< Luka 10 >

1 Bayan haka, Ubangiji ya naɗa waɗansu mutum saba’in da biyu, ya aike su biyu-biyu, su riga shi yin gaba zuwa kowane gari da kowane wuri da zai shiga.
After these things the Lord chose seventy others also, and sent them out two by two before His face, into every place and city, where He was about to come.
2 Ya ce musu, “Girbi na da yawa, amma ma’aikata kaɗan ne. Saboda haka, ku roƙi Ubangijin girbi ya aikar da ma’aikata zuwa gonarsa.
And He said to them, The harvest is indeed great, but the laborers are few: therefore pray you the Lord of the harvest, that He may send forth laborers into His harvest.
3 Ku tafi! Ina aikan ku kamar tumaki cikin kyarketai.
Go: behold, I send you forth as lambs in the midst of wolves.
4 Kada ku ɗauki jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma. Kada ma ku gai da kowa a kan hanya.
Take neither purse, nor valise, nor sandals: salute no one by the way.
5 “Sa’ad da kuka shiga wani gida, ku fara da cewa, ‘Salama a gare ku mutanen gida.’
Into whatsoever house you may enter, first say, Peace be unto this house.
6 In akwai mutum mai salama a gidan, salamarku za tă kasance tare da shi, in kuwa babu, salamarku za tă koma muku.
And if the son of peace may be there, your peace shall rest upon it: but if not, it shall return unto you.
7 Ku zauna a wannan gidan, kuna ci kuna shan duk abin da suka ba ku, gama ma’aikaci ya cancanci albashinsa. Kada ku yi yawan sāke masauƙi, daga gida zuwa gida.
Abide in the same house, eating and drinking those things which are with them: for the laborer is worthy of his hire. Go not from house to house.
8 “Sa’ad da kuka shiga garin, kuma aka karɓe ku, ku ci ko mene ne da aka ajiye a gabanku.
Into whatsoever city you may enter and they may receive you, eat those things which are placed by you:
9 Ku warkar da marasa lafiya da suke wurin. Ku kuma faɗa musu cewa, ‘Mulkin Allah yana kusa da ku.’
and heal the sick who are in it, and say to them, The kingdom of God has come nigh unto you.
10 Amma sa’ad da kuka shiga garin, kuma ba a karɓe ku ba, ku bi titi-titi ku ce,
And into whatsoever city you may enter, and they may not receive you, having come out into the streets of the same, say,
11 ‘Ko ƙurar garinku da kuke manne a ƙafafunmu, mun karkaɗe muku. Duk da haka, ku tabbatar da wannan, “Mulkin Allah yana kusa.”’
Even the dust from your city, that cleaveth to our feet, do we wipe off against you: but know this, that the kingdom of God is at hand.
12 Ina dai faɗa muku, a ranan nan, za a fi jin tausayin Sodom fiye da wannan garin.
For I say unto you, that it will be more tolerable in that day for Sodom than for that city.
13 “‘Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida!’ Ai, da a ce a Taya da Sidon ne aka yi ayyukan banmamaki da aka yi a cikinku, da tuni sun tuba, suna zama cikin rigar makoki da toka.
Woe unto thee, Chorazin! woe unto thee, Bethsaida! for if the mighty works which were wrought in you had been in Tyre and Sidon, they would have repented long ago, sitting down in sackcloth and ashes.
14 A ranar shari’a, za a fi jin tausayin Taya da Sidon fiye da ku.
Moreover it shall be more tolerable for Tyre and Sidon in the judgment than for you.
15 Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani za ki sami ɗaukaka ne? A’a, za a hallaka ki. (Hadēs g86)
And thou, Capernaum, art thou not exalted up to heaven? thou shalt be cast down to Hades. (Hadēs g86)
16 “Wanda ya saurare ku, ni yake saurara. Wanda ya ƙi ku, ni yake ƙi. Amma wanda ya ƙi ni kuwa, ya ƙi wanda ya aiko ni ne.”
He that heareth you heareth me; he that rejecteth you rejecteth me; and he that rejecteth me rejecteth Him that sent me.
17 Mutum saba’in da biyun nan suka dawo da murna, suka ce, “Ubangiji, har mun sha ƙarfin aljanu ma a cikin sunanka.”
And the seventy returned with joy, saying, Lord, even the demons are subordinated to us in thy name.
18 Sai ya amsa ya ce, “Na ga Shaiɗan ya fāɗi daga sama kamar walƙiya.
And He said to them, I saw Satan having fallen as the lightning from heaven.
19 Na ba ku iko da za ku tattaka macizai, da kunamai, ku kuma shawo kan dukan ikon abokin gāba, kuma ba wani lahani da zai same ku.
Behold I have given you authority to tread upon serpents and scorpions, and over all the power of the enemy; and nothing shall hurt you.
20 Duk da haka, kada ku yi farin ciki da cewa, kun sha ƙarfin ruhohi, amma ku yi farin ciki, domin an rubuta sunayenku a sama.”
Moreover do not rejoice in this, that the spirits are subject unto you; but rejoice that your names are written in the heavens.
21 A wannan lokaci, Yesu, cike da murna ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Na yabe ka, ya Uba, Ubangijin sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima, da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. I, ya Uba, gama wannan shi ne nufinka mai kyau.
At the same hour He rejoiced in the Holy Spirit, and said, I praise thee, O Father, Lord of the heaven and the earth, because thou hast hidden these things from the wise and prudent, and revealed them to babes: yea, Father, because it was thus pleasing in thy sight.
