< Luka 10 >

1 Bayan haka, Ubangiji ya naɗa waɗansu mutum saba’in da biyu, ya aike su biyu-biyu, su riga shi yin gaba zuwa kowane gari da kowane wuri da zai shiga.
这之后,主又另外指派了七十名门徒,派他们两人一组先行一步,去往他计划造访的所有城邦。
2 Ya ce musu, “Girbi na da yawa, amma ma’aikata kaɗan ne. Saboda haka, ku roƙi Ubangijin girbi ya aikar da ma’aikata zuwa gonarsa.
耶稣对他们说:“需要收割的庄稼很多,但工人太少,这时候就要向收获之主祈祷,让他派工人去他的农田收割庄稼。
3 Ku tafi! Ina aikan ku kamar tumaki cikin kyarketai.
所以去吧,我派你们出去,就像羊羔走进狼群。
4 Kada ku ɗauki jakar kuɗi, ko jaka, ko takalma. Kada ma ku gai da kowa a kan hanya.
不要带钱袋、口袋和鞋,遇见其他人也不要闲聊。
5 “Sa’ad da kuka shiga wani gida, ku fara da cewa, ‘Salama a gare ku mutanen gida.’
无论走进哪一栋房子,先说:‘愿平安降临这里!’
6 In akwai mutum mai salama a gidan, salamarku za tă kasance tare da shi, in kuwa babu, salamarku za tă koma muku.
那里若有平安之人,你们的平安就会降临于他们,否则,这平安仍为你们所有。
7 Ku zauna a wannan gidan, kuna ci kuna shan duk abin da suka ba ku, gama ma’aikaci ya cancanci albashinsa. Kada ku yi yawan sāke masauƙi, daga gida zuwa gida.
你们要住在那人的家中,他们给你吃喝,因为工人就应该获得报酬,不必在各家之间搬来搬去。
8 “Sa’ad da kuka shiga garin, kuma aka karɓe ku, ku ci ko mene ne da aka ajiye a gabanku.
无论你走进哪座城中,那里的人若欢迎你们,他们送上什么食物就吃什么。
9 Ku warkar da marasa lafiya da suke wurin. Ku kuma faɗa musu cewa, ‘Mulkin Allah yana kusa da ku.’
然后医治城中的病人,告诉他们:‘上帝之国已经降临。’
10 Amma sa’ad da kuka shiga garin, kuma ba a karɓe ku ba, ku bi titi-titi ku ce,
但无论你们进入哪座城,那里的人若不接待你们,就穿街过巷地告诉他们:
11 ‘Ko ƙurar garinku da kuke manne a ƙafafunmu, mun karkaɗe muku. Duk da haka, ku tabbatar da wannan, “Mulkin Allah yana kusa.”’
‘我们会把这城里沾在我们脚上的尘土拂去,以此表达对你们的失望。但你们应该意识到:上帝之国已经降临。’
12 Ina dai faɗa muku, a ranan nan, za a fi jin tausayin Sodom fiye da wannan garin.
我告诉你们,到了审判日那天,索多玛甚至都要比这座城更好。
13 “‘Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida!’ Ai, da a ce a Taya da Sidon ne aka yi ayyukan banmamaki da aka yi a cikinku, da tuni sun tuba, suna zama cikin rigar makoki da toka.
哥拉逊啊,你有祸了!伯赛大啊,你有祸了!因为在你们那里显化的神迹,如果换做是在推罗和西顿,城里的人早就披上粗布衣,坐在地上悔改了。
14 A ranar shari’a, za a fi jin tausayin Taya da Sidon fiye da ku.
所以到了审判日那天,你们所受的苦,要比推罗和西顿还重。
15 Ke kuma Kafarnahum, kina tsammani za ki sami ɗaukaka ne? A’a, za a hallaka ki. (Hadēs g86)
还有你,迦百农!你不会被高举到天堂,而是会坠入阴府。 (Hadēs g86)
16 “Wanda ya saurare ku, ni yake saurara. Wanda ya ƙi ku, ni yake ƙi. Amma wanda ya ƙi ni kuwa, ya ƙi wanda ya aiko ni ne.”
