< Makoki 3 >

1 Ni ne mutumin da ya ga azaba ta wurin bulalar fushin Ubangiji.
Aleph. I am the man that see my poverty by the rod of his indignation.
2 Ya kore ni, ya sa na yi tafiya a cikin duhu maimakon a cikin haske;
Aleph. He hath led me, and brought me into darkness, and not into light.
3 ba shakka, ya juya mini baya, yana gāba da ni sau da sau, dukan yini.
Aleph. Only against me he hath turned, and turned again his hand all the day.
4 Ya sa fatar jikina da naman jikina sun tsufa ya kuma karya ƙasusuwana.
Beth. My skin and my flesh he hath made old, he hath broken my bones.
5 Ya yi mini kwanton ɓauna ya kuma kewaye ni da baƙin ciki da kuma wahala.
Beth. He hath built round about me, and he hath compassed me with gall and labour.
6 Ya sa na zauna a cikin duhu kamar waɗanda suka mutu da jimawa.
Beth. He hath set me in dark places as those that are dead for ever.
7 Ya kewaye ni yadda ba zan iya gudu ba; Ya daure ni da sarƙa mai nauyi.
Ghimel. He hath built against me round about, that I may not get out: he hath made my fetters heavy.
8 Ko lokacin da nake kira don neman taimako, ba ya jin addu’ata.
Ghimel. Yea, and when I cry, and entreat, he hath shut out my prayer.
9 Ya tare hanyata da tubula na duwatsu; ya sa hanyata ta karkace.
Ghimel. He hath shut up my ways with square stones, he hath turned my paths upside down.
10 Kamar beyar da take a laɓe tana jira, kamar zaki a ɓoye,
Daleth. He is become to me as a bear lying in wait: as a lion in secret places.
11 ya janye ni daga kan hanya ya ɓatar da ni ya bar ni ba taimako.
Daleth. He hath turned aside my paths, and hath broken me in pieces, he hath made me desolate.
12 Ya ja kwarinsa ya sa in zama abin baratarsa.
Daleth. He hath bent his bow, and set me as a mark for his arrows.
13 Ya harbi zuciyata da kibiyoyin kwarinsa.
He. He hath shot into my reins the daughters of his quiver.
14 Na zama abin dariya ga mutanena duka; suna yi mini ba’a cikin waƙa dukan yini.
He. I am made a derision to all my people, their song all the day long.
15 Ya cika ni da kayan ɗaci ya gundure ni da abinci mai ɗaci.
He. He hath filled me with bitterness, he hath inebriated me with wormwood.
16 Ya kakkarya haƙorana da tsakuwa; ya tattake ni cikin ƙura.
Vau. And he hath broken my teeth one by one, he hath fed me with ashes.
17 An hana ni salama; na manta da ko mene ne ake kira wadata.
Vau. And my soul is removed far off from peace, I have forgotten good things.
18 Saboda haka na ce, “Darajata ta ƙare da kuma duk abin da nake begen samu daga wurin Ubangiji.”
Vau. And I said: My end and my hope is perished from the Lord.
19 Na tuna da azabata da kuma sintiri, da na yi ta yi da ɗacin rai.
Zain. Remember my poverty, and transgression, the wormwood, and the gall.
20 Na tuna su sosai, sai kuma na ji ba daɗi a raina.
Zain. I will be mindful and remember, and my soul shall languish within me.
21 Duk da haka na tuna da wannan na kuma sa bege ga nan gaba.
Zain. These things I shall think over in my heart, therefore will I hope.
22 Domin ƙaunar Ubangiji ba mu hallaka ba; gama jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa.
Heth. The mercies of the Lord that we are not consumed: because his commiserations have not failed.
23 Sababbi ne kowace safiya; amincinka kuwa mai girma ne.
Heth. They are new every morning, great is thy faithfulness.
24 Na ce wa kaina, “Ubangiji shi ne nawa; saboda haka zan jira shi.”
Heth. The Lord is my portion, said my soul: therefore will I wait for him.
25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke da bege a cikinsa, ga kuma wanda yake neman shi;
Teth. The Lord is good to them that hope in him, to the soul that seeketh him.
26 yana da kyau ka jira shiru domin samun ceton Ubangiji.
Teth. It is good to wait with silence for the salvation of God.
27 Yana da kyau mutum yă sha wuya tun yana yaro.
Teth. It is good for a man, when he hath borne the yoke from his youth.
28 Bari yă zauna shiru shi kaɗai, gama haka Ubangiji ya sa yă yi.
Jod. He shall sit solitary, and hold his peace: because he hath taken it up upon himself.
29 Bari yă ɓoye fuskarsa cikin ƙura kila akwai bege.
Jod. He shall put his mouth in the dust, if so be there may be hope.
30 Bari yă ba da kumatunsa a mare shi, yă kuma bari a ci masa mutunci.
Jod. He shall give his cheek to him that striketh him, he shall be filled with reproaches.
31 Gama Ubangiji ba ya yashe mutane har abada.
Caph. For the Lord will not cast off for ever.
32 Ko da ya kawo ɓacin rai, zai nuna tausayi sosai, ƙaunarsa tana da yawa.
Caph. For if he hath cast off, he will also have mercy, according to the multitude of his mercies.
33 Gama ba haka kawai yake kawo wahala ko ɓacin rai ga’yan adam ba.
Caph. For he hath not willingly afflicted, nor cast off the children of men.
