< Luka 11 >

1 Wata rana Yesu yana addu’a a wani wuri. Da ya gama, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Ubangiji, ka koya mana yin addu’a, kamar yadda Yohanna ya koya wa almajiransa.”
I kad se moljaše Bogu na jednom mjestu pa presta, reèe mu neki od uèenika njegovijeh: Gospode! nauèi nas moliti se Bogu, kao što i Jovan nauèi svoje uèenike.
2 Sai ya ce musu, “Sa’ad da kuke yin addu’a ku ce, “‘Ya Uba, sunanka mai tsarki ne mulkinka ya zo.
A on im reèe: kad se molite Bogu govorite: oèe naš koji si na nebesima, da se sveti ime tvoje; da doðe carstvo tvoje; da bude volja tvoja i na zemlji kao na nebu;
3 Ka ba mu kowace rana abincin yini.
Hljeb naš potrebni daji nam svaki dan;
4 Ka gafarta mana zunubanmu, kamar yadda mu ma ke gafarta wa duk wanda ya yi mana laifi. Kada ka bari a kai mu cikin jarraba.’”
I oprosti nam grijehe naše, jer i mi opraštamo svakome dužniku svojemu; i ne navedi nas u napast; nego nas izbavi oda zla.
5 Sa’an nan ya ce musu, “Da a ce ɗayanku yana da aboki, sa’an nan ya je wurinsa da tsakar dare ya ce, ‘Aboki, ranta mini burodi guda uku,
I reèe im: koji od vas ima prijatelja, i otide mu u ponoæi i reèe mu: prijatelju! daj mi tri hljeba u zajam;
6 domin wani abokina da yake tafiya ya sauka a wurina. Ga shi, ba ni da abinci da zan ba shi.’
Jer mi doðe prijatelj s puta, i nemam mu šta postaviti;
7 Sai wanda yake cikin ɗaki ya amsa ya ce, ‘Kada ka dame ni. An riga an kulle ƙofa, da ni da yarana kuwa mun kwanta, ba zan iya tashi in ba ka kome ba.’
A on iznutra odgovarajuæi da reèe: ne uznemiruj me; veæ su vrata zatvorena i djeca su moja sa mnom u postelji, i ne mogu ustati da ti dam.
8 Ina gaya muku, ko da yake ba zai so ya tashi ya ba shi burodin don shi abokinsa ne ba, duk da haka, zai tashi ya ba shi yawan abin da yake bukata, saboda nacewarsa.
I kažem vam: ako i ne ustane da mu da zato što mu je prijatelj, ali za njegovo bezobrazno iskanje ustaæe i daæe mu koliko treba.
9 “Don haka ina faɗa muku, ku roƙa, za a ba ku, ku nema za ku samu, ku ƙwanƙwasa za a kuwa buɗe muku ƙofa.
I ja vama kažem: ištite i daæe vam se: tražite i naæi æete; kucajte i otvoriæe vam se.
10 Gama duk wanda ya roƙa, yana karɓa, mai nema yana samu, wanda ya ƙwanƙwasa kuma, za a buɗe masa ƙofa.
Jer svaki koji ište, prima; i koji traži, nalazi; i koji kuca, otvora mu se.
11 “Wane mahaifi ne a cikinku, in ɗansa ya roƙe shi kifi, zai ba shi maciji a maimakon,
Koji je meðu vama otac u koga ako sin zaište hljeba da mu da kamen? Ili ako zaište ribe da mu da mjesto ribe zmiju?
12 ko kuma in ya roƙi ƙwai, ya ba shi kunama?
Ili ako zaište jaje da mu da skorpiju?
13 In fa haka ne, ko da yake ku mugaye ne, kun san ba’ya’yanku kyautai masu kyau, balle fa Ubanku na sama, zai yi fiye da haka, ta wurin ba da Ruhu Mai Tsarki, ga masu roƙonsa!”
Kad dakle vi, zli buduæi, umijete dobre dare davati djeci svojoj, koliko æe više otac nebeski dati Duha svetoga onima koji ištu u njega?
14 Sa’ad da Yesu yake fitar da wani beben aljani daga wani mutum, da aljanin ya fita, sai mutumin wanda da bebe ne, ya yi magana, taron kuwa suka yi mamaki.
