< Luka 13 >

1 A yanzun fa, akwai waɗansu da suka kasance a lokacin can, suka ba Yesu labarin Galiliyawa da Bilatus ya gauraye jininsu tare da jinin hadayunsu.
På samma tid voro der någre tillstädes, som bådade honom om de Galileer, hvilkas blod Pilatus hade blandat med deras offer.
2 Yesu ya amsa ya ce, “Kuna tsammani waɗannan Galiliyawan sun fi dukan sauran Galiliyawa zunubi ne, shi ya sa suka sha irin wannan wahala?
Då svarade Jesus, och sade till dem: Menen I att desse Galileer voro syndare för alla Galileer, efter de sådant ledo?
3 Ina gaya muku, a’a! Amma in ba ku tuba ba, ku ma duka za ku hallaka.
Nej, säger jag eder; utan om I icke bättren eder, skolen I alle sammalunda förgås.
4 Ko kuwa kuna tsammani, sha takwas ɗin nan da suka mutu lokacin da hasumiya a Silowam ya fāɗi a kansu, sun fi dukan sauran mutanen Urushalima laifi ne?
Eller de aderton, som tornet i Siloa föll uppå, och drap dem, menen I att de brottslige voro för alla menniskor, som bo i Jerusalem?
5 Ina gaya muku, a’a! Amma in ba ku tuba ba, ku ma duka za ku hallaka.”
Nej, säger jag eder; utan om I icke bättren eder, skolen I alle sammalunda förgås.
6 Sai ya ba su wannan misali ya ce, “Wani mutum yana da itacen ɓaure, da aka shuka a gonar inabinsa. Da ya je cire’ya’yan itacen, sai ya tarar ba tă yi’ya’ya ba.
Sade han ock denna liknelsen: En man hade ett fikonaträ planteradt i sin vingård, och han kom och sökte frukt derpå, och fann ingen.
7 Sai ya ce wa mai lura da gonar inabin, ‘Yau shekara uku ke nan ina zuwa neman’ya’yan ɓaure daga itacen nan, amma ba na samun kome. Sare shi! Don me za a bar shi ya tare wuri.’
Då sade han till vingårdsmannen: Si, nu i tre år hafver jag kommit, och sökt frukt på detta fikonaträt, och finner ingen; hugg det bort; hvarefter skall det förhindra jordena?
8 “Mutumin ya amsa ya ce, ‘Ranka yă daɗe, ka bar shi, in yi masa banƙasa, in kuma zuba masa taki har na shekara ɗaya.
Han svarade, och sade till honom: Herre, låt stå det ännu i detta året, så länge jag grafver omkring det och göder det;
9 In kuwa ya ba da’ya’ya shekara mai zuwa, yana da kyau! In kuwa ba haka ba, sai ka sare shi.’”
Om det så kunde bära frukt; hvar ock icke, så hugg det sedan bort.
10 Wata ranar Asabbaci, Yesu yana koyarwa a wata majami’a,
Och han lärde om Sabbathen i en Synagogo.
11 a wurin kuwa, akwai wata mace wadda aljani ya gurgunta, har na shekaru goma sha takwas. Duk ta tanƙware, ba ta ma iya miƙewa ko kaɗan.
Och si, der var en qvinna, som hade haft krankhetenes anda i aderton år; och var krumpen, och förmådde icke upplyfta hufvudet.
12 Da Yesu ya gan ta, sai ya kirata gaba, ya ce mata, “Mace, an’yantar da ke daga rashin lafiyarki.”
När Jesus såg henne, kallade han henne till sig, och sade till henne: Qvinna, var fri af dine krankhet.
13 Sai ya ɗibiya hannuwansa a kanta, nan da nan sai ta miƙe, ta yabi Allah.
Och han lade händerna på henne: och straxt reste hon sig upp, och prisade Gud.