34 Bai yarda a tattake’yan kurkuku a ƙasa ba,
Lamed. To crush under his feet all the prisoners of the land,
35 ko kuma a danne wa mutum hakkinsa a gaban Maɗaukaki,
Lamed. To turn aside the judgment of a man before the face of the most High,
36 ko kuma a danne wa mutum shari’ar gaskiya ashe Ubangiji ba zai ga irin waɗannan abubuwa ba?
Lamed. To destroy a man wrongfully in his judgment, the Lord hath not approved.
37 Wane ne ya isa yă yi magana kuma ta cika in ba Ubangiji ne ya umarta ba?
Mem. Who is he that hath commanded a thing to be done, when the Lord commandeth it not?
38 Ba daga bakin Maɗaukaki ne bala’i da abubuwa masu kyau suke fitowa ba?
Mem. Shall not both evil and good proceed out of the mouth of the Highest?
39 Don mene ne wani mai rai zai yi gunaguni sa’ad da aka ba shi horo domin zunubansa?
Mem. Why hath a living man murmured, man suffering for his sins?
40 Bari mu auna tafiyarmu mu gwada ta, sai mu kuma koma ga Ubangiji.
Nun. Let us search our ways, and seek, and return to the Lord.
41 Bari mu ɗaga zuciyarmu da hannuwanmu ga Allah na cikin sama, mu ce,
Nun. Let us lift up our hearts with our hands to the Lord in the heavens.
42 “Mun yi zunubi mun yi tawaye ba ka kuwa gafarta ba.
Nun. We have done wickedly, and provoked thee to wrath: therefore thou art inexorable.
43 “Ka rufe kanka da fushi, ka fafare mu; ka karkashe mu ba tausayi.
Samech. Thou hast covered in thy wrath, and hast struck us: thou hast killed and hast not spared.
44 Ka rufe kanka da gajimare don kada addu’armu ta kai wurinka.
Samech. Thou hast set a cloud before thee, that our prayer may not pass through.
45 Ka mai da mu tarkace da juji a cikin mutane.
Samech. Thou hast made me as an outcast, and refuse in the midst of the people.
46 “Dukan maƙiyanmu suna ta yin mana magana marar daɗi.
Phe. All our enemies have opened their mouths against us.
47 Muna cika da tsoro, da lalatarwa da hallakarwa.”
Phe. Prophecy is become to us a fear, and a snare, and destruction.
48 Hawaye na kwararowa daga idanuna domin an hallaka mutanena.
Phe. My eye hath run down with streams of water, for the destruction of the daughter of my people.
49 Idanuna za su ci gaba da kwararowa da hawaye, ba hutawa.
Ain. My eye is afflicted, and hath not been quiet, because there was no rest:
50 Har sai in Ubangiji ya duba daga sama ya gani.
Ain. Till the Lord regarded and looked down from the heavens.
51 Abin da nake gani yana kawo mini baƙin ciki domin dukan matan birnina.
Ain. My eye hath wasted my soul because of all the daughters of my city.
52 Maƙiyana suna farauta ta ba dalili kamar tsuntsu.
Sade. My enemies have chased me and caught me like a bird, without cause.
53 Sun yi ƙoƙari su kashe ni a cikin rami suka kuma jajjefe ni da duwatsu;
Sade. My life is fallen into the pit, and they have laid a stone over me.
54 ruwaye suka rufe kaina, sai na yi tunani cewa na kusa mutuwa.
Sade. Waters have flowed over my head: I said: I am cut off.
55 Na yi kira ga sunanka, ya Ubangiji, daga rami mai zurfi.
Coph. I have called upon thy name, O Lord, from the lowest pit.
56 Ka ji roƙona, “Kada ka toshe kunnuwanka ka ƙi jin roƙona na neman taimako.”
Coph. Thou hast heard my voice: turn not away thy ear from my sighs, and cries.
57 Ka zo kusa lokacin da na kira ka, kuma ka ce mini, “Kada ka ji tsoro.”
Coph. Thou drewest near in the day, when I called upon thee, thou saidst: Fear not.
58 Ya Ubangiji, ka goyi bayana; ka fanshi raina.
Res. Thou hast judged, O Lord, the cause of my soul, thou the Redeemer of my life.
59 Ya Ubangiji, ka ga inda aka yi mini ba daidai ba. Ka shari’anta, ka ba ni gaskiya!
Res. Thou hast seen, O Lord, their iniquity against me: judge thou my judgment.
60 Ka ga zurfin ramakonsu, da duk mugun shirin da suke yi mini.
Res. Thou hast seen all their fury, and all their thoughts against me.
61 Ya Ubangiji, ka ji zaginsu, da duka mugun shirin da suke yi mini
Sin. Thou hast heard their reproach, O Lord, all their imaginations against me.
62 Abin da maƙiyana suke yin raɗa a kai game da ni duk yini.
Sin. The lips of them that rise up against me: and their devices against me all the day.
63 Dube su! A zaune ko a tsaye, suna yi mini ba’a cikin waƙoƙinsu.
Sin. Behold their sitting down, and their rising up, I am their song.
64 Ka ba su abin da ya dace su samu, ya Ubangiji, domin abin da hannuwansu suka yi.
Thau. Thou shalt render them a recompense, O Lord, according to the works of their hands.
65 Ka sa yana ta rufe zuciyarsu, kuma bari la’anarka ta bi su.
Thau. Thou shalt give them a buckler of heart, thy labour.
66 Ka fafare su cikin fushi ka hallaka su daga cikin duniya ta Ubangiji.
Thau. Thou shalt persecute them in anger, and shalt destroy them from under the heavens, O Lord.

< Makoki 3 >