< Firistoci 10 >

1 ’Ya’yan Haruna maza, Nadab da Abihu suka ɗauki farantansu, suka sa wuta a ciki, suka zuba turare a kai; suka kuma miƙa haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji, ba irin wadda Ubangiji ya umarta ba.
Men Arons sønner Nadab og Abihu tok hver sitt ildkar og la ild i dem og la røkelse på ilden og bar fremmed ild inn for Herrens åsyn, som han ikke hadde befalt dem.
2 Sai wuta ta fito daga Ubangiji ta cinye su, suka kuma mutu a gaban Ubangiji.
Da gikk det ild ut fra Herrens åsyn og fortærte dem, og de døde for Herrens åsyn.
3 Sai Musa ya ce Haruna, “Ga abin da Ubangiji yake nufi sa’ad da ya ce, “‘A cikin waɗanda suka kusace ni za a tabbata ni mai tsarki ne; a fuskar dukan mutane za a kuwa girmama ni.’” Haruna ya yi shiru.
Da sa Moses til Aron: Dette var det Herren talte om da han sa: På dem som står mig nær, vil jeg åpenbare min hellighet, og for alt folkets åsyn vil jeg forherlige mig. Og Aron tidde.
4 Sai Musa ya kira Mishayel da Elzafan,’ya’yan Uzziyel kawun Haruna, ya ce musu, “Ku zo nan; ku ɗauki’yan’uwanku waje da sansani, daga gaban wuri mai tsarki.”
Men Moses kalte på Misael og Elsafan, sønner av Arons farbror Ussiel, og sa til dem: Tred frem og bær eders brødre bort fra helligdommen og utenfor leiren!
5 Sai suka zo suka ɗauke su, suna nan cikin taguwoyinsu, zuwa waje da sansani yadda Musa ya umarta.
Og de trådte frem og bar dem i deres kjortler utenfor leiren, som Moses hadde sagt.
6 Sa’an nan Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza, “Kada ku bar gashin kanku barkatai, kada kuma ku yage tufafinku, don kada ku mutu. Yin haka zai jawo fushin Ubangiji a kan dukan jama’a. Amma dangoginku, wato, dukan Isra’ilawa, suna iya kuka saboda waɗanda Ubangiji ya hallaka da wuta.
Da sa Moses til Aron og hans sønner Eleasar og Itamar: I skal ikke rake eders hoder og ikke sønderrive eders klær, forat I ikke skal dø, og forat han ikke skal vredes på hele menigheten; men eders brødre, hele Israels hus, skal gråte over denne brand som Herren har optendt.
7 Kada ku bar ƙofar Tentin Sujada ko kuwa ku mutu, domin man Shafan Ubangiji yana kanku.” Saboda haka suka yi kamar yadda Musa ya faɗa.
Og I skal ikke gå bort fra inngangen til sammenkomstens telt, forat I ikke skal dø; for Herrens salvings-olje er på eder. Og de gjorde som Moses sa.
8 Sa’an nan Ubangiji ya yi magana da Haruna ya ce,
Og Herren talte til Aron og sa:
9 “Kai da’ya’yanka maza, ba za ku sha ruwan inabi ko wani abu mai sa jiri ba a duk sa’ad da za ku shiga cikin Tentin Sujada, in ba haka ba za ku mutu. Wannan dawwammamiyar farilla ce wa tsararraki masu zuwa.
Vin eller sterk drikk skal hverken du eller dine sønner drikke når I går inn i sammenkomstens telt, forat I ikke skal dø - det skal være en evig lov for eder, fra slekt til slekt -
10 Dole ku bambanta tsakanin mai tsarki da marar tsarki, tsakanin marar tsabta da mai tsabta,
så I kan gjøre forskjell mellem hellig og vanhellig, mellem urent og rent,
11 za ku kuma koyar da Isra’ilawa dukan farillan da Ubangiji ya ba su ta wurin Musa.”
og lære Israels barn alle de lover som Herren har kunngjort dem ved Moses.
