< Luka 1 >

1 Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
To his Excellency, Theophilus. Many attempts have been already made to draw up an account of those events which have reached their conclusion among us,
2 kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
just as they were reported to us by those who from the beginning were eye-witnesses, and afterward became bearers of the message.
3 Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
And, therefore, I also, since I have investigated all these events with great care from their very beginning, have resolved to write a connected history of them for you,
4 don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
in order that you may be able to satisfy yourself of the accuracy of the story which you have heard from the lips of others.
5 A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
In the reign of Herod, king of Judea, there was a priest named Zechariah, who belonged to the division called after Abijah. His wife, whose name was Elizabeth, was also a descendant of Aaron.
6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
They were both righteous people, who lived blameless lives, guiding their steps by all the commandments and ordinances of the Lord.
7 Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
But they had no child, Elizabeth being barren; and both of them were advanced in years.
8 Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
One day, when Zechariah was officiating as priest before God, during the turn of his division,
9 sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
it fell to him by lot, in accordance with the practice among the priests, to go into the Temple of the Lord and burn incense;
10 Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
and, as it was the Hour of Incense, the people were all praying outside.
11 Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
And an angel of the Lord appeared to him, standing on the right of the Altar of Incense.
12 Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
Zechariah was startled at the sight and was awe-struck.
13 Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
But the angel said to him, “Do not be afraid, Zechariah; your prayer has been heard, and your wife Elizabeth will bear you a son, whom you will call by the name John.
14 Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
He will be to you a joy and a delight; and many will rejoice over his birth.
15 gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
For he will be great in the sight of the Lord; he will not drink any wine or strong drink, and he will be filled with the Holy Spirit from the very hour of his birth,
16 Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
and will reconcile many of the Israelites to the Lord their God.
17 Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
He will go before him in the spirit and with the power of Elijah, to reconcile fathers to their children and the disobedient to the wisdom of the righteous, and so make ready for the Lord a people prepared for him.”
18 Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
“How can I be sure of this?” Zechariah asked the angel. “For I am an old man and my wife is advanced in years.”
19 Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
“I am Gabriel,” the angel answered, “who stand in the presence of God, and I have been sent to speak to you and to bring you this good news.
20 Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
And now you will be silent and unable to speak until the day when this takes place, because you did not believe what I said, though my words will be fulfilled in due course.”
21 Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
Meanwhile the people were watching for Zechariah, wondering at his remaining so long in the Temple.
22 Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
When he came out, he was unable to speak to them, and they perceived that he had seen a vision there. But Zechariah kept making signs to them, and remained dumb.
23 Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
And, as soon as his term of service was finished, he returned home.
24 Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
After this his wife, Elizabeth, became pregnant and lived in seclusion for five months.
25 Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
“The Lord has done this for me,” she said, “he has shown me kindness and taken away the public disgrace of childlessness under which I have been living.”
26 A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
Six months later the angel Gabriel was sent from God to a town in Galilee called Nazareth,
27 gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
to a maiden there who was engaged to a man named Joseph, a descendant of David. Her name was Mary.
28 Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
Gabriel came into her presence and greeted her, saying, “You have been shown great favor – the Lord is with you.”
29 Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
Mary was much disturbed at his words, and was wondering to herself what such a greeting could mean,
30 Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
when the angel spoke again, “Do not be afraid, Mary, for you have found favor with God.
31 Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
And now, you will conceive and give birth to a son, and you will give him the name Jesus.
32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
The child will be great and will be called ‘Son of the Most High,’ and the Lord God will give him the throne of his ancestor David,
33 zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
and he will reign over the descendants of Jacob for ever; And to his kingdom there will be no end.” (aiōn g165)
34 Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
“How can this be?” Mary asked the angel. “For I have no husband.”
35 Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
“The Holy Spirit will descend on you,” answered the angel, “and the Power of the Most High will overshadow you; and therefore the child will be called ‘holy,’ and ‘Son of God.’
