< Luka 12 >

1 Ana nan sa’ad da taron dubban mutane suka taru har suna tattaka juna, Yesu fara yin magana, da farko da almajiransa ya ce, “Ku yi hankali da yistin Farisiyawa, wato, munafunci.
Meanwhile the people had gathered in thousands, so that they trod on one another, when Jesus, addressing himself to his disciples, began by saying to them, ‘Be on your guard against the leaven – that is, the hypocrisy – of the Pharisees.
2 Ba abin da yake rufe da ba za a fallasa ba, ko kuma abin da yake ɓoye da ba za a bayyana ba.
There is nothing, however covered up, which will not be uncovered, nor anything kept secret which will not become known.
3 Abin da kuka faɗa a cikin duhu, za a ji shi a hasken rana. Kuma abin da kuka faɗa a kunne, a cikin ɗakunan ciki-ciki, za a yi shelarsa daga kan rufin ɗakuna.
So all that you have said in the dark will be heard in the light, and what you have spoken in the ear, within closed doors, will be proclaimed on the housetops.
4 “Ina dai gaya muku abokaina, kada ku ji tsoron masu kashe jiki, amma bayan haka, ba sauran abin da za su iya yi.
To you who are my friends I say, Do not be afraid of those who kill the body, but after that can do no more.
5 Amma zan nuna muku wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron wanda, bayan da ya kashe jikin, yana da iko ya jefa ku cikin jahannama ta wuta. I, ina gaya muku, ku ji tsoronsa. (Geenna g1067)
I will show you of whom you should be afraid. Be afraid of him who, after killing you, has the power to fling you into Gehenna. Yes, I say, be afraid of him. (Geenna g1067)
6 Ba ana sayar da kanari biyar a kan kobo biyu ba? Duk da haka, Allah bai manta da ko ɗayansu ba.
Are not five sparrows sold for two copper coins? Yet not one of them has escaped God’s notice.
7 Tabbatacce, gashin kanku ɗin nan ma, an ƙidaya su duka. Kada ku ji tsoro. Darajarku ta fi na kanari masu yawa girma.
No, even the hairs of your head are all numbered. Do not be afraid; you are of more value than many sparrows.
8 “Ina gaya muku, duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, Ɗan Mutum ma zai shaida shi a gaban mala’ikun Allah.
Everyone, I tell you, who publicly acknowledges me, the Son of Man, also, will acknowledge before God’s angels;
9 Amma wanda ya yi mūsun sanina a gaban mutane, shi ma za a yi mūsunsa a gaban mala’ikun Allah.
but the person who publicly disowns me will be altogether disowned before God’s angels.
10 Kuma duk wanda ya faɗi kalmar zagi a kan Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya saɓa wa Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.
Everyone who will say anything against the Son of Man will be forgiven, but for the person who slanders the Holy Spirit there will be no forgiveness.
11 “Sa’ad da an kai ku a gaban majami’u, da gaban masu mulki, da kuma gaban masu iko, kada ku damu da yadda za ku kāre kanku, ko kuma abin da za ku faɗa,
Whenever they take you before the synagogue Courts or the magistrates or other authorities, do not be anxious as to how you will defend yourselves, or what your defence will be, or what you will say;
12 gama Ruhu Mai Tsarki zai koya muku abin da ya dace ku faɗa a lokacin.”
for the Holy Spirit will show you at the moment what you ought to say.’
13 Sai wani mutum daga cikin taron ya ce masa, “Malam, ka ce wa ɗan’uwana ya raba gādon da ni.”
‘Teacher,’ a man in the crowd said to Jesus, ‘tell my brother to share the property with me.’
14 Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai, wa ya naɗa ni alƙali, ko mai sulhu a tsakaninku?”
But Jesus said to him, ‘Man, who made me a judge or an arbiter between you?’
15 Sai ya ce musu, “Ku lura fa! Ku tsare kanku daga dukan kowane irin kwaɗayi. Ran mutum ba ya danganta a kan yawan dukiyarsa ba.”
