< Firistoci 22 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa,
OLELO mai la hoi o Iehova ia Mose, i mai la,
2 “Faɗa wa Haruna da’ya’yansa maza, su lura da tsarkakakkun abubuwan da Isra’ilawa suka keɓe gare ni da bangirma, saboda ba za su ƙazantar da sunana mai tsarki ba. Ni ne Ubangiji.
E olelo aku ia Aarona, a i kana mau keiki, e hookaawale lakou ia lakou iho mai na mea hoano o na mamo a Iseraela, i ole ai lakou e hoino mai i ko'u inoa hoano i na mea a lakou i hoano mai ai no'u; owau no Iehova.
3 “Faɗa musu cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, in wani zuriyarku ya ƙazantu, duk da haka ya kusaci tsarkakakku hadayun da Isra’ilawa suka keɓe ga Ubangiji, dole a raba wannan mutum daga gabana. Ni ne Ubangiji.
E olelo aku ia lakou, O ka mea o ka oukou mau keiki a pau iwaena o ko oukou mau hanauna, e hele i na mea hoano a na mamo a Iseraela i hoolaa aku ai ia Iehova, me kona haumia maluna ona, e okiia'ku oia mai ko'u alo aku: owau no Iehova.
4 “‘In zuriyar Haruna yana da kuturu, ko mai ɗiga, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa ba, sai lokacin da ya tsarkaka. Duk wanda ya taɓa wani abu marar tsarki na mamaci, ko wanda maniyyinsa yake ɗiga,
O kela kanaka, keia kanaka he keiki a Aarona, he lepero, a he hilo kahe kona; aole ia e ai i na mea hoano a hiki i kona maemae ana. A o ke kanaka hoopa aku i ka mea haumia no ka mea make, a o ke kanaka ua hele aku kona anoano mai ona aku;
5 da duk kuma wanda ya taɓa wani abu mai rarrafe wanda yake ƙazantarwa, ko kuwa wani mutum mai ƙazanta,
A o ke kanaka hoopa aku i ka mea kolo e haumia ai, a i ke kanaka paha e haumia ai, o kela haumia keia haumia kona;
6 duk mutumin da ya taɓa kowane irin abu haka, zai ƙazantu har yamma, ba kuwa zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwan nan ba, sai ya yi wanka tukuna.
O ke kanaka i pa aku i kekahi o ia mau mea, e haumia no ia a hiki i ke ahiahi, aole ia e ai i na mea hoano, ke holoi ole oia i kona io i ka wai.
7 Sa’ad da rana ta fāɗi, zai zama tsarkakakke, bayan wannan kuwa zai iya cin tsarkakakkun hadayu, gama abincinsa ne.
A napoo ka la, e maemae no ia, a mahope iho e ai no oia i na mea hoano; no ka mea, o kana ai no ia.
8 Kada yă ci wani abin da ya mutu mushe, ko wanda namun jeji suka yayyaga, don kada yă ƙazantar da kansa. Ni ne Ubangiji.
O ka mea make wale, a o ka mea i nahaeia, aole oia e ai ia, e hoohauraia'i ia ia iho: owau no Iehova.
9 “‘Firistoci za su kiyaye umarnaina don kada su yi laifi su mutu saboda sun rena su. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da su masu tsarki.
E malama hoi lakou i ka'u oihana, o hooili lakou i ka hewa maluna ona, a make, ke hoohaumia Iakou ia mea: na'u ua Iehova lakou e hoano nei.
10 “‘Duk wanda ba daga cikin iyalin firistoci ba, ko da yake yana zama tare da su, ko kuwa an ɗauke shi yana yin musu aiki, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun hadayun ba.
Aole e ai ka malihini i ka mea hoano; o ko ke kahuna mea e noho malihini mai, a o ke kauwa hoolimalima, aole no e ai i ka mea hoano.
