< Luka 14 >

1 Wata ranar Asabbaci, da Yesu ya shiga gidan wani sanannen Bafarisiye don cin abinci, sai mutane suka zuba masa ido da kyau.
Then it happened, when He entered the house of one of the rulers of the Pharisees to eat bread on the Sabbath, that they were watching Him closely.
2 A nan a gabansa kuwa akwai wani mutum mai ciwon kumburin ƙafa da hannu.
And then, there in front of Him was a man who had dropsy!
3 Sai Yesu ya tambayi masanan dokoki da Farisiyawa ya ce, “Daidai ne bisa ga doka, a yi warkarwa a ranar Asabbaci, ko babu?”
And Jesus reacted by saying to the lawyers and Pharisees, “Is it lawful to heal on the Sabbath?”
4 Amma ba su ce kome ba. Sai ya riƙe mutumin, ya warkar da shi, sa’an nan ya sallame shi.
But they kept silent. So He took hold of him, healed him, and let him go.
5 Sai ya tambaye, su ya ce, “In wani a cikinku yana da ɗa, ko bijimi da ya faɗa a rijiya a ranar Asabbaci, ba za ku cire shi nan da nan ba?”
Then He addressed them saying, “Which of you, if a son or an ox falls into a pit, will not immediately pull him out on the Sabbath day?”
6 Suka rasa abin faɗi.
And they could not answer Him regarding these things.
7 Da ya lura da yadda baƙi suna zaɓan wuraren zama masu bangirma a tebur, sai ya faɗa musu wannan misali, ya ce;
Then He told a parable to those who were invited, having observed how they kept trying for the best places, saying to them:
8 “In wani ya gayyace ka bikin aure, kada ka zaɓi wurin zama mai bangirma, don wataƙila akwai wani da ya fi ka girma, da aka gayyata.
“Whenever you are invited by someone to a wedding feast, do not recline in the place of honor, in case someone more honorable than you has been invited by him;
9 In kuwa haka ne, wanda ya gayyace duk biyunku, zai zo ya ce maka, ‘Ka ba wa mutumin nan wurin zamanka.’ Ka ga, an ƙasƙantar da kai, kuma dole ka ɗauki wuri mafi ƙasƙanci.
then he who invited you both will come and say, ‘You, give this man place!’ and then, with shame, you start to take the lowest place.
10 Amma in an gayyace ka, ɗauki wuri mafi ƙasƙanci, don in wanda ya gayyace ka ya zo, zai ce maka, ‘Ka hawo nan aboki a wuri mafi girma.’ Wannan zai ɗaukaka ka a gaban dukan’yan’uwanka baƙi.
Rather, whenever you are invited, go and recline in the lowest place, so that when your host comes, he may say to you, ‘Friend, move up higher.’ Then you will have honor in the presence of your fellow guests.
11 Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Shi wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
Because everyone who exalts himself will be humbled, and he who humbles himself will be exalted.”
12 Sai Yesu ya ce wa wanda ya gayyace shi, “Lokacin da ka shirya biki ko liyafa, kada ka gayyaci abokanka, ko’yan’uwanka, ko danginka, ko kuma maƙwabtanka masu arziki, gama in ka yi haka, suna iya gayyatarka, su biya maka alherin da ka yi musu.
Then He said directly to His host: “Whenever you give a dinner or a supper, do not invite your friends, nor your brothers, nor your relatives, nor rich neighbors, lest they also invite you back, and you be repaid.
13 Amma lokacin da ka kira biki, ka gayyaci matalauta, da guragu, da shanyayyu, da makafi.
But whenever you make a banquet, invite the poor, the crippled, the lame, the blind;
14 Ta haka, za ka sami albarka. Ko da yake ba za su iya biyan ka ba, za a biya ka a ranar tashin masu adalci daga matattu.”
and you will be blessed, because they cannot repay you—you will be repaid at the resurrection of the righteous.”
15 Da jin haka, sai wani da yake tare da shi a tebur ɗin, ya ce wa Yesu, “Mai albarka ne wanda zai ci abinci a bikin nan a mulkin Allah.”
Well when one of the fellow-recliners heard these things, he said to Him, “Blessed is he who will eat dinner in the Kingdom of God!”
16 Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum yana shirya wani babban biki, ya kuma gayyaci baƙi da yawa.
So He said to him: “A certain man prepared a great banquet and invited many.
17 Da lokacin bikin ya yi, sai ya aiki bawansa ya je ya ce wa waɗanda aka gayyata, ‘Ku zo, don an shirya kome.’
And at meal time he sent his slave to say to those who were invited, ‘Come, because everything is now ready.’
