< Luka 14 >

1 Wata ranar Asabbaci, da Yesu ya shiga gidan wani sanannen Bafarisiye don cin abinci, sai mutane suka zuba masa ido da kyau.
And it came to pass, when Jesus went into the house of one of the chief of the Pharisees, on the sabbath day, to eat bread, that they watched him.
2 A nan a gabansa kuwa akwai wani mutum mai ciwon kumburin ƙafa da hannu.
And behold, there was a certain man before him that had the dropsy.
3 Sai Yesu ya tambayi masanan dokoki da Farisiyawa ya ce, “Daidai ne bisa ga doka, a yi warkarwa a ranar Asabbaci, ko babu?”
And Jesus answering, spoke to the lawyers and Pharisees, saying: Is it lawful to heal on the sabbath day?
4 Amma ba su ce kome ba. Sai ya riƙe mutumin, ya warkar da shi, sa’an nan ya sallame shi.
But they held their peace. But he taking him, healed him, and sent him away.
5 Sai ya tambaye, su ya ce, “In wani a cikinku yana da ɗa, ko bijimi da ya faɗa a rijiya a ranar Asabbaci, ba za ku cire shi nan da nan ba?”
And answering them, he said: Which of you shall have an ass or an ox fall into a pit, and will not immediately draw him out, on the sabbath day?
6 Suka rasa abin faɗi.
And they could not answer him to these things.
7 Da ya lura da yadda baƙi suna zaɓan wuraren zama masu bangirma a tebur, sai ya faɗa musu wannan misali, ya ce;
And he spoke a parable also to them that were invited, marking how they chose the first seats at the table, saying to them:
8 “In wani ya gayyace ka bikin aure, kada ka zaɓi wurin zama mai bangirma, don wataƙila akwai wani da ya fi ka girma, da aka gayyata.
When thou art invited to a wedding, sit not down in the first place, lest perhaps one more honourable than thou be invited by him:
9 In kuwa haka ne, wanda ya gayyace duk biyunku, zai zo ya ce maka, ‘Ka ba wa mutumin nan wurin zamanka.’ Ka ga, an ƙasƙantar da kai, kuma dole ka ɗauki wuri mafi ƙasƙanci.
And he that invited thee and him, come and say to thee, Give this man place: and then thou begin with shame to take the lowest place.
10 Amma in an gayyace ka, ɗauki wuri mafi ƙasƙanci, don in wanda ya gayyace ka ya zo, zai ce maka, ‘Ka hawo nan aboki a wuri mafi girma.’ Wannan zai ɗaukaka ka a gaban dukan’yan’uwanka baƙi.
But when thou art invited, go, sit down in the lowest place; that when he who invited thee, cometh, he may say to thee: Friend, go up higher. Then shalt thou have glory before them that sit at table with thee.
11 Gama duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Shi wanda kuma ya ƙasƙantar da kansa, za a ɗaukaka shi.”
Because every one that exalteth himself, shall be humbled; and he that humbleth himself, shall be exalted.
12 Sai Yesu ya ce wa wanda ya gayyace shi, “Lokacin da ka shirya biki ko liyafa, kada ka gayyaci abokanka, ko’yan’uwanka, ko danginka, ko kuma maƙwabtanka masu arziki, gama in ka yi haka, suna iya gayyatarka, su biya maka alherin da ka yi musu.
And he said to him also that had invited him: When thou makest a dinner or a supper, call not thy friends, nor thy brethren, nor thy kinsmen, nor thy neighbours who are rich; lest perhaps they also invite thee again, and a recompense be made to thee.
13 Amma lokacin da ka kira biki, ka gayyaci matalauta, da guragu, da shanyayyu, da makafi.
But when thou makest a feast, call the poor, the maimed, the lame, and the blind;
14 Ta haka, za ka sami albarka. Ko da yake ba za su iya biyan ka ba, za a biya ka a ranar tashin masu adalci daga matattu.”
And thou shalt be blessed, because they have not wherewith to make thee recompense: for recompense shall be made thee at the resurrection of the just.
15 Da jin haka, sai wani da yake tare da shi a tebur ɗin, ya ce wa Yesu, “Mai albarka ne wanda zai ci abinci a bikin nan a mulkin Allah.”
When one of them that sat at table with him, had heard these things, he said to him: Blessed is he that shall eat bread in the kingdom of God.
16 Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum yana shirya wani babban biki, ya kuma gayyaci baƙi da yawa.
But he said to him: A certain man made a great supper, and invited many.
17 Da lokacin bikin ya yi, sai ya aiki bawansa ya je ya ce wa waɗanda aka gayyata, ‘Ku zo, don an shirya kome.’
And he sent his servant at the hour of supper to say to them that were invited, that they should come, for now all things are ready.