听从你们的人就是听从于我,拒绝你们的人就是拒绝我。但拒绝我,就是拒绝那派我来此之人。”
17 Mutum saba’in da biyun nan suka dawo da murna, suka ce, “Ubangiji, har mun sha ƙarfin aljanu ma a cikin sunanka.”
那七十名门徒回来的时候兴奋地说:“主啊,因你之名,即使是魔鬼也听从我们!”
18 Sai ya amsa ya ce, “Na ga Shaiɗan ya fāɗi daga sama kamar walƙiya.
耶稣说:“我看见撒旦像闪电一样从天空坠落。
19 Na ba ku iko da za ku tattaka macizai, da kunamai, ku kuma shawo kan dukan ikon abokin gāba, kuma ba wani lahani da zai same ku.
是的,我给了你们力量去毁灭蛇和蝎子,去战胜所有实力强大的仇敌。没有什么能伤害你们了。
20 Duk da haka, kada ku yi farin ciki da cewa, kun sha ƙarfin ruhohi, amma ku yi farin ciki, domin an rubuta sunayenku a sama.”
但不要因鬼怪听从你们就欢喜。你们欢喜,应该是因为你们的名字被记录在天堂。”
21 A wannan lokaci, Yesu, cike da murna ta wurin Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Na yabe ka, ya Uba, Ubangijin sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima, da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. I, ya Uba, gama wannan shi ne nufinka mai kyau.
就在这时,耶稣心中充满圣灵的喜悦。他说:“父啊,天地之主,我感谢你,因为你在智慧和聪明人面前隐藏起这一切,却将其显现给孩童。父啊,是的,这样做会让你感到欢喜。
22 “Ubana ya danƙa mini dukan kome. Ba wanda ya san Ɗan sai Uban, kuma ba wanda ya san Uban, sai Ɗan, da kuma waɗanda Ɗan ya zaɓa ya bayyana musu shi.”
我父已经把一切交给我,除了我父没有人能理解人子。除了人子以及人子愿意向其显示之人,没有人能理解我父。”
23 Sai ya juya wajen almajiransa, ya ce musu a ɓoye, “Albarka ga idanun da suka ga abin da kuke gani.
当周围没有其他人时,耶稣转过身来对门徒说:“那些能见你们所见之人,真的是有福了!
24 Ina faɗa muku, annabawa da sarakuna da yawa sun so su ga abin nan da kuke gani, amma ba su gani ba. Sun so su ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.”
我告诉你们,曾有许多先知和君王,想看到你们所见的一切,却无法看到,想听你们所听的一切,却无法听到。”
25 Wata rana, sai wani masanin dokoki ya miƙe tsaye don yă gwada Yesu. Ya tambaya ya ce, “Malam, me zan yi don in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
曾有一个研究法律的专家站起来,试图用问题为难耶稣。他说:“老师,我要怎么做才可以获得永生呢?” (aiōnios g166)
26 Yesu ya amsa ya ce, “Me aka rubuta a cikin Doka? Yaya kake karanta ta?”
耶稣问他:“律法上是怎么写的?你看到了什么?”
27 Sai ya amsa ya ce, “‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka, da dukan ranka, da dukan ƙarfinka, da kuma dukan hankalinka’; kuma, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’”
那人回答:“你要全心、全性、全力、全意爱你的主上帝,要爱邻居如爱自己。”
28 Yesu ya ce, “Ka amsa daidai. Ka yi haka, kuma za ka rayu.”
耶稣说:“你说对了。这样做就会获得永生。”
29 Amma domin ya kāre kansa, sai ya tambayi Yesu ya ce, “Shin, wane ne maƙwabcina?”
但那人还想为自己的想法辩护,就问耶稣:“那么谁是我的邻居呢?”
