< Luka 12 >

1 Ana nan sa’ad da taron dubban mutane suka taru har suna tattaka juna, Yesu fara yin magana, da farko da almajiransa ya ce, “Ku yi hankali da yistin Farisiyawa, wato, munafunci.
Munako zana, chikiti chavantu chibena hamwina, mbwita nibalilyata jo bungi, chatanga kuwamba kuva rutwana bakwe, Mutokomere mulungo wava Farisi, iri kuliha
2 Ba abin da yake rufe da ba za a fallasa ba, ko kuma abin da yake ɓoye da ba za a bayyana ba.
Kono kakwina chinchinte, chete nichi kanwe kwi zibahazwa,
3 Abin da kuka faɗa a cikin duhu, za a ji shi a hasken rana. Kuma abin da kuka faɗa a kunne, a cikin ɗakunan ciki-ciki, za a yi shelarsa daga kan rufin ɗakuna.
Cwale chose cimu va wambi mwififi kachi zibahazwe mwiseli, mi chimubali kushovota muma ntwi kachi huwerezwe hakantungandi ke zuvo.
4 “Ina dai gaya muku abokaina, kada ku ji tsoron masu kashe jiki, amma bayan haka, ba sauran abin da za su iya yi.
Ni wamba kwenu balikani, kanji muntiyi behaya mubili, kuzwa ho kavena chimwi chiva ola kupanga,
5 Amma zan nuna muku wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron wanda, bayan da ya kashe jikin, yana da iko ya jefa ku cikin jahannama ta wuta. I, ina gaya muku, ku ji tsoronsa. (Geenna g1067)
Kono me ni mikalimera kuamana neni umowola kutiya. Mutiye yenke uzo Hamana kwi haya, wina ziho zo kutumina mwi here, Eye, Ni miwambira, mumutiye. (Geenna g1067)
6 Ba ana sayar da kanari biyar a kan kobo biyu ba? Duk da haka, Allah bai manta da ko ɗayansu ba.
Kena kuti tuzuni tukuma he yanza limwina tu uziwa hetenko i likana tukoviri to Vere? Kono nanganti konke kutuli kase hupulwa kweIreza.
7 Tabbatacce, gashin kanku ɗin nan ma, an ƙidaya su duka. Kada ku ji tsoro. Darajarku ta fi na kanari masu yawa girma.
Kono nangati i mpalo ye nsunki nzenu ivalitwe, Kanji mutiyi. Mwina butokwa kuhita tuzuni tungi.
8 “Ina gaya muku, duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, Ɗan Mutum ma zai shaida shi a gaban mala’ikun Allah.
Ni wamba kwenu, yense yo niwamba havusu bwa bantu, Mwana u muntu kaka muwambe naye habusu bwa mañiloyi e Ireza.
9 Amma wanda ya yi mūsun sanina a gaban mutane, shi ma za a yi mūsunsa a gaban mala’ikun Allah.
kono nyense yo nisampula havusu bwa Vvantu kaka sampulwe havunsu bwa mañiloyi e Reza.
10 Kuma duk wanda ya faɗi kalmar zagi a kan Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya saɓa wa Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
Yense yo wamba linzwi ivilala kuamana ni mwana wo Muntu, ka wonderwe awo mazwi, kono kozo yo wamba vuvilala kuamana ni Luhuho lu Njolola, kasana a wonderwe.
11 “Sa’ad da an kai ku a gaban majami’u, da gaban masu mulki, da kuma gaban masu iko, kada ku damu da yadda za ku kāre kanku, ko kuma abin da za ku faɗa,
Hasana kava mi lete havusu bwa masinangonge, va yendisi, ni vena ha muvuso, kanji ni muvireri kuamana nimwete ni mwi tavire ku amana ni kulizimanina, kamba chete ni muwambe,
12 gama Ruhu Mai Tsarki zai koya muku abin da ya dace ku faɗa a lokacin.”
kakuli Luhuho lu Njolola kalumi ka lumi lute mweyo nako chizi chi muswanera kuwamba.