12 Musa ya ce wa Haruna da Eleyazar da Itamar’ya’yansa maza da suka ragu, “Ku ɗauki ragowar hadaya ta gari wadda aka yi hadaya ta ƙonawa da ita ga Ubangiji ku ci ba tare da yisti ba, a gefen bagaden, gama tsattsarka ne.
Så sa Moses til Aron og hans sønner Eleasar og Itamar, som ennu var i live: Ta det matoffer som er tilovers av Herrens ildoffer, og et det usyret ved siden av alteret; for det er høihellig.
13 Ku ci shi a tsattsarkan wuri, gama rabonka ne da na’ya’yanka daga cikin hadayun da akan ƙone da wuta ga Ubangiji; gama haka aka umarce ni.
I skal ete det på et hellig sted, for det er din og dine sønners fastsatte del av Herrens ildoffer; således er det mig befalt.
14 Amma kai da’ya’yanka maza da mata za su iya ci ƙirjin da aka kaɗa, da kuma cinyar da aka miƙa. Ku ci su a wuri mai tsabta; an ba da su gare ku da kuma’ya’yanku a matsayin rabo daga hadaya ta salama ta Isra’ilawa.
Og svinge-brystet og løfte-låret skal I ete på et rent sted, du og dine sønner og dine døtre med dig; for det er gitt dig og dine barn som eders fastsatte del av Israels barns takkoffer.
15 Cinyar da aka miƙa da kuma ƙirjin da aka kaɗa, dole a kawo su tare da ɓangarori kitsen hadayun da aka yi ta wuri wuta, don a kaɗa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa. Wannan zai zama na kullayaumi gare ka da’ya’yanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
Løfte-låret og svinge-brystet skal de bære frem sammen med ildofferfettstykkene og svinge dem for Herrens åsyn; og det skal være din og dine barns fastsatte del til evig tid, således som Herren har befalt.
16 Sa’ad da Musa ya nemi sani game da akuyar hadaya don zunubi, ya kuwa gane cewa an ƙone shi, sai ya yi fushi da Eleyazar da kuma Itamar,’ya’yan Haruna maza da suka ragu, ya kuma yi tambaya,
Da nu Moses spurte efter syndoffer-bukken, viste det sig at den var opbrent; da blev han vred på Eleasar og Itamar, Arons sønner som ennu var i live, og han sa:
17 “Me ya sa ba ku ci hadaya don zunubi a cikin wuri mai tsarki ba? Mafi tsaki ne; an ba ku ne don a ɗauke laifin jama’a ta wurin yin kafara saboda su a gaban Ubangiji.
Hvorfor har I ikke ett syndofferet på det hellige sted? Det er jo høihellig, og han har gitt eder det forat I skal bortta menighetens syndeskyld og gjøre soning for dem for Herrens åsyn.
18 Da yake ba a kai jininsa cikin wuri mai tsarki ba, ya kamata ku ci akuyar a wuri mai tsarki, kamar yadda na umarta.”
Blodet blev jo ikke båret inn i helligdommen; derfor skulde I ha ett kjøttet på det hellige sted, således som jeg har befalt.
19 Sai Haruna ya amsa wa Musa, “Yau sun miƙa hadayarsu don zunubi da kuma hadayarsu ta ƙonawa a gaban Ubangiji, ga kuma irin waɗannan abubuwa da suka same ni, da a ce na ci hadaya don zunubi yau, da zai yi kyau ke nan a gaban Ubangiji?”
Da sa Aron til Moses: De har jo idag ofret sitt syndoffer og sitt brennoffer for Herrens åsyn, og enda er slik en ulykke hendt mig. Om jeg nu hadde ett syndoffer idag, skulde da det ha vært godt i Herrens øine?
20 Da Musa ya ji haka, sai ya gamsu.
Da Moses hørte dette, syntes han det var rett.

< Firistoci 10 >