And then he added, ‘Take care to keep yourselves free from every form of covetousness; for even in the height of their prosperity a person’s true life does not depend on what they have.’
16 Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Gonar wani mai arziki ta ba da amfani sosai.
Then Jesus told them this parable – ‘There was once a rich man whose land was very fertile;
17 Ya yi tunani a ransa ya ce, ‘Ba ni da inda zan ajiye amfanin gonana. Me zan yi ke nan?’
and he began to ask himself “What will I do, for I have nowhere to store my crops?
18 “Sai ya ce, ‘Ga abin da zan yi. Zan rushe rumbunana, in gina manya, in zuba dukan hatsina da kayana a ciki.
This is what I will do,” he said; “I will pull down my barns and build larger ones, and store all my grain and my goods in them;
19 Ni kuma zan ce wa raina, “Kana da kaya da yawa masu kyau, da aka yi ajiyarsu domin shekaru da dama masu zuwa. Yi hutunka, ka ci, ka sha, ka yi annashuwa.”’
and I will say to myself, Now you have plenty of good things put by for many years; take your ease, eat, drink, and enjoy yourself.”
20 “Amma Allah ya ce masa, ‘Kai wawa! A wannan dare za a nemi ranka. Bayan haka, wa zai gāji abin da ka tara wa kanka?’
But God said to the man “Fool! This very night your life is being demanded; and as for all you have prepared – who will have it?”
21 “Haka zai zama ga duk wanda ya tara wa kansa dukiya, amma ba shi da arziki a gaban Allah.”
So it is with those who lay by wealth for themselves and are not rich to the glory of God.’
22 Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Saboda haka, ina faɗa muku, kada ku damu game da rayuwarku, abin da za ku ci, ko kuma game da jikinku, abin da za ku yafa.
And Jesus said to his disciples, ‘That is why I say to you, Do not be anxious about the life here – what you can get to eat; or about your body – what you can get to wear.
23 Rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi.
For life is more than food, and the body than its clothes.
24 Ku dubi hankaki. Ba sa shuki ko girbi, kuma ba su da ɗakin ajiya ko rumbu ba, duk da haka, duk da haka, Allah na ciyar da su. Darajarku ta fi na tsuntsaye sau da yawa!
Think of the ravens – they neither sow nor reap; they have neither storehouse nor barn; and yet God feeds them! And how much more precious are you than birds!
25 Wane ne a cikinku ta wurin damuwarsa, zai iya ƙara ko sa’a ɗaya ga rayuwarsa?
But which of you, by being anxious, can prolong your life a moment?
26 Tun da ba za ku iya yin wannan ƙanƙanin abu ba, me ya sa kuke damuwa a kan sauran?
And, if you cannot do even the smallest thing, why be anxious about other things?
27 “Ku dubi yadda furanni suke girma. Ba sukan yi aiki, ko saƙa ba, duk da haka, ina faɗa muku cewa, ko Solomon cikin kyakkyawan darajarsa duka, bai yafa kayan ado da ya kai kamar na ko ɗaya a cikinsu ba.
Think of the lilies, and how they grow. They neither toil nor spin; yet, I tell you, even Solomon in all his splendour was not robed like one of these.
28 In haka ne Allah yake yi wa ciyayin jeji sutura, wadda yau suna nan, sa’an nan gobe kuma a jefa cikin wuta, Allah ba zai yi muku sutura fiye da ciyayin jeji ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya!
If, even in the field, God so clothes the grass which is living today and tomorrow will be thrown into the oven, how much more will he clothe you, you of little faith!
29 Kada ku sa zuciyarku a kan abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kada ku damu a kan su.
And you – do not be always seeking what you can get to eat or what you can get to drink; and do not waver.
30 Gama duniya da ba tă san Allah ba, tana faman neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa, ya san kuna bukatarsu.
These are the things for which all the nations of the world are seeking, and your Father knows that you need them.