13 Sai wani mutum daga cikin taron ya ce masa, “Malam, ka ce wa ɗan’uwana ya raba gādon da ni.”
Linu zumwi mukati kechisi cha cho kwali, “Muruti, wambire mukulwangu kuti a liyavire chifumu chavayoli name.”
14 Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai, wa ya naɗa ni alƙali, ko mai sulhu a tsakaninku?”
Jesu cha kwa li, “Mukwame, Jeni wani vika mu atuli kamba muzimanini hakati kenu?”
15 Sai ya ce musu, “Ku lura fa! Ku tsare kanku daga dukan kowane irin kwaɗayi. Ran mutum ba ya danganta a kan yawan dukiyarsa ba.”
Mi chati kuvali muli tokomere kobona kuti mulizwisa ku takazo yonse yomuuna, kakuti vuhalpo vo muntu kabwina vulyo hachi fumu chali kunganize muntu.”
16 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Gonar wani mai arziki ta ba da amfani sosai.
Linu Jesu chava wambira i nguli, ni kucho Iuwa lo mukwame yavali kufumite, luvali kuvikite ahulu,
17 Ya yi tunani a ransa ya ce, ‘Ba ni da inda zan ajiye amfanin gonana. Me zan yi ke nan?’
mi chali wambira ni kucho, chizi chete ni pange kakuli kanina chiviko cho kuvika zilyo zina lima?
18 “Sai ya ce, ‘Ga abin da zan yi. Zan rushe rumbunana, in gina manya, in zuba dukan hatsina da kayana a ciki.
Cha wamba, í chi jichona chete ni pange. Mu ni wise hansi zishente zangu ni kuzaka zikando ahulku, umo mwete ni vinke vuhenke bwangu vonse ni zimwi zimera zete ni sinze.
19 Ni kuma zan ce wa raina, “Kana da kaya da yawa masu kyau, da aka yi ajiyarsu domin shekaru da dama masu zuwa. Yi hutunka, ka ci, ka sha, ka yi annashuwa.”’
Muni wambe ku luhuho lwangu, “luhuho, wina zilyo zingi zisizitwe zonso seberise zirimo zingi. Pumule hande, lye, nwe, unsese.”
20 “Amma Allah ya ce masa, ‘Kai wawa! A wannan dare za a nemi ranka. Bayan haka, wa zai gāji abin da ka tara wa kanka?’
Kono Ireza cha cho kwali, 'Chihole cho mukwame, masiku a nsunu luhuho lwako luhindiwa kwanko, mi nzintu ziwa lukisa, muzive zani?'
21 “Haka zai zama ga duk wanda ya tara wa kansa dukiya, amma ba shi da arziki a gaban Allah.”
China mwe kalire muntu yoli kunganyiza chifumu kwali mi kafumite havusu bwe Ireza.”
22 Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Saboda haka, ina faɗa muku, kada ku damu game da rayuwarku, abin da za ku ci, ko kuma game da jikinku, abin da za ku yafa.
Jesu cha wamba kuva lutwana bakwe, “Cwale he nicho kwenu, kanji muivireri kuamana ni vuhalo bwenu - chizi chese mulye, kamba kuyana nizo mubiri wenu - chinzi chete muzwate.
23 Rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
Kakuti vuhalo bwina butokwa kuhita zilyo, mi muviri wina butokwa kuhita zizwato.
24 Ku dubi hankaki. Ba sa shuki ko girbi, kuma ba su da ɗakin ajiya ko rumbu ba, duk da haka, duk da haka, Allah na ciyar da su. Darajarku ta fi na tsuntsaye sau da yawa!
Mulemuhe ma ñwarara, kuti kava byali kamba kusiza. Kazina zivinko kamba zishete, kono Ireza uzilelra. Muvo vutokwa vule kuhita zizuni!
