< Firistoci 21 >

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Yi magana da firistoci,’ya’yan Haruna maza, ka ce musu, ‘Kada firist yă ƙazantar da kansa saboda wani cikin mutanensa da suka mutu,
The Lord also said to Moses: Speak to the priests, the sons of Aaron, and you shall say to them: Do not allow a priest to be contaminated by the death of his citizens,
2 sai dai na danginsa na kusa, kamar mahaifiyarsa ko mahaifinsa, ɗansa ko’yarsa, ɗan’uwansa,
except only by his blood-relatives and near-relatives, that is, by a father or mother, or by a son or daughter, or also a brother,
3 ko’yar’uwarsa da ba tă riga ta yi aure ba, wadda take dogara gare shi, da yake ba ta da miji, saboda ita zai iya ƙazantar da kansa.
or a virgin sister, who is not married to a husband.
4 Kada yă ƙazantar da kansa saboda mutanen da suke da dangantakar da shi ta wurin aure, ta yin haka zai ƙazantar da kansa.
But not even by the leader of his people shall he be contaminated.
5 “‘Kada firistoci su aske kansu ƙwal ko su kwakkwafe gemunsu, ko su tsattsage jikunansu.
Neither shall they shave their head or their beard, and they shall not make incisions in their flesh.
6 Dole su kasance masu tsarki ga Allahnsu, kada kuma su ɓata sunan Allahnsu. Domin sukan miƙa hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta, abincin Allahnsu, saboda haka sai su kasance da tsarki.
They shall be holy to their God, and they shall not pollute his name. For they offer the incense of the Lord and the bread of their God, and because of this they shall be holy.
7 “‘Ba za su auri matan da karuwanci ya ɓata su, ko waɗanda mazansu suka sake su ba, gama firistoci masu tsarki ne ga Allahnsu.
They shall not take as a wife a promiscuous woman, or a prostitute, or her who has been repudiated by her husband. For they are consecrated to their God,
8 An ɗauke su da tsarki, domin suna miƙa abincin Allahnku. An ɗauka su masu tsarki gama Ni Ubangiji, mai tsarki ne, Ni wanda ya mai da ku masu tsarki.
and they offer the bread of the presence. Therefore, let them be holy, for I also am holy: the Lord, who sanctifies them.
9 “‘In’yar firist ta ɓata kanta ta wurin zama karuwa, ta kunyatar da mahaifinta ke nan; dole a ƙone ta da wuta.
If the daughter of a priest will have been taken into prostitution, and will have violated the name of her father, she shall be consumed by fire.
10 “‘Babban firist, wanda yake ɗaya cikin’yan’uwansa wanda aka shafe da mai a kansa, wanda kuma aka naɗa don yă sa rigunan firistoci, kada yă bar gashin kansa buzu-buzu, ko ya kyakketa rigunansa.
The high priest, that is, the priest who is the greatest among his brothers, upon whose head the oil of anointing has been poured, and whose hands have been consecrated for the priesthood, and who has been vested with the holy vestments: he shall not expose his head; he shall not rend his vestments.
11 Ba zai shiga inda akwai gawa ba. Kada yă ƙazantar da kansa, ko ma ta mahaifinsa ce ko ta mahaifiyarsa.
And he shall not enter to any dead body whatsoever; likewise, not even by his father or mother shall he be contaminated.
12 An keɓe shi domina, kada yă ƙazantar da kansa, kada kuwa yă ɓata Tentin Sujada ta wurin shiga gidan da gawa take, ko ta mahaifinsa, ko ta mahaifiyarsa ce. Ni ne Ubangiji.
Neither shall he exit from the holy places, lest he pollute the Sanctuary of the Lord. For the oil of the holy anointing of his God is upon him. I am the Lord.
13 “‘Dole macen da zai aura ta kasance budurwa.
He shall take a virgin as his wife.
14 Ba zai auri matan da mijinta ya mutu, ko macen da mijinta ya rabu da ita, ko macen da ta ɓata kanta ta wurin karuwanci ba, sai dai yă auri budurwa daga cikin mutanensa,
But a widow, or one who has been repudiated or defiled, or also a mistress, he shall not accept, but only a maiden from among his own people.
15 don kada yă ƙazantar da’ya’yansa a cikin mutanensa. Ni ne Ubangiji, wanda ya mai da shi mai tsarki.’”
He shall not mingle the stock of his family with the common people of his nation. For I am the Lord, who sanctifies him.
16 Ubangiji ya ce wa Musa,
And the Lord spoke to Moses, saying:
17 “Faɗa wa Haruna cewa, ‘Don tsararraki masu zuwa, kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani yă zo kusa domin yă miƙa hadaya ta ci gare ni.
Say to Aaron: A man from your offspring, throughout their families, who has a blemish, shall not offer the bread to his God.
18 Duk mai lahani, ko makaho, ko gurgu, ko mai naƙasa, ko mai wani lahani a jiki;
Neither shall he approach to minister to him: if he is blind, if he is lame, if he is small, or large, or has a crooked nose,
19 ko mai karyayyen ƙafa, ko mai karyayyen hannu,
if his foot or hand is broken,
20 ko mai ƙusumbi, ko wada, ko wanda yake da lahani a ido, ko mai cuta mai sa ƙaiƙayi, ko mai kirci, ko wanda aka daƙe, ba zai yi kusa domin yă miƙa hadaya ba.
if he has a bulging back or bleary eyes, or if he has a white spot in his eye, or a chronic scab, or a skin disease on his body, or a hernia.
21 Ba zuriyar Haruna firist, mai lahanin da zai zo kusa don yă miƙa hadayun da aka yi ga Ubangiji da wuta. Da yake yana da lahani, ba zai zo kusa don yă miƙa abincin Allahnsa ba.
Anyone from the offspring of Aaron, the priest, who has a blemish, shall not approach to offer sacrifices to the Lord, nor the bread to his God.
22 Zai iya cin abinci mafi tsarki na Allahnsa, haka ma abinci mai tsarki;
Nevertheless, he shall eat from the loaves which are offered in the Sanctuary.
23 duk da haka saboda lahaninsa, ba zai yi kusa da labule, ko yă yi kusa da bagade don kada yă ƙazantar da wuri mai tsarkina. Ni ne Ubangiji wanda yake mai da su masu tsarki.’”
But even so, he may not enter within the veil, nor approach to the altar. For he has a blemish, and he must not contaminate my Sanctuary. I am the Lord, who sanctifies them.
24 Sai Musa ya faɗa wannan wa Haruna da’ya’yansa maza da kuma dukan Isra’ilawa.
Therefore, Moses spoke to Aaron, and to his sons, and to all of Israel, everything that had been commanded to him.

< Firistoci 21 >