I jednom izgna ðavola koji bješe nijem; kad ðavo iziðe progovori nijemi; i diviše se ljudi.
15 Amma waɗansunsu suka ce, “Ai, da ikon Be’elzebub, sarkin aljanu ne, yake fitar da aljanu.”
A neki od njih rekoše: pomoæu Veelzevula kneza ðavolskoga izgoni ðavole.
16 Waɗansu kuma suka gwada shi, ta wurin neman yă nuna musu wata alama daga sama.
A drugi kušajuæi ga iskahu od njega znak s neba.
17 Yesu kuwa ya san tunaninsu, sai ya ce musu, “Duk mulkin da yake gāba da kansa, zai lalace, kuma gidan da yake gaba da kansa zai rushe.
A on znajuæi pomisli njihove reèe im: svako carstvo koje se razdijeli samo po sebi, opustjeæe, i dom koji se razdijeli sam po sebi, propašæe.
18 In Shaiɗan yana gāba da kansa, yaya mulkinsa zai tsaya? Ina faɗin haka domin kun ce, da ikon Be’elzebub nake fitar da aljanu.
Tako i sotona ako se razdijeli sam po sebi, kako æe ostati njegovo carstvo? kao što kažete da pomoæu Veelzevula izgonim ðavole.
19 In da ikon Be’elzebub nake fitar da su, to, da ikon wa masu binku suke fitar da su? Saboda haka, za su zama alƙalanku ke nan.
Ako li ja pomoæu Veelzevula izgonim ðavole, sinovi vaši èijom pomoæu izgone? Zato æe vam oni biti sudije.
20 Amma in da ikon Allah ne ni nake fitar da aljanu, ashe, mulkin Allah ya zo muku ke nan.
A ako li ja prstom Božijim izgonim ðavole, dakle je došlo k vama carstvo Božije.
21 “Sa’ad da mutum mai ƙarfi, wanda yake da makamai yana gadin gidan kansa, an tsare lafiyar dukiyarsa ke nan.
Kad se jaki naoruža i èuva svoj dvor, imanje je njegovo na miru;
22 Amma in wani wanda ya fi shi ƙarfi, ya faɗa masa ya kuma sha ƙarfinsa, yakan ƙwace makaman da mutumin ke dogara da su, ya kuma rarraba ganima.
A kad doðe jaèi od njega i nadvlada ga, uzme sve oružje njegovo u koje se uzdao, i razdijeli što otme od njega.
23 “Wanda ba ya tare da ni, yana gāba da ni, wanda kuma ba ya tarawa da ni, watsarwa yake yi.
Koji nije sa mnom, protiv mene je; i koji sa mnom ne sabira, prosipa.
24 “Lokacin da mugun ruhu ya fita daga mutum, sai ya bi ta wuraren da ba mutane, yana neman hutu, amma ya kāsa samu, sai ya ce, ‘Zan koma gidan da na bari.’
Kad neèisti duh iziðe iz èovjeka, ide kroz bezvodna mjesta tražeæi pokoja, i ne našavši reèe: da se vratim u dom svoj otkuda sam izišao;
25 Sa’ad da ya koma, ya tarar da gidan a share da tsabta, kuma a shirye.
I došavši naðe pometen i ukrašen.
26 Sai ya je ya ɗebo waɗansu ruhohi bakwai da suka fi shi mugunta, sai su shiga su zauna a wurin. Ƙarshen wannan mutum kuwa zai fi farkonsa muni.”
Tada otide i uzme sedam drugijeh duhova gorijeh od sebe, i ušavši žive ondje; i bude potonje èovjeku onome gore od prvoga.
27 Da Yesu yake cikin faɗin waɗannan abubuwa, sai wata mace daga cikin taron ta ɗaga murya ta ce masa, “Mai albarka ce uwar da ta haife ka, wadda ka sha mamanta.”
A kad to govoraše, podiže glas jedna žena iz naroda i reèe mu: blago utrobi koja te je nosila, i sisama koje si sao!
28 Yesu ya amsa ya ce, “A maimakon, masu albarka ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma biyayya da ita.”