31 Amma ku nemi mulkinsa, za a kuwa ƙara muku waɗannan abubuwa.
No, seek his kingdom, and these things will be added for you.
32 “Ya ƙaramin garke, kada ku ji tsoro, gama ya gamshi Ubanku ya ba ku mulkin.
So do not be afraid, my little flock, for your Father has been pleased to give you the kingdom.
33 Ku sayar da dukiyarku, ku ba wa matalauta. Ku yi wa kanku jakar kuɗin da ba za su lalace ba. Ku yi wa kanku ajiyar dukiyar da ba za tă kare ba a sama, inda ɓarawo ba zai yi kusa ba, asu kuma ba za su iya su lalatar ba.
‘Sell what belongs to you, and give in charity. Make yourselves purses that will not wear out – an inexhaustible treasure in heaven, where no thief comes near, or moth works ruin.
34 Gama inda dukiyarku take, nan ne zuciyarku ma take.
For where your treasure is, there also will your heart be.
35 “Ku shirya ɗamara don hidima. Ku bar fitilunku suna ci,
Make yourselves ready, with your lamps alight;
36 kamar maza da suke jiran maigidansu ya dawo daga bikin aure. Saboda duk lokacin da ya dawo ya ƙwanƙwasa ƙofa, a shirye suke su buɗe masa nan da nan.
and be like servants who are waiting for their Master’s return from his wedding, so that, when he comes and knocks, they may open the door for him at once.
37 Zai zama da albarka in maigida ya dawo, ya tarar da bayinsa suna zaman tsaro. Gaskiya ni faɗa muku, zai sa kayan hidima da kansa, ya sa bayinsa su zauna kan tebur, sa’an nan ya yi musu hidimar abinci.
Happy are those servants whom, on his return, the Master will find watching. I tell you that he will make himself ready, and have them take their places at the table, and will come and serve them.
38 Zai zama da albarka ga bayin da maigidansu ya iske su, suna zaman tsaro, a duk lokacin da ya dawo, ko da ya dawo a sa’a ta biyu, ko ta uku na tsakar dare ne.
Whether it is late at night, or in the early morning that he comes, if he finds all as it should be, then happy are they.
39 Amma ku fahimci wannan. Da maigida ya san sa’ar da ɓarawo zai zo, ai, da ba zai bari a shiga, a fasa masa gida ba.
This you do know, that, had the owner of the house known at what time the thief was coming, he would have been on the watch, and would not have let his house be broken into.
40 Ku ma, sai ku zauna da shiri, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku yi tsammani ba.”
You must also prepare, for when you are least expecting him the Son of Man will come.’
41 Bitrus ya yi tambaya ya ce, “Ya Ubangiji, mu ne kake faɗa wa wannan misali, ko kuwa ga kowa da kowa ne?”
‘Master,’ said Peter, ‘are you telling this parable with reference to us or to everyone?’
42 Ubangiji ya amsa ya ce, “To, wane ne manaja mai aminci da hikima, wanda maigida ya ba shi riƙon bayinsa, domin ya ba su abincinsu a daidai lokaci?
‘Who, then,’ replied the Master, ‘is that trustworthy steward, the careful man, who will be placed by his master over his establishment, to give them their rations at the proper time?
43 Zai zama da albarka ga bawan nan wanda maigidan ya dawo, ya same shi yana yin haka.
Happy will that servant be whom his master, when he comes home, will find doing this.
44 Gaskiya nake gaya muku, maigidan zai ba shi riƙon dukan dukiyarsa.
His master, I tell you, will put him in charge of the whole of his property.
45 Amma da a ce bawan ya yi tunani a zuciyarsa ya ce, ‘Ai, maigidana ya yi jinkirin dawowa,’ sa’an nan ya fara dūkan bayin, maza da mata, ya kuma shiga ci, da sha, har da buguwa.