11 Amma in firist ya sayi bawa da kuɗi, ko kuwa in an haifi bawan a gidansa, wannan bawan zai iya cin tsattsarkan abincin.
Aka ina e kuai ke kahuna i ke kanaka me kana kala, e ai no oia ia, a me ka mea i hanau maloko o kona hale; o lakou ke ai i kana ai.
12 In’yar firist ta auri wani da ba firist ba, ba za tă ci wani tsarkakakkun sadaka ba.
Ina e mare ke kaikamahine a ke kahuna i ka malihini, aole oia e ai i ka alana o na mea hoano.
13 Amma idan’yar firist ta zama gwauruwa ko sakakkiya, ba ta da’ya’ya, ta kuwa dawo don tă zauna a gidan mahaifinta kamar matashiya, za tă iya cin abincin.
Aka ina he wahinekanemake ke kaikamahine a ke kahuna, a ua hemo paha me ke keiki ole, a ua hoi mai i ka hale o kona makuakane, e like me kona wa kamalii, e ai no oia i ka ai a kona makuakane; aka aole ka malihini e ai ia mea.
14 “‘In wani ya ci tsarkakakken abinci cikin kuskure, dole yă maido wa firist hadayar, yă kuma ƙara kashi ɗaya bisa biyar na tamanin abin.
A ina e ai ke kanaka i ka mea hoano, me ka ike ole, alaila e hui aku oia i ka hapa lima me ia, a e haawi aku i ke kahuna me ka mea hoano.
15 Firist ɗin ba zai ƙasƙantar da tsarkakakkun hadayun da Isra’ilawa suka kawo ga Ubangiji
Aole lakou e hoohaumia i ka na mamo a Iseraela mau mea hoano a lakou i hoolaa ai ia Iehova:
16 ta wurin barinsu su ci tsarkakakkun hadayu, ta yin haka su jawo wa kansu laifin da zai bukaci biya ba. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.’”
Aole hoi e waiho aku maluna o lakou i ka hewa o ka lawehala ana, i ka lakou ai ana i na mea hoano; no ka mea, na'u na Iehova lakou e hoano nei.
17 Ubangiji ya ce wa Musa,
Olelo mai la hoi o Iehova ia Mose, penei,
18 “Yi wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa magana ka ce musu, ‘In waninku, ko mutumin Isra’ila, ko baƙon da yake zama a Isra’ila, ya kawo kyauta don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko don yă cika alkawari, ko kuwa a matsayin hadaya ta yardar rai,
E olelo aku oe ia Aarona, a i kana mau keiki, a i na mamo a pau a Iseraela, a e i aku ia lakou, O kela kanaka keia kanaka o ka ohana o Iseraela, a o na malihini iloko o ka Iseraela, nana e kaumaha i kona mohai no kona hoohiki ana a pau, a no kana mau alana na kona makemake, ka mea a lakou e kaumaha'i ia Iehova, imohaikuni:
19 dole ku miƙa dabba namiji marar lahani, daga shanu, tumaki, ko awaki, domin yă zama yardajje a madadinku.
Na ko oukou makemake iho, i ke kane kina ole o na bipi, o na hipa, a o na kao.
20 Kada ku kawo wani abu mai lahani, domin ba zai zama yardajje ba a madadinku.
O ka mea kina, aole oukou e kaumaha ia; no ka mea, aole ia e maliuia no oukou.
21 Sa’ad da wani ya kawo hadaya ta salama daga garken shanu, ko na tumaki, ga Ubangiji don yă cika wani alkawari na musamman, ko hadaya ta yardar rai, dole yă zama marar lahani, ko tabo, don yă zama yardajje.
A o ke kanaka nana e kaumaha i ka alana o na mahaihoomalu ia Iehova, e hooko ai i kana i hoohiki ai, a ina he mohai na kona makemake, o na bipi, a o na hipa paha, e hemolele ia e maliuia'i: aole aku kina iloko ona.