14 Amma mai mulkin majami’ar ya ji haushi da Yesu ya yi warkarwa a ranar Asabbaci. Sai ya ce wa mutanen, “Akwai ranaku shida da ya kamata a yi aiki. Saboda haka, ku zo a ranakun nan a warkar da ku, ba ranar Asabbaci ba.”
Då svarade öfversten för Synagogon, och var vred att Jesus helade på Sabbathen, och sade till folket: Sex dagar äro, der I mågen arbeta på; kommer på dem, och låter hela eder; icke på Sabbathen.
15 Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Ku munafukai! Ashe, kowannenku ba yakan kunce bijiminsa ko jakinsa, yă kai shi waje yă ba shi ruwa, a ranar Asabbaci ba?
Då svarade Herren honom, och sade: Du skrymtare, löser icke hvar och en af eder om Sabbathen sin oxa eller åsna ifrå krubbone, och leder bort att vattna?
16 Ashe, bai kamata a’yantar da macen nan, diyar zuriyar Ibrahim, wadda Shaiɗan ya daure, har shekara goma sha takwas, a ranar Asabbaci, daga abin da ya daure ta ba?”
Måtte man då icke lösa af detta bandet, på Sabbathen, denna Abrahams dotter, hvilken Satan bundit hafver, si, nu i aderton år?
17 Sa’ad da ya faɗi wannan, sai duka masu gāba da shi suka kunyata. Amma mutane kuwa suka yi murna saboda dukan abubuwan banmamaki da yake yi.
Och då han detta sade, skämde sig alle som honom emotståndit hade, och allt folket gladde sig af de härliga gerningar, som gjordes af honom.
18 Sai Yesu ya yi tambaya ya ce, “Yaya mulkin Allah yake? Da me zan kwatanta shi?
Så sade han då: Hvem är Guds rike likt? Och vid hvad skall jag likna det?
19 Yana kama da ƙwayar mustad, wadda wani mutum ya ɗauka, kuma ya shuka a gonarsa. Ta yi girma, ta zama itace, kuma tsuntsayen sararin sama suka huta a rassansa.”
Det är likt vid ett senapskorn, som en man tog, och sådde i sin örtagård; och det växte, och blef ett stort trä, och foglarna under himmelen bodde på dess qvistar.
20 Ya sāke tambaya, “Da me zan kwatanta mulkin Allah?
Och åter sade han: Vid hvad skall jag likna Guds rike?
21 Yana kama da yisti wadda mace ta ɗauka, ta kwaɓa garin alkama mai yawa da shi, har sai da yistin ya gauraye kullun duka.”
Det är likt enom surdeg, hvilken en qvinna tog, och lade in uti tre skäppor mjöl, tilldess det surnade alltsammans.
22 Sa’ad da Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi ta cikin garuruwan da ƙauyukan, yana koyarwa.
Och han gick igenom städer och byar, och lärde, och tog vägen åt Jerusalem.
23 Sai wani ya tambaye shi ya ce, “Ya Ubangiji, shin, wai mutane kima ne kawai za su sami ceto?” Ya ce musu,
Och en sade till honom: Herre, äro de ock få, som varda salige? Då sade han till dem:
24 “Ku yi matuƙar ƙoƙari ku shiga ta matsattsiyar ƙofa, domin ina faɗa muku, mutane da yawa za su yi ƙoƙarin shiga, amma ba za su iya ba.
Vinnlägger eder derom, att I kunnen ingå igenom den trånga porten; ty månge, säger jag eder, skola söka derefter, att de må inkomma, och skola dock icke kunna.
25 Da zaran maigidan ya tashi ya rufe ƙofar, za ku tsaya a waje kuna ƙwanƙwasawa, kuna roƙo cewa, ‘Ranka yă daɗe, buɗe mana ƙofa.’ “Amma shi zai amma ya ce, ‘Ni ban san ku, ko inda kuka fito ba.’