But should that servant say to himself “My master is a long time coming,” and begin to beat the menservants and the maidservants, and to eat and drink and get drunk,
46 Maigidan bawan nan zai dawo a ranar da wannan bawan bai yi tsammaninsa ba, kuma a sa’ar da bai sani ba. Maigidan zai yayyanka shi, ya kuma ba shi rabonsa tare da marasa bangaskiya.
that servant’s master will come on a day when he does not expect him, and at an hour of which he is unaware, and will flog him severely and assign him his place among the untrustworthy.
47 “Bawan da ya san nufin maigidansa, kuma bai yi shiri ba, ko kuma bai yi abin da maigidansa yake so ba, zai sha mummunan duka.
The servant who knows his master’s wishes and yet does not prepare and act accordingly will receive many lashes;
48 Amma wanda bai sani ba, ya kuwa yi abin da ya isa horo, za a dūke shi kaɗan. Duk wanda aka ba shi mai yawa, mai yawan ne za a bida daga gare shi. Duk wanda kuma aka ba shi riƙon amana mai yawa, fiye da haka kuma za a bida daga gare shi.
while one who does not know his master’s wishes, but acts so as to deserve a flogging, will receive but few. From everyone to whom much has been given much will be expected, and from the man to whom much has been entrusted the more will be demanded.
49 “Na zo ne domin in kawo wuta a duniya. Ina so da ta riga ta ƙunu!
I came to cast fire on the earth; and what more can I wish, if it is already kindled?
50 Amma ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa damu sosai, sai na kammala ta!
There is a baptism that I must undergo, and how great is my distress until it is over!
51 Kuna tsammani na zo domin in kawo salama a duniya ne? A’a! Ina gaya muku, rabuwa ne.
Do you think that I am here to bring peace on earth? No, I tell you, but to cause division.
52 Daga yanzu, za a iske mutum biyar a gida ɗaya sun rabu, suna gāba da juna, uku suna gāba da biyu, biyun suna gāba da ukun.
For from this time, if there are five people in a house, they will be divided, three against two, and two against three.
53 Za su rarrabu. Mahaifi yana gāba da ɗan, ɗan kuma yana gāba da mahaifin. Mahaifiya tana gāba da diyar, diyar kuma tana gāba da mahaifiyar. Suruka tana gāba da matar ɗa, matar ɗa kuma tana gāba da suruka.”
Father will be opposed to son and son to father, mother to daughter and daughter to mother, mother-in-law to her daughter-in-law and daughter-in-law to her mother-in-law.’
54 Ya ce wa taron, “Sa’ad da kuka ga hadari ya fito daga yamma, nan da nan kukan ce, ‘Za a yi ruwan sama,’ sai a kuwa yi.
And to the people Jesus said, ‘When you see a cloud rising in the west, you say at once “There is a storm coming,” and come it does.
55 Sa’ad da kuma iska ta taso daga kudu, kukan ce, ‘Za a yi zafi,’ sai kuwa a yi.
And when you see that the wind is in the south, you say “It will be burning hot,” and so it proves.
56 Munafukai! Kuna san yadda za ku fassara yanayin ƙasa da na sararin sama. Ta yaya ba ku san yadda za ku yi fassarar wannan zamani ba?
Hypocrites! You know how to judge of the earth and the sky; how is it, then, that you cannot judge of this time?
57 “Don me ba ku iya auna wa kanku, abin da yake daidai ba?
Why don’t you yourselves decide what is right?
58 Yayinda kake kan hanyar zuwa kotu da maƙiyinka, ka yi matuƙar ƙoƙari ku shirya tun kuna kan hanya. In ba haka ba, zai kai ka gaban alƙali, alƙali kuma ya miƙa ka ga ɗan sanda, ɗan sanda kuma ya jefa ka a kurkuku.
When, for instance, you are going with your opponent before a magistrate, on your way to the court do your best to be quit of him; otherwise he might drag you before the judge, then the judge will hand you over to the bailiff of the court, and the bailiff throw you into prison.
59 Ina gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.”
You will not, I tell you, come out until you have paid the very last cent.’

< Luka 12 >