< Luka 1 >

1 Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
Après que plusieurs ont entrepris de composer une relation des choses dont on a parmi nous pleine conviction,
2 kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
conformément à ce que nous ont transmis ceux qui ont été dès le commencement, témoins oculaires et ministres de la parole;
3 Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
j’ai résolu moi aussi, après m’être appliqué à connaître exactement toutes choses depuis l’origine, de t’en écrire le récit suivi, excellent Théophile,
4 don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
afin que tu reconnaisses la certitude des enseignements que tu as reçus.
5 A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
Aux jours d’Hérode, roi de Judée, il y avait un prêtre, nommé Zacharie, de la classe d’Abia; et sa femme, qui était une des filles d’Aaron, s’appelait Elisabeth.
6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
Tous deux étaient justes devant Dieu, marchant dans tous les commandements et ordonnances du Seigneur, d’une manière irréprochable.
7 Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
Ils n’avaient pas d’enfants, parce qu’Elisabeth était stérile, et ils étaient l’un et l’autre avancés en âge.
8 Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
Or, pendant que Zacharie s’acquittait devant Dieu des fonctions sacerdotales, dans l’ordre de sa classe,
9 sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
il fut désigné par le sort, selon la coutume observée par les prêtres, pour entrer dans le sanctuaire du Seigneur et y offrir l’encens.
10 Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
Et toute la multitude du peuple était dehors en prière à l’heure de l’encens.
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
Mais un ange du Seigneur lui apparut, debout à droite de l’autel de l’encens.
12 Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
Zacharie, en le voyant, fut troublé, et la crainte le saisit.
13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
Mais l’ange lui dit: « Ne crains pas, Zacharie, car ta prière a été exaucée; ta femme Elisabeth te donnera un fils que tu appelleras Jean.
14 Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
Il sera pour toi un sujet de joie et d’allégresse, et beaucoup se réjouiront de sa naissance;
15 gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
car il sera grand devant le Seigneur. Il ne boira ni vin, ni rien qui enivre, car il sera rempli de l’Esprit-Saint dès le sein de sa mère.
16 Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
Il convertira beaucoup d’enfants d’Israël au Seigneur leur Dieu;
17 Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
et lui-même marchera devant lui, dans l’esprit et la puissance d’Élie, pour ramener les cœurs des pères vers les enfants, et les indociles à la sagesse des justes, afin de préparer au Seigneur un peuple parfait. »
18 Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
Zacharie dit à l’ange: « A quoi reconnaîtrai-je que cela sera? Car je suis vieux, et ma femme est avancée en âge. »
19 Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
L’ange lui répondit: « Je suis Gabriel, qui me tiens devant Dieu; j’ai été envoyé pour te parler et t’annoncer cette heureuse nouvelle.
20 Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
Et voici que tu seras muet et ne pourras parler jusqu’au jour où ces choses arriveront, parce que tu n’as pas cru à mes paroles, qui s’accompliront en leur temps. »
21 Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
Cependant le peuple attendait Zacharie, et il s’étonnait qu’il demeurât si longtemps dans le sanctuaire.
22 Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
Mais étant sorti, il ne pouvait leur parler, et ils comprirent qu’il avait eu une vision dans le sanctuaire, ce qu’il leur faisait entendre par signes; et il resta muet.
23 Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
Quand les jours de son ministère furent accomplis, il s’en alla en sa maison.
24 Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
Quelque temps après, Elisabeth, sa femme, conçut, et elle se tint cachée pendant cinq mois, disant:
25 Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
« C’est une grâce que le Seigneur m’a faite, au jour où il m’a regardée pour ôter mon opprobre parmi les hommes. »
26 A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
Au sixième mois, l’ange Gabriel fut envoyé de Dieu dans une ville de Galilée appelée Nazareth,
27 gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
auprès d’une vierge qui était fiancée à un homme de la maison de David, nommé Joseph, et le nom de la vierge était Marie.
28 Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
L’ange étant entré où elle était, lui dit: « Je te salue, pleine de grâce; le Seigneur est avec toi, tu es bénie entre les femmes. »
29 Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
Marie l’ayant aperçu, fut troublée de ses paroles, et elle se demandait ce que pouvait signifier cette salutation.
30 Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
L’ange lui dit: « Ne crains pas, Marie, car tu as trouvé grâce devant Dieu.
31 Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
Voici que tu concevras en ton sein, et tu enfanteras un fils, et tu lui donneras le nom de Jésus.
32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
Il sera grand, on l’appellera le Fils du Très-Haut; le Seigneur Dieu lui donnera le trône de David son père;
33 zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
il régnera éternellement sur la maison de Jacob, et son règne n’aura pas de fin. » (aiōn g165)
34 Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
Marie dit à l’ange: « Comment cela se fera-t-il, puisque je ne connais pas d’homme? »
35 Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
L’ange lui répondit: « L’Esprit-Saint viendra sur toi, et la vertu du Très-Haut te couvrira de son ombre. C’est pourquoi l’être saint qui naîtra de toi sera appelé Fils de Dieu.
36 ’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
Déjà Elisabeth, ta parente, a conçu elle aussi, un fils dans sa vieillesse, et c’est actuellement son sixième mois, à elle que l’on appelle stérile:
37 Gama ba abin da zai gagari Allah.”
car rien ne sera impossible à Dieu. »
38 Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
Marie dit alors: « Voici la servante du Seigneur, qu’il me soit fait selon ta parole. » Et l’ange la quitta.