Sedan husbonden hafver uppståndit, och låtit dörren igen; och I begynnen stå ute, och bulta på dörren, sägande: Herre, Herre, låt upp för oss; och han svarar, och säger till eder: Jag vet intet af eder, hvadan I ären;
26 “Sa’an nan za ku ce, ‘Haba, mu da muka ci, muka sha tare da kai, har ka yi koyarwa a cikin titi-titi namu.’
Då skolen I begynna säga: Vi hafvom ätit och druckit med dig, och du hafver lärt på våra gator.
27 “Amma shi zai amma ya ce, ‘Ban san ku, ko inda kuka fito ba. Ku rabu da ni, dukan ku masu aikata mugunta!’
Och han skall säga: Jag säger eder, jag vet intet af eder, hvadan I ären; går ifrå mig, alle I ogerningsmän.
28 “Za a yi kuka a can, da cizon haƙora, sa’ad da kuka ga Ibrahim, da Ishaku, da Yaƙub, da dukan annabawa a mulkin Allah, amma ku kuwa, za a jefar da ku a waje.
Och der skall vara gråt och tandagnisslan; när I fån se Abraham, Isaac och Jacob, och alla Propheterna, i Guds rike; och eder utdrifvas.
29 Mutane za su zo daga gabas, da yamma, da kudu, da arewa, su ɗauki wuraren zamansu a bikin, a cikin mulkin Allah.
Och de skola komma ifrån östan och vestan, och nordan och sunnan, och skola sitta till bords i Guds rike.
30 Tabbatacce, akwai waɗansu da suke na ƙarshe, da za su zama na farko, na farko kuma, da za su zama na ƙarshe.”
Och si, det äro någre ytterste, som skola varda de främste; och någre främste, som skola varda de ytterste.
31 A wannan lokaci, waɗansu Farisiyawa suka zo suka ce wa Yesu, “Ka bar nan ka tafi wani wuri dabam. Hiridus yana so ya kashe ka.”
Samma dagen gingo någre Phariseer fram, och sade till honom: Skynda dig, och gack hädan; ty Herodes vill dräpa dig.
32 Ya amsa ya ce, “Ku je ku gaya wa dilan nan, wato, mai makirci cewa, ‘Da yau da kuma gobe, zan fitar da aljanu, in kuma warkar da mutane, sa’an nan a rana ta uku in cika burin aikina.
Då sade han till dem: Går, och säger dem räfvenom: Si, jag utdrifver djeflar, och helar i dag, och i morgon; och tredje dagen varder det ändadt med mig.
33 Duk da haka, dole in ci gaba da aikin a yau, da kuma gobe, sa’an nan in ci gaba da yin haka kashegari kuma, gama tabbatacce, ba annabi da yakan mutu a bayan birnin Urushalima!’
Dock likväl måste jag ännu vandra i dag, och i morgon, och öfvermorgon; ty det kan icke vara, att en Prophet förgås annorstädes än i Jerusalem.
34 “Urushalima, ayya Urushalima, ke da kika kashe annabawa, kuma kika jefa wa waɗanda aka aika gare ki da duwatsu. Sau da yawa na yi kewan in tattara’ya’yanki wuri ɗaya, kamar yadda kaza takan tattara’ya’yanta cikin fikafikanta, amma ba ki yarda ba!
Jerusalem, Jerusalem, du som dräper Propheterna, och stenar dem som sändas till dig; huru ofta ville jag församla din barn, likavisst som foglen sitt näste under sina vingar; och I villen icke?
35 Duba, an bar muku gidanku fanko. Ina kuwa faɗa muku, ba za ku sāke ganina ba, sai kun ce, ‘Mai albarka ne shi wanda yake zuwa cikin sunan Ubangiji.’”
Si, edart hus skall varda eder öde; och säger jag eder, att I skolen icke se mig, tilldess tiden kommer, att I varden sägande: Välsignad är han, som kommer i Herrans Namn.

< Luka 13 >