A on reèe: blago i onima koji slušaju rijeè Božiju, i drže je.
29 Da taron mutane suka ƙaru, sai Yesu ya ce, “Wannan mugun zamani ne. Tana neman wani abin banmamaki, amma ba ko ɗaya da za a ba ta, sai dai ta Yunana.
A narodu koji se skupljaše stade govoriti: rod je ovaj zao; ište znak, i neæe mu se dati znak osim znaka Jone proroka;
30 Kamar yadda Yunana ya zama alama ga mutanen Ninebe, haka ma Ɗan Mutum zai zama ga zamanin nan.
Jer kako što Jona bi znak Ninevljanima, tako æe i sin èovjeèij biti rodu ovome.
31 A ranar shari’a, Sarauniyar Kudu za tă tashi tsaye tare da wannan zamani, ta yanke wa wannan zamani hukunci, domin ta zo daga ƙarshen duniya ta saurari hikimar Solomon, ga shi kuwa, shi wanda ya fi Solomon girma, na nan.
Carica južna iziæi æe na sud s ljudima roda ovoga, i osudiæe ih; jer ona doðe s kraja zemlje da sluša premudrost Solomunovu: a gle, ovdje je veæi od Solomuna.
32 A ranar shari’a, mutanen Ninebe za su tashi tsaye tare da wannan zamani, su yanke wa wannan zamani hukunci. Gama sun tuba sa’ad da Yunana ya yi musu wa’azi. Ga shi yanzu, shi wanda ya fi Yunana girma, na nan.
Ninevljani iziæi æe na sud s rodom ovijem, i osudiæe ga; jer se pokajaše pouèenjem Joninijem: a gle, ovdje je veæi od Jone.
33 “Babu wanda yakan ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta, ko ya rufe ta da murfi ba. A maimako, yakan ajiye ta a kan wurin ajiye fitila, don masu shiga su ga haske.
Niko ne meæe zapaljene svijeæe na sakriveno mjesto, niti pod sud, nego na svijeænjak da vide svjetlost koji ulaze.
34 Idonka shi ne fitilar jikinka. Sa’ad da idanunka suna da lafiya, dukan jikinka ma na cike da haske, amma sa’ad da idanunka suna da lahani, dukan jikinka ma na cike da duhu.
Svijeæa je tijelu oko. Ako dakle oko tvoje bude zdravo, sve æe tijelo tvoje biti svijetlo; ako li oko tvoje bude kvarno, i tijelo je tvoje tamno.
35 Ka lura fa, kada hasken da yake cikinka ya zamana duhu ne.
Gledaj dakle da vidjelo koje je u tebi ne bude tama.
36 Saboda haka, in dukan jikinka yana cike da haske, ba inda ke da duhu, jikinka kuwa zai kasance da haske gaba ɗaya, kamar yadda hasken fitila yake haskaka ka.”
Jer ako je sve tijelo tvoje svijetlo da nema nikakvoga uda tamna, biæe svijetlo kao kad te svijeæa obasjava svjetlošæu.
37 Da Yesu ya gama magana, sai wani Bafarisiye ya gayyace shi cin abinci tare da shi. Sai kuwa ya shiga ya zauna a tebur.
A kad govoraše, moljaše ga nekakav farisej da objeduje u njega. A on ušavši sjede za trpezu.
38 Amma Bafarisiyen ya lura cewa, Yesu bai wanke hannu kafin ya ci abinci ba, sai mamaki ya kama shi.
A farisej se zaèudi kad vidje da se najprije ne umi prije objeda.
39 Sai Ubangiji ya ce masa, “Ku Farisiyawa, kukan wanke bayan kwano da kwaf, amma a ciki kuna cike da kwaɗayi da mugunta.
A Gospod reèe mu: sad vi fariseji spolja èistite èašu i zdjelu, a iznutra vam je puno grabeža i zlobe.
40 Ku wawayen mutane! Ashe, wanda ya yi bayan, ba shi ne kuma ya yi cikin ba?
Bezumni! nije li onaj naèinio i iznutra koji je spolja naèinio?
41 Ku ba matalauta abin da yake cikin kwano, kuma kome zai zama muku da tsabta.
Ali dajite milostinju od onoga što je unutra; i gle, sve æe vam biti èisto.