22 “Ubana ya danƙa mini dukan kome. Ba wanda ya san Ɗan sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Ɗan, da kuma waɗanda Ɗan ya zaɓa ya bayyana musu shi.”
And turning to His disciples, He said, All things have been delivered to me by my Father: and no one knoweth who the Son is, except the Father; and who the Father is, except the Son, and he to whom He may wish to reveal Him.
23 Sai ya juya wajen almajiransa, ya ce musu a ɓoye, “Albarka ga idanun da suka ga abin da kuke gani.
And turning to His disciples, privately He said, Happy are your eyes, seeing those things which you see.
24 Ina faɗa muku, annabawa da sarakuna da yawa sun so su ga abin nan da kuke gani, amma ba su gani ba. Sun so su ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.”
For I say unto you, that many kings and prophets desired to see those things which you see, and saw them not; and to hear those things which you hear, and heard them not.
25 Wata rana, sai wani masanin dokoki ya miƙe tsaye don yă gwada Yesu. Ya tambaya ya ce, “Malam, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
And behold, a certain lawyer stood up tempting Him, saying, Teacher, having done what shall I inherit eternal life? (aiōnios g166)
26 Yesu ya amsa ya ce, “Me aka rubuta a cikin Doka? Yaya kake karanta ta?”
He said to him, What has been written in the law? how do you read it?
27 Sai ya amsa ya ce, “‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan ƙarfinka, da kuma dukan hankalinka’; kuma, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
And he responding said, Thou shalt love the Lord thy God with divine love from all thy heart, and with all thy soul, and with all thy strength, and with all thy mind; and thy neighbor as thyself.
28 Yesu ya ce, “Ka amsa daidai. Ka yi haka, kuma za ka rayu.”
And He said to him, You answered correctly: do this, and you shall live.
29 Amma domin ya kāre kansa, sai ya tambayi Yesu ya ce, “Shin, wane ne maƙwabcina?”
But he, wishing to justify himself, said to Jesus, And who is my neighbor?
30 Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum ya tashi daga Urushalima za shi Yeriko, sai ya fāɗi a hannun mafasa, wato,’yan fashi. Suka ƙwace tufafinsa, suka yi masa dūka, suka bar shi nan bakin rai da mutuwa.
Jesus responding said, A certain man was going down from Jerusalem to Jericho; and fell among thieves, who indeed having stripped him of his raiment, administered blows, went away, leaving him half dead.
31 Ya zamana wani firist ya bi kan wannan hanya. Da ya ga mutumin, sai ya bi gefe ya wuce abinsa.
And by chance a certain priest came down that way: and seeing him, passed by on the other side.
32 Haka ma wani daga kabilar Lawi, mai hidima cikin haikali, da ya zo wurin, ya gan shi, sai shi ma ya bi gefe ɗaya, ya wuce abinsa.
And likewise also a Levite, being at the place, coming and seeing, passed by on the other side.
33 Amma wani mutumin Samariya da yake kan tafiya, da ya kai inda mutumin yake, ya gan shi, sai ya ji tausayinsa.
And a certain Samaritan, on a journey, came near him: and seeing, had compassion on him,
34 Ya je wurinsa, ya daddaure masa raunukansa, sa’an nan ya zuba mai, da ruwan inabi. Ya ɗauki mutumin ya sa a kan jakinsa, ya kai shi wani masauƙi, ya yi jinyarsa.
and having come to him, he bound up his wounds, pouring in oil and wine: and having mounted him on his own beast, carried him to a tavern, and cared for him.
35 Kashegari, sai ya ɗauki dinari biyu, ya ba wa mai masauƙin ya ce, ‘Ka lura da shi, bayan na dawo, zan biya ka duk abin da ka ƙara kashewa a kansa.’
And on the morrow, taking out two denaria, gave them to the host, and said, Care for him; and whatsoever you expend in addition, on my return, I will pay you.
36 “A ganinka, a cikin waɗannan mutane uku, wane ne maƙwabcin mutumin da ya fāɗi a hannun mafasa?”
Which one of these three seems to you to have been the neighbor of him who fell among the thieves?
37 Masanin dokoki ya amsa ya ce, “Wanda ya nuna masa jinƙai.” Yesu ya ce masa, “Je ka, ka yi haka nan.”
And he said, The one having done mercy with him. And Jesus said to him, Go, thou, and do likewise.
38 Yayinda Yesu da almajiransa suna cikin tafiya, sai ya kai wani ƙauye inda wata mace mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.
And it came to pass while they were going round, He also came into a certain village: and a certain woman by name Martha received Him into her house.
39 Tana da’yar’uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a gaban Ubangiji tana jin maganarsa.
And there was a sister to her called Mary, who indeed sitting down at the feet of the Lord, continued to hear his word:
40 Marta kuwa, aikin hidima da ya kamata a yi, ya ɗauke mata hankali, sai ta zo wurin Yesu, ta ce, “Ubangiji, ba ka damu da yadda’yar’uwata ta bar mini aiki ni kaɗai ba? Gaya mata ta taimake ni!”
and Martha was very busy about much serving. And standing over Him, she said, Lord, is there no care to thee that my sister has left me to serve alone? then say to her that she must assist me.
41 Amma Ubangiji ya amsa ya ce, “Marta, Marta, hankalinki ya tashi, kuma kina damuwa a kan abubuwa da yawa.
And the Lord responding said to her, Martha, Martha, you are solicitous and encumbered concerning many things:
42 Amma abu ɗaya tak ake bukata, Maryamu ta zaɓi abin da ya fi kyau, kuma ba za a raba ta da shi ba.”
but there is need of one thing: for Mary has chosen the good part, which shall not be taken from her.

< Luka 10 >