18 “Amma sai dukansu suka fara ba da hujjoji. Na farkon ya ce, ‘Na sayi gona yanzun nan, dole in je in ga yadda take, ina roƙonka ka yi mini haƙuri.’
And they began all at once to make excuse. The first said to him: I have bought a farm, and I must needs go out and see it: I pray thee, hold me excused.
19 “Wani ya ce, ‘Na sayi shanun noma guda goma yanzun nan, ina kan hanyata ke nan in gwada su, ina roƙonka, ka yi mini haƙuri.’
And another said: I have bought five yoke of oxen, and I go to try them: I pray thee, hold me excused.
20 “Har yanzu wani ya ce, ‘Na yi aure yanzun nan, don haka ni ba zan iya zuwa ba.’
And another said: I have married a wife, and therefore I cannot come.
21 “Bawansa ya dawo ya gaya wa maigidansa wannan. Sai maigidan ya yi fushi, ya ba da umarni ga bawansa ya ce, ‘Ka fita da sauri, ka bi titi-titi da lungu-lungu na garin, ka kawo matalauta, da guragu, da makafi, da shanyayyu.’
And the servant returning, told these things to his lord. Then the master of the house, being angry, said to his servant: Go out quickly into the streets and lanes of the city, and bring in hither the poor, and the feeble, and the blind, and the lame.
22 “Bawan ya dawo ya ce, ‘Ranka yă daɗe, an yi abin da ka umarta, amma har yanzu da sauran wuri.’
And the servant said: Lord, it is done as thou hast commanded, and yet there is room.
23 “Maigidan ya ce wa bawansa, ‘Ka je kan hanyoyin da layi-layi na karkara, ka sa su shigo, don gidana ya cika.’
And the Lord said to the servant: Go out into the highways and hedges, and compel them to come in, that my house may be filled.
24 Ina gaya muku, babu ko ɗaya daga cikin mutanen nan da aka gayyata da zai ɗanɗana bikina.”
But I say unto you, that none of those men that were invited, shall taste of my supper.
25 Taron mutane mai yawa suna tafiya tare da Yesu, sai ya juya ya ce musu,
And there went great multitudes with him. And turning, he said to them:
26 “Duk wanda yakan zo wurina, amma bai ƙi mahaifinsa da mahaifiyarsa, da matarsa da’ya’yansa, da’yan’uwansa mata da maza, kai, har ma ransa ba, ba zai iya zama almajirina ba.
If any man come to me, and hate not his father, and mother, and wife, and children, and brethren, and sisters, yea and his own life also, he cannot be my disciple.
27 Kuma duk wanda ba yakan ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, ba zai iya zama almajirina ba.
And whosoever doth not carry his cross and come after me, cannot be my disciple.
28 “In wani daga cikinku yana so ya gina gidan sama, ai, yakan fara zama ne, ya yi lissafin abin da ginin zai ci tukuna, don yă ga ko yana da isashen kuɗi da zai gama ginin.
For which of you having a mind to build a tower, doth not first sit down, and reckon the charges that are necessary, whether he have wherewithal to finish it:
29 Gama in ya sa tushen gini, amma bai iya gamawa ba, duk wanda ya gani zai yi masa ba’a,
Lest, after he hath laid the foundation, and is not able to finish it, all that see it begin to mock him,
30 yana cewa, ‘Wannan mutum ya fara gini, amma bai iya gamawa ba.’
Saying: This man began to build, and was not able to finish.
31 “Ko kuma, wane sarki ne, in zai je yaƙi da wani sarki, ai, yakan fara zama ne, ya duba ya ga, ko da mutane dubu goma, shi zai iya ƙarawa da mai zuwa da dubu ashirin?
Or what king, about to go to make war against another king, doth not first sit down, and think whether he be able, with ten thousand, to meet him that, with twenty thousand, cometh against him?
32 In ba zai iya ba, to, tun suna nesa, zai aika da wakilai, su je neman sharuɗan salama.
Or else, whilst the other is yet afar off, sending an embassy, he desireth conditions of peace.
33 Haka nan fa, kowane ne a cikinku, da ba ya rabu da abin da yake da shi ba, ba zai iya zama almajirina ba.
So likewise every one of you that doth not renounce all that he possesseth, cannot be my disciple.
34 “Gishiri fa yana da kyau, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, ta yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa?
Salt is good. But if the salt shall lose its savour, wherewith shall it be seasoned?
35 Ba shi da wani amfani, ko ga ƙasa, ko ga juji, sai dai a zubar da shi. “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
It is neither profitable for the land nor for the dunghill, but shall be cast out. He that hath ears to hear, let him hear.

< Luka 14 >