22 Kada ku miƙa wa Ubangiji dabbobi makafi, ko naƙasassu, ko masu gundumi, ko masu ɗiga, ko masu susa, ko masu kirci. Kada ku sa wani daga cikin waɗannan a bisa bagade a matsayin hadaya, gama hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
O ka makapaa, o ka oopa, a he puu kona, he puupuu, he kakio, aole oukou e kaumaha ia mau mea ia Iehova, aole hoi e hoolilo ia mau mea i mohai e kaumahaia ma ke ahi maluna o ke kuahu ia Iehova.
23 Za ku iya miƙa hadaya ta yardar rai da maraƙi, ko tunkiya mai naƙasa, ko marar cikakken lafiya, amma ba za tă zama yardajje don cika alkawarin da aka yi ba.
O ka bipikane, a o ka hipakeiki, he oi aku ko ka lala ona, he hemahema paha, e hiki no ke kaumaha oe ia i mohai na kou makemake no; aka no ka hoohiki ana aole e maliuia'ku ia.
24 Ba za ku miƙa wa Ubangiji dabbar da lunsayinta yake da ƙujewa, ko dandaƙewa, ko yagewa, ko yankewa ba.
O ka mea i pepeia, a i paopaoia, a uhaeia, a i poaia, aole oukou e kaumaha ia mea ia Iehova, aole oukou e hana ma ko oukou aina.
25 Ba za ku kuma karɓi irin waɗannan dabbobi daga hannun baƙi ku miƙa su a matsayin abinci ga Allahnku ba. Ba za su zama yardajje a madadinku ba, domin sun naƙasa, suna kuma da lahani.’”
Aole hoi noloko mai a ko ka malihini lima, e kaumaha ai oukou i ka berena a ko oukou Akua, no keia mau mea; no ka mea, iloko o lakou ko lakou popopo, he mau kina iloko o lakou; aole e maliuia no oukou.
26 Ubangiji ya ce wa Musa,
Olelo mai la hoi o Iehova ia Mose, i mai la,
27 “Sa’ad da aka haifi ɗan maraƙi, tunkiya, ko akuya, sai yă kasance da mahaifiyarsa kwana bakwai. Daga rana ta takwas zuwa gaba, zai zama yardajje hadaya, hadaya ce da aka ƙone da wuta ga Ubangiji.
Aia hanau ka bipikane, a he hipa paha, a he kao paha, alaila e noho ia malalo iho o ka makua, i na la ehiku; a mai ka walu o ka la, a mahope aku e maliuia'i ia i mohai puhi no Iehova.
28 Kada a yanka saniya, ko tunkiya da ɗanta rana ɗaya.
Ina he bipiwahine, a he hipawahine paha, aole oukou e pepehi pu ia mea me kana keiki i ka la hookahi.
29 “Sa’ad da kuka miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, ku miƙa ta a yadda za tă zama yardajje a madadinku.
Aia kaumaha aku oukou i ka mohai aloha ia Iehova, e kaumaha oukou ia ua ko oukou makemake no.
30 Dole a ci hadayar a ranar; kada a bar saura sai da safe. Ni ne Ubangiji.
Ia la hookahi no, e aiia ia, aole e hookoe oukou i kauwahi ona a ao ae: owau no Iehova.
31 “Ku kiyaye dokokina, ku kuma bi su. Ni ne Ubangiji.
Nolaila e malama oukou i ka'u mau kauoha, a e hana ma ia mau mea: owau no Iehova.
32 Kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Dole Isra’ilawa su gane Ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji, wanda ya keɓe ku a matsayin tsarkaka
Aole hoi oukou e hoino i ko'u inoa hoano; e hoanoia no wau iwaena o na mamo a Iseraela; owau no Iehova nana oukou e hoano nei,
33 da kuma wanda ya fitar da ku daga Masar don in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”
Nana hoi oukoa i lawe mai mai ka aina o Aigupita mai i Akua au no oukou: owau no Iehova.

< Firistoci 22 >