< Makoki 4 >

1 Zinariya ta rasa kyanta, hasken zinariya ya dushe! An warwatsar da tsarkakakkun duwatsu masu daraja a kan tituna.
How is the gold become dim! [how] is the most pure gold changed! the stones of the sanctuary are poured out at the top of every street.
2 Dubi samarin Sihiyona masu daraja, waɗanda a dā darajarsu ta isa nauyin zinariya, yanzu ana ɗaukar su a matsayin tukwanen ƙasa, aikin maginin tukwane!
The precious sons of Zion, comparable to fine gold, how are they esteemed as earthen pitchers, the work of the hands of the potter!
3 Ko diloli suna ba’ya’yansu nono su sha, amma mutanena sun zama marasa zuciya kamar jiminai a cikin jeji.
Even the jackals draw out the breast, they give suck to their young ones: the daughter of my people is become cruel, like the ostriches in the wilderness.
4 Domin ƙishirwa harshen jarirai ya manne a rufin bakinsu; yaran suna roƙo a ba su burodi, amma ba wanda ya ba su.
The tongue of the sucking child cleaveth to the roof of his mouth for thirst: the young children ask bread, and no man breaketh it unto them.
5 Waɗanda a dā sukan ci abinci mai daɗi yanzu su ne masu bara a tituna. Waɗanda a dā suke sa kaya masu kyau yanzu suna kwance a kan tarin toka.
They that did feed delicately are desolate in the streets: they that were brought up in scarlet embrace dung-hills.
6 Horon mutanena ya fi na Sodom girma, wadda aka hallaka farat ɗaya ba wani hannu da ya juya ya taimake ta.
For the iniquity of the daughter of my people is greater than the sin of Sodom, that was overthrown as in a moment, and no hands were laid upon her.
7 ’Ya’yan sarakunansu sun fi ƙanƙara haske sun kuma fi madara fari, jikunansu sun fi murjani ja, kyansu kamar shuɗin yakutu.
Her nobles were purer than snow, they were whiter than milk, they were more ruddy in body than rubies, their polishing was as of sapphire:
8 Amma yanzu sun fi dare duhu; ba a iya gane su a tituna. Fatar jikinsu ta manne da ƙasusuwansu; sun bushe kamar itace.
Their visage is blacker than a coal; they are not known in the streets: their skin cleaveth to their bones; it is withered, it is become like a stick.
9 Gara waɗanda aka kashe su da takobi da waɗanda suke mutuwa da yunwa; sun rame domin rashin abinci a gona.
They that be slain with the sword are better than they that be slain with hunger; for these pine away, stricken through, for want of the fruits of the field.
10 Da hannuwansu mata masu tausayi sun dafa yaransu, suka zama masu abinci sa’ad da aka hallaka mutanena.
The hands of the pitiful women have sodden their own children; they were their meat in the destruction of the daughter of my people.
11 Ubangiji ya saki fushinsa; ya zuba zafin fushinsa. Ya hura wuta a Sihiyona ta kuma cinye harsashin gininta.
The LORD hath accomplished his fury, he hath poured out his fierce anger; and he hath kindled a fire in Zion, which hath devoured the foundations thereof.
12 Sarakunan duniya ba su gaskata ba, haka ma mutanen duniya, cewa magabta da maƙiya za su iya shiga ƙofofin Urushalima.
The kings of the earth believed not, neither all the inhabitants of the world, that the adversary and the enemy should enter into the gates of Jerusalem.
13 Amma ya faru domin zunuban annabawanta da muguntar firistocinta, waɗanda suka zub da jinin masu adalci a cikinsu.
[It is] because of the sins of her prophets, [and] the iniquities of her priests, that have shed the blood of the just in the midst of her.
14 Yanzu suna yawo barkatai a tituna kamar makafi. Sun ƙazantu da jini yadda ba wanda zai kuskura ya taɓa rigunansu.
They wander as blind men in the streets, that are polluted with blood, so that men cannot touch their garments.
15 “Ku tafi! Ba ku da tsabta!” Haka mutane suke ihu suke ce musu. “Ku tashi daga nan! Ku tashi daga nan! Kada ku taɓa mu!” Sa’ad da suka gudu suna yawo, mutanen waɗansu ƙasashe suka ce, “Ba za su ci gaba da zama a nan ba.”
Depart ye, they cried unto them, Unclean! depart, depart, touch not: when they fled away and wandered, men said among the nations, They shall no more sojourn [here].
16 Ubangiji kansa ya warwatsa su; ya daina duban su. Ba a ba firistoci girma, ba su ba dattawa gata.
The anger of the LORD hath divided them; he will no more regard them: they respected not the persons of the priests, they favoured not the elders.
17 Idanunmu sun gaji, suna ta dubawa ko taimako zai zo; mu sa ido ko za mu ga ƙasar da za tă iya taimakon mu.
Our eyes do yet fail [in looking] for our vain help; in our watching we have watched for a nation that could not save.
18 Ana bin sawunmu, ba za mu iya tafiya kan tituna ba. Ƙarshenmu ya kusa, kwanakinmu sun ƙare, gama ƙarshenmu ya zo.
They hunt our steps, that we cannot go in our streets: our end is near, our days are fulfilled; for our end is come.
19 Masu fafarar mu sun fi gaggafa mai firiya a sararin sama sauri; sun fafare mu a kan duwatsu suna fakon mu a jeji.
Our pursuers were swifter than the eagles of the heaven: they chased us upon the mountains, they laid wait for us in the wilderness.
20 Shafaffe na Ubangiji, numfashin ranmu, ya fāɗi cikin tarkonsu. Muna tunani cewa za mu iya rayuwa cikin sauran mutane a ƙarƙashin inuwarsa.
The breath of our nostrils, the anointed of the LORD, was taken in their pits; of whom we said, Under his shadow we shall live among the nations.
21 Ku yi murna da farin ciki, ya Diyar Edom, ke mai zama a ƙasar Uz. Amma ke ma za a ba ki kwaf; za ki bugu ki zama tsirara.
Rejoice and be glad, O daughter of Edom, that dwellest in the land of Uz: the cup shall pass through unto thee also; thou shalt be drunken, and shalt make thyself naked.
22 Ya Diyar Sihiyona, hukuncinki zai ƙare; ba zai sa zaman bautarki yă yi tsayi ba. Amma ya Diyar Edom, zai hukunta zunubinki yă tona tsiraicinki.
The punishment of thine iniquity is accomplished, O daughter of Zion; he will no more carry thee away into captivity: he will visit thine iniquity, O daughter of Edom; he will discover thy sins.

< Makoki 4 >