ya yi, sai ya aiki bawansa ya je ya ce wa waɗanda aka gayyata, ‘Ku zo, don an shirya kome.’
and he sent his servant at the hour of the supper to say to those having been called, Be coming, because now are all things ready.
18 “Amma sai dukansu suka fara ba da hujjoji. Na farkon ya ce, ‘Na sayi gona yanzun nan, dole in je in ga yadda take, ina roƙonka ka yi mini haƙuri.’
'And they began with one consent all to excuse themselves: The first said to him, A field I bought, and I have need to go forth and see it; I beg of thee, have me excused.
19 “Wani ya ce, ‘Na sayi shanun noma guda goma yanzun nan, ina kan hanyata ke nan in gwada su, ina roƙonka, ka yi mini haƙuri.’
'And another said, Five yoke of oxen I bought, and I go on to prove them; I beg of thee, have me excused:
20 “Har yanzu wani ya ce, ‘Na yi aure yanzun nan, don haka ni ba zan iya zuwa ba.’
and another said, A wife I married, and because of this I am not able to come.
21 “Bawansa ya dawo ya gaya wa maigidansa wannan. Sai maigidan ya yi fushi, ya ba da umarni ga bawansa ya ce, ‘Ka fita da sauri, ka bi titi-titi da lungu-lungu na garin, ka kawo matalauta, da guragu, da makafi, da shanyayyu.’
'And that servant having come, told to his lord these things, then the master of the house, having been angry, said to his servant, Go forth quickly to the broad places and lanes of the city, and the poor, and maimed, and lame, and blind, bring in hither.
22 “Bawan ya dawo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, an yi abin da ka umarta, amma har yanzu da sauran wuri.’
'And the servant said, Sir, it hath been done as thou didst command, and still there is room.
23 “Maigidan ya ce wa bawansa, ‘Ka je kan hanyoyin da layi-layi na karkara, ka sa su shigo, don gidana ya cika.’
'And the lord said unto the servant, Go forth to the ways and hedges, and constrain to come in, that my house may be filled;
24 Ina gaya muku, babu ko ɗaya daga cikin mutanen nan da aka gayyata da zai ɗanɗana bikina.”
for I say to you, that none of those men who have been called shall taste of my supper.'
25 Taron mutane mai yawa suna tafiya tare da Yesu, sai ya juya ya ce musu,
And there were going on with him great multitudes, and having turned, he said unto them,
26 “Duk wanda yakan zo wurina, amma bai ƙi mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa da’ya’yansa, da’yan’uwansa mata da maza, kai, har ma ransa ba, ba zai iya zama almajirina ba.
'If any one doth come unto me, and doth not hate his own father, and mother, and wife, and children, and brothers, and sisters, and yet even his own life, he is not able to be my disciple;
27 Kuma duk wanda ba yakan ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
and whoever doth not bear his cross, and come after me, is not able to be my disciple.
28 “In wani daga cikinku yana so ya gina gidan sama, ai, yakan fara zama ne, ya yi lissafin abin da ginin zai ci tukuna, don yă ga ko yana da isashen kuɗi da zai gama ginin.
'For who of you, willing to build a tower, doth not first, having sat down, count the expence, whether he have the things for completing?
29 Gama in ya sa tushen gini, amma bai iya gamawa ba, duk wanda ya gani zai yi masa ba’a,
lest that he having laid a foundation, and not being able to finish, all who are beholding may begin to mock him,
30 yana cewa, ‘Wannan mutum ya fara gini, amma bai iya gamawa ba.’
saying — This man began to build, and was not able to finish.
31 “Ko kuma, wane sarki ne, in zai je yaƙi da wani sarki, ai, yakan fara zama ne, ya duba ya ga, ko da mutane dubu goma, shi zai iya ƙarawa da mai zuwa da dubu ashirin?
'Or what king going on to engage with another king in war, doth not, having sat down, first consult if he be able with ten thousand to meet him who with twenty thousand is coming against him?
32 In ba zai iya ba, to, tun suna nesa, zai aika da wakilai, su je neman sharuɗan salama.
and if not so — he being yet a long way off — having sent an embassy, he doth ask the things for peace.
33 Haka nan fa, kowane ne a cikinku, da ba ya rabu da abin da yake da shi ba, ba zai iya zama almajirina ba.
'So, then, every one of you who doth not take leave of all that he himself hath, is not able to be my disciple.
34 “Gishiri fa yana da kyau, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa?
'The salt [is] good, but if the salt doth become tasteless, with what shall it be seasoned?
35 Ba shi da wani amfani, ko ga ƙasa, ko ga juji, sai dai a zubar da shi. “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
neither for land nor for manure is it fit — they cast it without. He who is having ears to hear — let him hear.'

< Luka 14 >