30 Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum ya tashi daga Urushalima za shi Yeriko, sai ya fāɗi a hannun mafasa, wato,’yan fashi. Suka ƙwace tufafinsa, suka yi masa dūka, suka bar shi nan bakin rai da mutuwa.
耶稣回答:“一个人从耶路撒冷去往耶利哥,途中遇到强盗,他们剥去他的衣服,殴打他,然后把他丢在那里,让他等死。
31 Ya zamana wani firist ya bi kan wannan hanya. Da ya ga mutumin, sai ya bi gefe ya wuce abinsa.
正好有一名祭司走过那条路,但看见他后,却绕道走开了。
32 Haka ma wani daga kabilar Lawi, mai hidima cikin haikali, da ya zo wurin, ya gan shi, sai shi ma ya bi gefe ɗaya, ya wuce abinsa.
有一个利未人也路过,但走到这里看到这个男人,也绕道走开了。
33 Amma wani mutumin Samariya da yake kan tafiya, da ya kai inda mutumin yake, ya gan shi, sai ya ji tausayinsa.
最后一个撒玛利亚人走来路过此地,看见这个男人,心生怜悯。
34 Ya je wurinsa, ya daddaure masa raunukansa, sa’an nan ya zuba mai, da ruwan inabi. Ya ɗauki mutumin ya sa a kan jakinsa, ya kai shi wani masauƙi, ya yi jinyarsa.
于是走上前,用油和酒处理他的伤口,将他包扎好,扶上自己的驴子,带他住进一个客店,照顾他。
35 Kashegari, sai ya ɗauki dinari biyu, ya ba wa mai masauƙin ya ce, ‘Ka lura da shi, bayan na dawo, zan biya ka duk abin da ka ƙara kashewa a kansa.’
第二天,这个撒玛利亚人拿出两个银币交给店主,说:‘请你照顾他,如果有额外的花销,等我回来的时候会还给你。’
36 “A ganinka, a cikin waɗannan mutane uku, wane ne maƙwabcin mutumin da ya fāɗi a hannun mafasa?”
那么你认为,对于这个被强盗抢劫的人而言,这三个人中谁是他的邻居呢?”
37 Masanin dokoki ya amsa ya ce, “Wanda ya nuna masa jinƙai.” Yesu ya ce masa, “Je ka, ka yi haka nan.”
研究法律的专家说:“就是那个表达善意的人。” 耶稣说:“那就去做同样的事情吧。”
38 Yayinda Yesu da almajiransa suna cikin tafiya, sai ya kai wani ƙauye inda wata mace mai suna Marta ta marabce shi a gidanta.
耶稣和众人继续赶路,走进一个村庄。有一个名叫马大的女人,请耶稣到自己家里。
39 Tana da’yar’uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a gaban Ubangiji tana jin maganarsa.
她有一个妹妹名叫玛利亚,坐在主的面前听道。
40 Marta kuwa, aikin hidima da ya kamata a yi, ya ɗauke mata hankali, sai ta zo wurin Yesu, ta ce, “Ubangiji, ba ka damu da yadda’yar’uwata ta bar mini aiki ni kaɗai ba? Gaya mata ta taimake ni!”
马大当时忙着准备饭菜,有很多需要做的事情,感到有些不快。于是就上前来说:“主人,我妹妹让我一个人做这些事情,请让她来帮帮我。”
41 Amma Ubangiji ya amsa ya ce, “Marta, Marta, hankalinki ya tashi, kuma kina damuwa a kan abubuwa da yawa.
主回答她:“马大啊,马大,你为所有这些事操心忙碌,
42 Amma abu ɗaya tak ake bukata, Maryamu ta zaɓi abin da ya fi kyau, kuma ba za a raba ta da shi ba.”
但只有一件事是必做的,玛利亚选择了正确之事,这不能从她那里剥夺。”

< Luka 10 >