25 Wane ne a cikinku ta wurin damuwarsa, zai iya ƙara ko sa’a ɗaya ga rayuwarsa?
Mi jeni kwenu choku virera u wola kuyekeza i zuva kuvuhalo bwakwe?
26 Tun da ba za ku iya yin wannan ƙanƙanin abu ba, me ya sa kuke damuwa a kan sauran?
Cwale haiva kamu oli kupanga nanga nti chitu chinini, chinzi hamu virera kuamana ni nzonse?
27 “Ku dubi yadda furanni suke girma. Ba sukan yi aiki, ko saƙa ba, duk da haka, ina faɗa muku cewa, ko Solomon cikin kyakkyawan darajarsa duka, bai yafa kayan ado da ya kai kamar na ko ɗaya a cikinsu ba.
Mulemuhe tuyanga yanga mutumenena - zikula vule. Kazi sevezi, kamba kuhosa. Kono ni cho kwenu, nanga Salumoni mwi kanya yakwe kenba aba zwatikiwa uvu ji limwi.
28 In haka ne Allah yake yi wa ciyayin jeji sutura, wadda yau suna nan, sa’an nan gobe kuma a jefa cikin wuta, Allah ba zai yi muku sutura fiye da ciyayin jeji ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya!
Haiva Iraza uzwatika lyani lyomukanda, lina kwateni nsunu, mi inzona lizindirwa muhisa, inwe cwale mwa mizwatike vule, mawe inwe ve tumero inini!
29 Kada ku sa zuciyarku a kan abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kada ku damu a kan su.
Kanji mungani zete mulye kamba zete munwe kanji mu vireri.
30 Gama duniya da ba tă san Allah ba, tana faman neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa, ya san kuna bukatarsu.
Kakuli inkanda zonse ze fasi bangana inzi nzintu, mi Ishenu wizi kuti musaka inzi zintu.
31 Amma ku nemi mulkinsa, za a kuwa ƙara muku waɗannan abubuwa.
Kono musake mubuso wakwe, mi inzi zintu ka muziyekerezwe.
32 “Ya ƙaramin garke, kada ku ji tsoro, gama ya gamshi Ubanku ya ba ku mulkin.
Kanji mutiyi, tumberere tunini, kakuli i shenu i sangitwe kumiha Muvuso.
33 Ku sayar da dukiyarku, ku ba wa matalauta. Ku yi wa kanku jakar kuɗin da ba za su lalace ba. Ku yi wa kanku ajiyar dukiyar da ba za tă kare ba a sama, inda ɓarawo ba zai yi kusa ba, asu kuma ba za su iya su lalatar ba.
Mu uze maluwo enu mi muhe kuva shevete. Muli pangire ziviko zisa woli kusupala - Vufumu mwi wulu muzisa mani, uko kusengiri vasa mi Ifulapepe kuzisa shinyi.
34 Gama inda dukiyarku take, nan ne zuciyarku ma take.
Kakuti kwina chifumu chenu, uko ni inkulo yenu kwete ive nayo.
35 “Ku shirya ɗamara don hidima. Ku bar fitilunku suna ci,
Imunda zenu zisuminwe muma tunga mi malambi enu a zwirenhavusu ni kumbukuka,
36 kamar maza da suke jiran maigidansu ya dawo daga bikin aure. Saboda duk lokacin da ya dawo ya ƙwanƙwasa ƙofa, a shirye suke su buɗe masa nan da nan.
mi muswane uvu vantu bakwete kulola muyendisi wavo chakavola kumukiti we senso, iri kuti cha keza ni kwiza kungongo ta, yahaho bamwi yalwira mulyango.
37 Zai zama da albarka in maigida ya dawo, ya tarar da bayinsa suna zaman tsaro. Gaskiya ni faɗa muku, zai sa kayan hidima da kansa, ya sa bayinsa su zauna kan tebur, sa’an nan ya yi musu hidimar abinci.
Imbuyoti yaba bahikana, vesana keza wanikize niva lindire chakeza. Chama niti ni miwambire kuti keza nsumine ziwato zakwe zile mumunda che tunga, ni kuve kalika hasi kuzilyo, mi mwakeze nikwiza kuva haza.
