< Luka 1 >

1 Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
Как уже многие начали составлять повествования о совершенно известных между нами событиях,
2 kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
как передали нам то бывшие с самого начала очевидцами и служителями Слова,
3 Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
то рассудилось и мне, по тщательном исследовании всего сначала, по порядку описать тебе, достопочтенный Феофил,
4 don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
чтобы ты узнал твердое основание того учения, в котором был наставлен.
5 A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
Во дни Ирода, царя Иудейского, был священник из Авиевой чреды, именем Захария, и жена его из рода Ааронова, имя ей Елисавета.
6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
Оба они были праведны пред Богом, поступая по всем заповедям и уставам Господним беспорочно.
7 Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
У них не было детей, ибо Елисавета была неплодна, и оба были уже в летах преклонных.
8 Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
Однажды, когда он в порядке своей чреды служил пред Богом,
9 sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
по жребию, как обыкновенно было у священников, досталось ему войти в храм Господень для каждения,
10 Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
а все множество народа молилось вне во время каждения, -
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
тогда явился ему Ангел Господень, стоя по правую сторону жертвенника кадильного.
12 Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
Захария, увидев его, смутился, и страх напал на него.
13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
Ангел же сказал ему: не бойся, Захария, ибо услышана молитва твоя, и жена твоя Елисавета родит тебе сына, и наречешь ему имя: Иоанн;
14 Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
и будет тебе радость и веселие, и многие о рождении его возрадуются,
15 gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
ибо он будет велик пред Господом; не будет пить вина и сикера, и Духа Святаго исполнится еще от чрева матери своей;
16 Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
и многих из сынов Израилевых обратит к Господу Богу их;
17 Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
и предъидет пред Ним в духе и силе Илии, чтобы возвратить сердца отцов детям, и непокоривым образ мыслей праведников, дабы представить Господу народ приготовленный.
18 Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
И сказал Захария Ангелу: по чему я узнаю это? ибо я стар, и жена моя в летах преклонных.
19 Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
Ангел сказал ему в ответ: я Гавриил, предстоящий пред Богом, и послан говорить с тобою и благовестить тебе сие;
20 Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
и вот, ты будешь молчать и не будешь иметь возможности говорить до того дня, как это сбудется, за то, что ты не поверил словам моим, которые сбудутся в свое время.
21 Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
Между тем народ ожидал Захарию и дивился, что он медлит в храме.
22 Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
Он же, выйдя, не мог говорить к ним; и они поняли, что он видел видение в храме; и он объяснялся с ними знаками, и оставался нем.
23 Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
А когда окончились дни службы его, возвратился в дом свой.
24 Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
После сих дней зачала Елисавета, жена его, и таилась пять месяцев и говорила:
25 Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
так сотворил мне Господь во дни сии, в которые призрел на меня, чтобы снять с меня поношение между людьми.
26 A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
В шестой же месяц послан был Ангел Гавриил от Бога в город Галилейский, называемый Назарет,
27 gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
к Деве, обрученной мужу, именем Иосифу, из дома Давидова; имя же Деве: Мария.
28 Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
Ангел, войдя к Ней, сказал: радуйся, Благодатная! Господь с Тобою; благословенна Ты между женами.
29 Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
Она же, увидев его, смутилась от слов его и размышляла, что бы это было за приветствие.
30 Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
И сказал Ей Ангел: не бойся, Мария, ибо Ты обрела благодать у Бога;
31 Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
и вот, зачнешь во чреве, и родишь Сына, и наречешь Ему имя: Иисус.
32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
Он будет велик и наречется Сыном Всевышнего, и даст Ему Господь Бог престол Давида, отца Его;
33 zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
и будет царствовать над домом Иакова во веки, и Царству Его не будет конца. (aiōn g165)
34 Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
Мария же сказала Ангелу: как будет это, когда я мужа не знаю?
35 Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
Ангел сказал Ей в ответ: Дух Святый найдет на Тебя, и сила Всевышнего осенит Тебя; посему и рождаемое Святое наречется Сыном Божиим.
