< Firistoci 1 >

1 Ubangiji ya kira Musa ya yi masa magana daga cikin Tentin Sujada ya ce,
And the LORD called unto Moses, and spake unto him out of the tent of meeting, saying,
2 “Yi magana da Isra’ilawa ka ce musu, ‘Duk sa’ad da waninku ya kawo hadaya ga Ubangiji, ku kawo hadayarku ta dabba daga garkenku ta shanu ko kuwa daga tumakinku.
Speak unto the children of Israel, and say unto them, When any man of you offereth an oblation unto the LORD, ye shall offer your oblation of the cattle, [even] of the herd and of the flock.
3 “‘In hadaya ta ƙonawar daga shanu ne, sai yă miƙa namiji marar lahani. Dole yă kawo shi a ƙofar Tentin Sujada don yă zama yardajje ga Ubangiji.
If his oblation be a burnt offering of the herd, he shall offer it a male without blemish: he shall offer it at the door of the tent of meeting, that he may be accepted before the LORD.
4 Zai ɗibiya hannunsa a kan hadaya ta ƙonawar, za a kuwa karɓa a madadinsa don a yi kafara dominsa.
And he shall lay his hand upon the head of the burnt offering; and it shall be accepted for him to make atonement for him.
5 Zai yanka ɗan bijimin a gaban Ubangiji, Haruna kuwa da’ya’yansa maza firist, za su kawo jinin su kuma yafa shi a kan bagaden a kowane gefe a mashigin Tentin Sujada.
And he shall kill the bullock before the LORD: and Aaron’s sons, the priests, shall present the blood, and sprinkle the blood round about upon the altar that is at the door of the tent of meeting.
6 Zai feɗe hadaya ta ƙonawar, yă yayyanka shi gunduwa-gunduwa.
And he shall flay the burnt offering, and cut it into its pieces.
7 ’Ya’yan Haruna maza waɗanda suke firistoci za su hura wuta a bagade, su kuma shirya itace a kan wutar.
And the sons of Aaron the priest shall put fire upon the altar, and lay wood in order upon the fire:
8 Sa’an nan’ya’yan Haruna maza waɗanda suke firistoci za su shirya gunduwa-gunduwar haɗe da kan da kuma kitsen a kan itace mai cin wuta wanda yake a kan bagaden.
and Aaron’s sons, the priests, shall lay the pieces, the head, and the fat, in order upon the wood that is on the fire which is upon the altar:
9 Zai wanke kayan cikin da kuma ƙafafun da ruwa, firist ɗin kuwa zai ƙone dukan waɗannan a kan bagade. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
but its inwards and its legs shall he wash with water: and the priest shall burn the whole on the altar, for a burnt offering, an offering made by fire, of a sweet savour unto the LORD.
10 “‘In hadaya ta ƙonawar daga garke ne, ko na tumaki, ko na awaki, zai miƙa namiji ne marar lahani.
And if his oblation be of the flock, of the sheep, or of the goats, for a burnt offering; he shall offer it a male without blemish.
11 Zai yanka shi a gefen arewa na bagaden a gaban Ubangiji,’ya’yan Haruna firistoci kuwa za su yayyafa jinin dabbar a bagaden a kowane gefe.
And he shall kill it on the side of the altar northward before the LORD: and Aaron’s sons, the priests, shall sprinkle its blood upon the altar round about.
12 Zai yanka shi gunduwa-gunduwa, firist kuwa zai shirya su haɗe da kan, da kuma kitsen a kan itace mai cin wutar da yake a kan bagade.
And he shall cut it into its pieces, with its head and its fat: and the priest shall lay them in order on the wood that is on the fire which is upon the altar:
13 Zai wanke kayan cikin da kuma ƙafafun da ruwa, firist ɗin kuwa zai ƙone dukan waɗannan a kan bagade. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
but the inwards and the legs shall he wash with water: and the priest shall offer the whole, and burn it upon the altar: it is a burnt offering, an offering made by fire, of a sweet savour unto the LORD.
14 “‘In hadaya ga Ubangiji ɗin, hadaya ta ƙonawa ta tsuntsaye ce, zai miƙa kurciya ko’yar tattabara.
And if his oblation to the LORD be a burnt offering of fowls, then he shall offer his oblation of turtledoves, or of young pigeons.
15 Firist zai kawo ta bagade, yă murɗe wuyan tsuntsun yă ƙone shi a kan bagade; zai tsiyaye jininsa tsuntsun a gefen bagaden.
And the priest shall bring it unto the altar, and wring off its head, and burn it on the altar; and the blood thereof shall be drained out on the side of the altar:
16 Amma zai ɗauki kayan cikin tsuntsun da gashin yă zubar da su a gefen bagaden a wajen gabas a wurin zuba toka.
and he shall take away its crop with the filth thereof, and cast it beside the altar on the east part, in the place of the ashes:
17 Zai tsaga shi biyu a tsaka, amma ba zai raba shi ba. Firist ɗin zai ɗibiya shi a bisa itacen da yake bisa bagaden, yă ƙone shi. Hadaya ce ta ƙonawa, hadaya ce kuma wadda aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.
and he shall rend it by the wings thereof, [but] shall not divide it asunder: and the priest shall burn it upon the altar, upon the wood that is upon the fire: it is a burnt offering, an offering made by fire, of a sweet savour unto the LORD.

< Firistoci 1 >