38 Zai zama da albarka ga bayin da maigidansu ya iske su, suna zaman tsaro, a duk lokacin da ya dawo, ko da ya dawo a sa’a ta biyu, ko ta uku na tsakar dare ne.
Haiva muyendisi ukeza malunga siku, kamba kalya butatu bwe nako, ni kwiza kuva wana vali tukise, Imbuyoti zavo vahikana.
39 Amma ku fahimci wannan. Da maigida ya san sa’ar da ɓarawo zai zo, ai, da ba zai bari a shiga, a fasa masa gida ba.
Konohape mwizive inchi, kuti haiva muyendisi we nzuvo ave zivite inako iyo musa avali kukeza, nasana a va siyiriri inzuvo yakwe ni iñatulwa.
40 Ku ma, sai ku zauna da shiri, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku yi tsammani ba.”
Mulitukiseze nanwe vulyo, kakuti kamwizi inako iyo mwana o Muntu sana keze.”
41 Bitrus ya yi tambaya ya ce, “Ya Ubangiji, mu ne kake faɗa wa wannan misali, ko kuwa ga kowa da kowa ne?”
Pitorosi chati, “Simwine, uwambira iyi nguli kwetu fera, kamba niku vantu vonse?”
42 Ubangiji ya amsa ya ce, “To, wane ne manaja mai aminci da hikima, wanda maigida ya ba shi riƙon bayinsa, domin ya ba su abincinsu a daidai lokaci?
Mi Simwine chati, “Njeni he you sepahala ni kutalifa muyendisi simwine yata vike vuyendisi he wulu lya va hikana kuti a kuva hanga zilyo che nako iswanera?
43 Zai zama da albarka ga bawan nan wanda maigidan ya dawo, ya same shi yana yin haka.
Ufuyaulitwe uzo muhikana, uzo muyendisi wakwe keza wane napanga izo hakeza.
44 Gaskiya nake gaya muku, maigidan zai ba shi riƙon dukan dukiyarsa.
Cheniti niwamba kwenu kamuvike vuyendisi bwe luwo lyakwe.
45 Amma da a ce bawan ya yi tunani a zuciyarsa ya ce, ‘Ai, maigidana ya yi jinkirin dawowa,’ sa’an nan ya fara dūkan bayin, maza da mata, ya kuma shiga ci, da sha, har da buguwa.
Kono haiva uzo muhikana nali wambnira mwinkulo ya kwe, 'Simwine wangu unlyeha kuku vola; mi utanga ku mbupola bahikana vava kwame ni ve chanakazi Vahikana, ni kulya ni nwa, ni kukolwa,
46 Maigidan bawan nan zai dawo a ranar da wannan bawan bai yi tsammaninsa ba, kuma a sa’ar da bai sani ba. Maigidan zai yayyanka shi, ya kuma ba shi rabonsa tare da marasa bangaskiya.
simwine wozuna mu hikana kakeze mwizuba lyasa mulindire, ni mwi nako yasenzi mi kamu konsole mutu vindivindi nikumu tumina kuchi vaka chimwi navana vasasepahali.
47 “Bawan da ya san nufin maigidansa, kuma bai yi shiri ba, ko kuma bai yi abin da maigidansa yake so ba, zai sha mummunan duka.
Zuna muhikana, hace zivite mihupulo ya simwine wakwe, mi kena ava lukise kamba kuyendereza mwa sakira, kakaviwe cha mafaindi mangi.
48 Amma wanda bai sani ba, ya kuwa yi abin da ya isa horo, za a dūke shi kaɗan. Duk wanda aka ba shi mai yawa, mai yawan ne za a bida daga gare shi. Duk wanda kuma aka ba shi riƙon amana mai yawa, fiye da haka kuma za a bida daga gare shi.