39 A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
En ces jours-là, Marie se levant, s’en alla en hâte au pays des montagnes, en une ville de Juda.
40 inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
Et elle entra dans la maison de Zacharie, et salua Élisabeth.
41 Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
Or, dès qu’Élisabeth eut entendu la salutation de Marie, l’enfant tressaillit dans son sein, et elle fut remplie du Saint-Esprit.
42 Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
Et élevant la voix, elle s’écria: « Tu es bénie entre les femmes, et le fruit de tes entrailles est béni.
43 Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
Et d’où m’est-il donné que la mère de mon Seigneur vienne à moi?
44 Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
Car ta voix, lorsque tu m’as saluée, n’a pas plus tôt frappé mes oreilles, que mon enfant a tressailli de joie dans mon sein.
45 Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
Heureuse celle qui a cru! car elles seront accomplies les choses qui lui ont été dites de la part du Seigneur! »
46 Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
Et Marie dit: « Mon âme glorifie le Seigneur.
47 ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
Et mon esprit tressaille de joie en Dieu, mon Sauveur,
48 gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
Parce qu’ il a jeté les yeux sur la bassesse de sa servante. Voici, en effet, que désormais toutes les générations m’appelleront bienheureuse,
49 gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
Parce qu’il a fait en moi de grandes choses, Celui qui est puissant, Et dont le nom est saint,
50 Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
Et dont la miséricorde s’étend d’âge en âge, Sur ceux qui le craignent.
51 Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
Il a déployé la force de son bras; Il a dissipé ceux qui s’enorgueillissaient dans les pensées de leur cœur;
52 Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
Il a renversé de leur trône les potentats, Et il a élevé les petits;
53 Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
Il a comblé de biens les affamés, Et les riches, il les a renvoyés les mains vides.
54 Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
Il a pris soin d’Israël son serviteur, Se ressouvenant de sa miséricorde,
55 ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
(Ainsi qu’il l’avait promis à nos pères) Envers Abraham et sa race, pour toujours. » (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
Marie demeura avec Elisabeth environ trois mois, et s’en retourna chez elle.
57 Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
Cependant, le temps s’accomplit où Elisabeth devait enfanter, et elle mit au monde un fils.
58 Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
Ses voisins et ses parents, ayant appris que le Seigneur avait signalé en elle sa miséricorde, se réjouissaient avec elle.
59 A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
Le huitième jour, ils vinrent pour circoncire l’enfant, et ils le nommaient Zacharie d’après le nom de son père.
60 amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
Mais sa mère, prenant la parole: « Non, dit-elle, mais il s’appellera Jean. »
61 Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
Ils lui dirent: « Il n’y a personne dans votre famille qui soit appelé de ce nom. »
62 Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
Et ils demandaient par signe à son père comment il voulait qu’on le nommât.
63 Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
S’étant fait apporter une tablette, il écrivit: « Jean est son nom »; et tous furent dans l’étonnement.
64 Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
Au même instant sa bouche s’ouvrit, sa langue se délia; et il parlait, bénissant Dieu.
65 Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
La crainte s’empara de tous les habitants d’alentour, et partout dans les montagnes de la Judée, on racontait toutes ces merveilles.
66 Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
Tous ceux qui en entendirent parler les recueillirent dans leur cœur, et ils disaient: « Que sera donc cet enfant? Car la main du Seigneur était avec lui. »
67 Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
Et Zacharie, son père, fut rempli de l’Esprit-Saint, et il prophétisa, en disant:
68 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
« Béni soit le Seigneur, le Dieu d’Israël, Parce qu’il a visité et racheté son peuple.
69 Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
Et qu’il a suscité une Force pour nous sauver, Dans la maison de David, son serviteur,
70 (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
(Ainsi qu’il l’a promis par la bouche de ses saints, De ses prophètes, dès les temps anciens). (aiōn g165)
71 cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
Pour nous sauver de nos ennemis Et du pouvoir de tous ceux qui nous haïssent.
72 don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
Afin d’exercer sa miséricorde envers nos pères. Et de se souvenir de son pacte saint;
73 rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
Selon le serment qu’il fit à Abraham, notre père,
74 don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
De nous accorder que, sans crainte, Affranchis du pouvoir de nos ennemis,
75 cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
Nous le servions, avec une sainteté et une justice Dignes de ses regards, tous les jours de notre vie.
76 “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
Quant à toi, petit enfant, tu seras appelé prophète du Très-Haut, Car tu marcheras devant la face du Seigneur, Pour lui préparer les voies;
77 don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
Pour apprendre à son peuple à reconnaître le salut Dans la rémission de leurs péchés:
78 saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
Par l’effet de la tendre miséricorde de notre Dieu, Grâce à laquelle nous a visités, d’en haut, le Soleil levant,
79 don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
Pour éclairer ceux qui sont assis dans les ténèbres et l’ombre de la mort, Pour diriger nos pas dans la voie de la paix. »
80 Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.
Or l’enfant croissait et se fortifiait en esprit, et il demeura dans le désert jusqu’au jour de sa manifestation devant Israël.

< Luka 1 >