36 ’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
Вот и Елисавета, родственница Твоя, называемая неплодною, и она зачала сына в старости своей, и ей уже шестой месяц,
37 Gama ba abin da zai gagari Allah.”
ибо у Бога не останется бессильным никакое слово.
38 Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
Тогда Мария сказала: се, Раба Господня; да будет Мне по слову твоему. И отошел от Нее Ангел.
39 A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
Встав же Мария во дни сии, с поспешностью пошла в нагорную страну, в город Иудин,
40 inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
и вошла в дом Захарии, и приветствовала Елисавету.
41 Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
Когда Елисавета услышала приветствие Марии, взыграл младенец во чреве ее; и Елисавета исполнилась Святаго Духа,
42 Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
и воскликнула громким голосом, и сказала: благословенна Ты между женами, и благословен плод чрева Твоего!
43 Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
И откуда это мне, что пришла Матерь Господа моего ко мне?
44 Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
Ибо когда голос приветствия Твоего дошел до слуха моего, взыграл младенец радостно во чреве моем.
45 Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
И блаженна Уверовавшая, потому что совершится сказанное ей от Господа.
46 Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
И сказала Мария: величает душа моя Господа,
47 ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
и возрадовался дух мой о Боге, Спасителе моем,
48 gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
что призрел Он на смирение рабы своей, ибо отныне будут ублажать меня все роды;
49 gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
что сотворил мне величие Сильный, и свято имя Его;
50 Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
и милость Его в роды родов к боящимся Его;
51 Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
явил силу мышцы Своей; рассеял надменных помышлениями сердца их;
52 Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
низложил сильных с престолов, и вознес смиренных;
53 Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
алчущих исполнил благ, и богатящихся отпустил ни с чем;
54 Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
воспринял Израиля, отрока Своего, воспомянув милость,
55 ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
как говорил отцам нашим, к Аврааму и семени его до века. (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
Пребыла же Мария с нею около трех месяцев, и возвратилась в дом свой.
57 Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
Елисавете же настало время родить, и она родила сына.
58 Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
И услышали соседи и родственники ее, что возвеличил Господь милость Свою над нею, и радовались с нею.
59 A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
В восьмой день пришли обрезать младенца и хотели назвать его, по имени отца его, Захариею.
60 amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
На это мать его сказала: нет, а назвать его Иоанном.
61 Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
И сказали ей: никого нет в родстве твоем, кто назывался бы сим именем.
62 Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
И спрашивали знаками у отца его, как бы он хотел назвать его.
63 Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
Он потребовал дощечку и написал: Иоанн имя ему. И все удивились.
64 Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
И тотчас разрешились уста его и язык его, и он стал говорить, благословляя Бога.
65 Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
И был страх на всех живущих вокруг них; и рассказывали обо всем этом по всей нагорной стране Иудейской.
66 Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
Все слышавшие положили это на сердце своем и говорили: что будет младенец сей? И рука Господня была с ним.
67 Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
И Захария, отец его, исполнился Святаго Духа и пророчествовал, говоря:
68 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
благословен Господь Бог Израилев, что посетил народ Свой и сотворил избавление ему,
69 Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
и воздвиг рог спасения нам в дому Давида, отрока Своего,
70 (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
как возвестил устами бывших от века святых пророков Своих, (aiōn g165)
71 cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
что спасет нас от врагов наших и от руки всех ненавидящих нас;
72 don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
сотворит милость с отцами нашими и помянет святой завет Свой,
73 rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
клятву, которою клялся Он Аврааму, отцу нашему, дать нам,
74 don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
небоязненно, по избавлении от руки врагов наших,
75 cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
служить Ему в святости и правде пред Ним, во все дни жизни нашей.
76 “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
И ты, младенец, наречешься пророком Всевышнего, ибо предъидешь пред лицем Господа приготовить пути Ему,
77 don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
дать уразуметь народу Его спасение в прощении грехов их,
78 saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
по благоутробному милосердию Бога нашего, которым посетил нас Восток свыше,
79 don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
просветить сидящих во тьме и тени смертной, направить ноги наши на путь мира.
80 Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.
Младенец же возрастал и укреплялся духом, и был в пустынях до дня явления своего Израилю.

< Luka 1 >