18 “Amma sai dukansu suka fara ba da hujjoji. Na farkon ya ce, ‘Na sayi gona yanzun nan, dole in je in ga yadda take, ina roƙonka ka yi mini haƙuri.’
But they all alike began to make excuses. The first said to him: ‘I bought a field, and I need to go and see it. I ask you to have me excused.’
19 “Wani ya ce, ‘Na sayi shanun noma guda goma yanzun nan, ina kan hanyata ke nan in gwada su, ina roƙonka, ka yi mini haƙuri.’
Another said: ‘I bought five yoke of oxen, and I am going to test them. I ask you to have me excused.’
20 “Har yanzu wani ya ce, ‘Na yi aure yanzun nan, don haka ni ba zan iya zuwa ba.’
Yet another said, ‘I have married a wife, and so I cannot come.’
21 “Bawansa ya dawo ya gaya wa maigidansa wannan. Sai maigidan ya yi fushi, ya ba da umarni ga bawansa ya ce, ‘Ka fita da sauri, ka bi titi-titi da lungu-lungu na garin, ka kawo matalauta, da guragu, da makafi, da shanyayyu.’
So that slave came and reported these things to his master. Then the owner of the house became angry and said to his slave, ‘Go out quickly into the streets and lanes of the city, and bring in here the poor and crippled and blind and lame.’
22 “Bawan ya dawo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, an yi abin da ka umarta, amma har yanzu da sauran wuri.’
And the slave said, ‘Master, what you ordered has been done, and there is still room.’
23 “Maigidan ya ce wa bawansa, ‘Ka je kan hanyoyin da layi-layi na karkara, ka sa su shigo, don gidana ya cika.’
Then the master said to the slave: ‘Go out to the roads and hedges and make people come in, so that my house may be filled.
24 Ina gaya muku, babu ko ɗaya daga cikin mutanen nan da aka gayyata da zai ɗanɗana bikina.”
For I tell you that none of those men who were invited will get a taste of my banquet!’”
25 Taron mutane mai yawa suna tafiya tare da Yesu, sai ya juya ya ce musu,
Now large crowds were traveling with Him, and turning He said to them:
26 “Duk wanda yakan zo wurina, amma bai ƙi mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa da’ya’yansa, da’yan’uwansa mata da maza, kai, har ma ransa ba, ba zai iya zama almajirina ba.
“If anyone comes to me and does not hate his father and mother, wife and children, brothers and sisters, yes, and even his own life, he cannot be my disciple.
27 Kuma duk wanda ba yakan ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
And whoever does not carry his cross, and come after me, cannot be my disciple.
28 “In wani daga cikinku yana so ya gina gidan sama, ai, yakan fara zama ne, ya yi lissafin abin da ginin zai ci tukuna, don yă ga ko yana da isashen kuɗi da zai gama ginin.
“Further, which of you, intending to build a tower, does not sit down first and calculate the cost, whether he has enough to complete it?
29 Gama in ya sa tushen gini, amma bai iya gamawa ba, duk wanda ya gani zai yi masa ba’a,
This so he does not lay a foundation without being able to finish, and all who see it begin to ridicule him,
30 yana cewa, ‘Wannan mutum ya fara gini, amma bai iya gamawa ba.’
saying, ‘This man began to build and was not able to finish!’
31 “Ko kuma, wane sarki ne, in zai je yaƙi da wani sarki, ai, yakan fara zama ne, ya duba ya ga, ko da mutane dubu goma, shi zai iya ƙarawa da mai zuwa da dubu ashirin?
“Or what king, going to engage another king in battle, does not sit down first and consider whether he is able with ten thousand to meet the one coming against him with twenty thousand?
32 In ba zai iya ba, to, tun suna nesa, zai aika da wakilai, su je neman sharuɗan salama.
And if not, while the other is still far away he sends a delegation and asks for terms for peace.
33 Haka nan fa, kowane ne a cikinku, da ba ya rabu da abin da yake da shi ba, ba zai iya zama almajirina ba.
“So likewise, any of you who does not renounce all his own possessions cannot be my disciple.
34 “Gishiri fa yana da kyau, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa?
Salt is good; but should the salt become insipid, with what can it be seasoned?
35 Ba shi da wani amfani, ko ga ƙasa, ko ga juji, sai dai a zubar da shi. “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
It is fit for neither soil nor fertilizer; it is thrown out. He who has ears to hear, let him hear!”

< Luka 14 >