36 ’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
And Elizabeth, your cousin, is herself also expecting a son in her old age; and it is now the sixth month with her, though she is called barren;
37 Gama ba abin da zai gagari Allah.”
for no promise from God will fail to be fulfilled.”
38 Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
“I am the servant of the Lord,” exclaimed Mary. “Let it be with me as you have said.” Then the angel left her.
39 A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
Soon after this Mary set out, and made her way quickly into the hill-country, to a town in Judah;
40 inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
and there she went into Zechariah’s house and greeted Elizabeth.
41 Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
When Elizabeth heard Mary’s greeting, the child moved within her, and Elizabeth herself was filled with the Holy Spirit,
42 Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
and cried aloud, “Blessed are you among women, and blessed is your unborn child!
43 Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
But how have I this honor, that the mother of my Lord should come to me?
44 Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
For, as soon as your greeting reached my ears, the child moved within me with delight!
45 Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
Happy indeed is she who believed that the promise which she received from the Lord would be fulfilled.”
46 Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
And Mary said: “My soul exalts the Lord,
47 ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
and my spirit delights in God my Savior,
48 gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
for he has looked with favor on his humble servant girl. From now on all generations will call me blessed!
49 gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
“For the Almighty has done great things for me, and holy is his name.
50 Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
He has mercy on those who revere him in every generation.
51 Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
“Mighty are the deeds of his arm! He has scattered the self-satisfied proud,
52 Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
he has cast down the mighty from their thrones, and he uplifts the humble,
53 Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
he has filled the hungry with good things, and the rich he has sent away empty.
54 Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
“He has stretched out his hand to his servant Israel, ever mindful of his mercy,
55 ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
as he promised to our ancestors, to Abraham and his descendants for ever.” (aiōn g165)
56 Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
Mary stayed with Elizabeth about three months, and then returned to her home.
57 Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
When Elizabeth’s time came, she gave birth to a son;
58 Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
and her neighbors and relatives, hearing of the great goodness of the Lord to her, came to share her joy.
59 A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
A week later they met to circumcise the child, and were about to call him Zechariah after his father,
60 amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
when his mother spoke up, “No, he is to be called John.”
61 Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
“You have no relation of that name!” they exclaimed;
62 Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
and they made signs to the child’s father, to find out what he wished the child to be called.
63 Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
Asking for a writing tablet, he wrote the words – ‘His name is John.’ Everyone was surprised
64 Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
and immediately Zechariah recovered his voice and the use of his tongue, and began to bless God.
65 Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
All their neighbors were awe-struck at this, and throughout the hill-country of Judea the whole story was much talked about.
66 Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
All who heard it kept it in mind, asking one another – “What can this child be destined to become?” For the Power of the Lord was with him.
67 Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
Then his father Zechariah was filled with the Holy Spirit, and, speaking under inspiration, said:
68 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
“Blessed is the Lord, the God of Israel, who has visited his people and wrought their deliverance,
69 Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
and has raised up for us the strength of our salvation in the house of his servant David –
70 (yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
as he promised by the lips of his holy prophets of old – (aiōn g165)
71 cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
salvation from our enemies and from the hands of all who hate us,
72 don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
showing mercy to our ancestors, and mindful of his sacred covenant.
73 rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
This was the oath which he swore to our ancestor Abraham –
74 don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
that we should be rescued from the hands of our enemies,
75 cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
and should serve him without fear in holiness and righteousness, in his presence all our days.
76 “Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
And you, child, will be called prophet of the Most High, for you will go before the Lord to make ready his way,
77 don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
to give his people the knowledge of salvation through the forgiveness of their sins,
78 saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
through the tender mercy of our God, whereby the dawn will break on us from heaven,
79 don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
to give light to those who live in darkness and the shadow of death, and guide our feet into the way of peace.”
80 Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.
The child grew and became strong in spirit, and he lived in the wilds until the time came for his appearance before Israel.

< Luka 1 >