Kono uzo yasana a bezivite, kakaviwe chama faindi mache. Zumwi ni zumwi kwali kuherwe a hulu, zingi kazi sakahane kwali, mi kwali vava sepahali ahulu, kava vuze zingi ahulu kwali.
49 “Na zo ne domin in kawo wuta a duniya. Ina so da ta riga ta ƙunu!
Ni vakezi kuzindira muliro mwi kanda, mi muni sangirwa kuti kamba ciwuva mbukulwa kale.
50 Amma ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa damu sosai, sai na kammala ta!
Kono nina i nkolovezo ini swanera kukolovezwa chayo, mi kaini kalikite hande konji chiya lizuziriza!
51 Kuna tsammani na zo domin in kawo salama a duniya ne? A’a! Ina gaya muku, rabuwa ne.
Muhupula kuti ni va kezi kuleta inkozo mwi ikanda? Ne, Ni ki wambira, kono niva leti ikauhano.
52 Daga yanzu, za a iske mutum biyar a gida ɗaya sun rabu, suna gāba da juna, uku suna gāba da biyu, biyun suna gāba da ukun.
Cwale kuzwa hanu kuya kuvusu, mukube mwizuvo nyonke inkauhano zeyanza lyonke - vantu vo tatwe kulyisa vovere, vantu vo vere kulwisa vantu vo tatwe.
53 Za su rarrabu. Mahaifi yana gāba da ɗan, ɗan kuma yana gāba da mahaifin. Mahaifiya tana gāba da diyar, diyar kuma tana gāba da mahaifiyar. Suruka tana gāba da matar ɗa, matar ɗa kuma tana gāba da suruka.”
Kava kauhane mushemi we chikwame kulwisa mwana kwe we chiswisu, ni mwana we chiswisu kulwisa isi; mushemi we chanakazi kulwisa mwanakwe we chikazana, ni mwana kazana kulwisa nyina; mukwenyani we chanakazi kulwisa mukwenyana kwe we chikazana, ni mukwenyani we chikazana kulwisa mukwenyanakwe we chanakazi.”
54 Ya ce wa taron, “Sa’ad da kuka ga hadari ya fito daga yamma, nan da nan kukan ce, ‘Za a yi ruwan sama,’ sai a kuwa yi.
Jesu avali kuwamba ni kuchisi bulyo,”Hamubona i kope lizimana kubwimino, yahaho mu wamba, 'I vula ikezite; mi iza kuva bulyo.
55 Sa’ad da kuma iska ta taso daga kudu, kukan ce, ‘Za a yi zafi,’ sai kuwa a yi.
Mi haiva luhuho lo kwiyaza lye chimonso ni hunga, mu wamba, 'Mukuhise a hulu nsunu; mi kwiza kuva vulyo.
56 Munafukai! Kuna san yadda za ku fassara yanayin ƙasa da na sararin sama. Ta yaya ba ku san yadda za ku yi fassarar wannan zamani ba?
Balihere, mwinzi kutoloka mayemo e kanda ni e wulu, linu vule hape hamusezi muku tolokerwa i nako ya hanu?
57 “Don me ba ku iya auna wa kanku, abin da yake daidai ba?
Chinzi hamusa atuli zina hande kwenu?
58 Yayinda kake kan hanyar zuwa kotu da maƙiyinka, ka yi matuƙar ƙoƙari ku shirya tun kuna kan hanya. In ba haka ba, zai kai ka gaban alƙali, alƙali kuma ya miƙa ka ga ɗan sanda, ɗan sanda kuma ya jefa ka a kurkuku.
Kakuli haiva no yenda niyo ku zekisa kumu atuli, mu zira ulike ahulu kuti mumane indava naye, iri kuli kanji naka kutambinki kumu atuli, mi kuti muatuli kanji a kaku tambiki kumu yendisi, mi munyendisi kanji a kakusoheri mwi ntorongo.
59 Ina gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.”
Ni wamba kwenu, kasana ko zwe mwateni konji hete no lihire ishereñi yama manimani yo kwete.”

< Luka 12 >