42 “Kaitonku, Farisiyawa, domin kuna ba wa Allah zakka na na’ana’arku, da ƙarƙashinku, da kuma sauran ganyen lambunku iri-iri, amma kun ƙyale adalci da ƙaunar Allah. Ya kamata da kun kiyaye na ƙarshen, ban ba barin na farkon.
Ali teško vama farisejima što dajete desetak od metvice i od rute i od svakoga povræa, a prolazite pravdu i ljubav Božiju: ovo je trebalo èiniti, i ono ne ostavljati.
43 “Kaitonku, Farisiyawa, domin kun cika son wuraren zama masu daraja a majami’u, da kuma yawan gaisuwa a wuraren kasuwanci.
Teško vama farisejima što tražite zaèelja po zbornicama i da vam se klanja po ulicama.
44 “Kaitonku, domin ku kamar kaburbura ne da ba a sa musu alama ba, waɗanda mutane suke takawa don rashin sani.”
Teško vama književnici i fariseji, licemjeri, što ste kao sakriveni grobovi po kojima ljudi idu i ne znadu ih.
45 Sai ɗaya daga cikin masanan dokoki ya ce wa Yesu, “Malam, in ka faɗi waɗannan abubuwa haka, kai kuma ka zage mu ke nan.”
A neki od zakonika odgovarajuæi reèe: uèitelju! govoreæi to i nas sramotiš.
46 Yesu ya amsa ya ce, “Ku masanan dokoki ma, kaitonku, domin kun ɗora wa mutane kaya masu nauyi waɗanda da ƙyar suke ɗaukawa, amma ku da kanku ba za ku sa ko yatsa ɗaya, don ku taimake su ba.
A on reèe: teško i vama zakonicima što tovarite na ljude bremena preteška za nošenje, a vi jednijem prstom svojijem neæete da ih prihvatite.
47 “Kaitonku, domin kun gina kaburbura saboda annabawa, nan kuwa kakannin-kakanninku ne suka kashe su.
Teško vama što zidate grobove prorocima, a vaši su ih ocevi pobili.
48 Wannan ya shaida cewa kun amince da abin da kakannin-kakanninku suka yi. Sun karkashe annabawa, ku kuma kun gina kaburburansu.
Vi dakle svjedoèite i odobravate djela otaca svojijeh; jer ih oni pobiše, a vi im grobove zidate.
49 Saboda haka, Allah a cikin hikimarsa ya ce, ‘Zan aika musu da annabawa da manzanni. Za su kashe waɗansu, su kuma tsananta wa waɗansu.’
Zato i premudrost Božija reèe: poslaæu im proroke i apostole, i od njih æe jedne pobiti, a druge protjerati;
50 Saboda haka, alhakin jinin dukan annabawa da aka kashe, tun farkon duniya, yana kan wannan zamani,
Da se ište od roda ovoga krv sviju proroka koja je prolivena od postanja svijeta,
51 wato, tun daga jinin Habila, har zuwa jinin Zakariya, wanda aka kashe tsakanin bagade da mazauni. I, ina gaya muku, alhakinsu duka yana kan wannan zamani.
Od krvi Aveljeve tja do krvi Zarijne, koji pogibe meðu oltarom i crkvom. Da, kažem vam, iskaæe se od roda ovoga.
52 “Kaitonku, masanan dokoki, domin kun ɗauke mabuɗin ilimi. Ku kanku ba ku shiga ba, kuma kun hana wa waɗanda suke shiga, su shiga.”
Teško vama zakonici što uzeste kljuè od znanja: sami ne uðoste, a koji šæadijahu da uðu, zabraniste im.
53 Da Yesu ya bar wurin, sai Farisiyawa da malaman dokoki suka fara gaba mai tsanani da shi, kuma suna tsokanansa da tambayoyi.
A kad im on ovo govoraše, poèeše književnici i fariseji vrlo navaljivati k njemu i mnogijem pitanjem zabunjivati ga,
54 Suna fakonsa, don su kama shi a kan wata magana da zai faɗa.
Vrebajuæi i pazeæi na njega ne bi li što ulovili iz usta njegovijeh da ga okrive.

< Luka 11 >