< Makoki 5 >

1 Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
Remember, Yahweh, what has come on us. Look, and see our reproach.
2 An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
Our inheritance has been turned over to strangers, our houses to aliens.
3 Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
We are orphans and fatherless. Our mothers are as widows.
4 Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
We must pay for water to drink. Our wood is sold to us.
5 Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
Our pursuers are on our necks. We are weary, and have no rest.
6 Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
We have given our hands to the Egyptians, and to the Assyrians, to be satisfied with bread.
7 Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
Our fathers sinned, and are no more. We have borne their iniquities.
8 Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
Servants rule over us. There is no one to deliver us out of their hand.
9 Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
We get our bread at the peril of our lives, because of the sword in the wilderness.
10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
Our skin is black like an oven, because of the burning heat of famine.
11 An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
They ravished the women in Zion, the virgins in the cities of Judah.
12 An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
Princes were hanged up by their hands. The faces of elders were not honored.
13 Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
The young men carry millstones. The children stumbled under loads of wood.
14 Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
The elders have ceased from the gate, and the young men from their music.
15 Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
The joy of our heart has ceased. Our dance is turned into mourning.
16 Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
The crown has fallen from our head. Woe to us, for we have sinned!
17 Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
For this our heart is faint. For these things our eyes are dim:
18 gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
for the mountain of Zion, which is desolate. The foxes walk on it.
19 Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
You, Yahweh, remain forever. Your throne is from generation to generation.
20 Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
Why do you forget us forever, and forsake us for so long a time?
21 Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
Turn us to yourself, Yahweh, and we will be turned. Renew our days as of old.
22 sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.
But you have utterly rejected us. You are very angry against us.

< Makoki 5 >