< Makoki 2 >

1 Yadda Ubangiji ya rufe Diyar Sihiyona da gizagizan fushi! Ya jefar da darajar Isra’ila daga sama zuwa ƙasa; bai tuna da wurin ɗora ƙafafunsa ba a ranar fushinsa.
How hath the Lord covered the daughter of Zion with a cloud in his anger! he hath cast down from heaven unto the earth the beauty of Israel, and hath not remembered his footstool in the day of his anger.
2 Ubangiji ya hallakar da wurin zaman Yaƙub ba tausayi; A cikin fushinsa kuma zai rurrushe kagaran Diyar Yahuda. Ya ƙasƙantar da mulki da masu mulki.
The Lord hath swallowed up all the habitations of Jacob, and hath not pitied; he hath thrown down in his wrath the strong holds of the daughter of Judah; he hath brought them down to the ground: he hath profaned the kingdom and the princes thereof.
3 A cikin zafin fushi ya fasa kowane ƙaho na Isra’ila. Ya janye hannun damansa sa’ad da maƙiyi ya zo. Ya yi ƙuna a cikin Yaƙub kamar wuta mai ƙone duk abin da yake kusa da ita.
He hath cut off in fierce anger all the horn of Israel; he hath drawn back his right hand from before the enemy: and he hath burned up Jacob like a flaming fire, which devoureth round about.
4 Kamar abokin gāba, ya ɗana bakansa; hannun damansa na shirye. Kamar maƙiyi, ya kashe duk wanda idonsa ya ji daɗin gani; ya zuba fushinsa kamar wuta a kan tenti na Diyar Sihiyona.
He hath bent his bow like an enemy, he hath stood with his right hand as an adversary, and hath slain all that were pleasant to the eye: in the tent of the daughter of Zion he hath poured out his fury like fire.
5 Ubangiji kamar maƙiyi ne; ya hallaka Isra’ila. Ya hallaka wurarenta duka ya kuma hallaka kagaranta. Ya ƙara yawan makoki da baƙin ciki wa Diyar Yahuda.
The Lord is become as an enemy, he hath swallowed up Israel; he hath swallowed up all her palaces, he hath destroyed his strong holds: and he hath multiplied in the daughter of Judah mourning and lamentation.
6 Ya rushe haikalinsa kamar lambu; ya hallaka wurin yi masa sujada. Ubangiji ya sa Sihiyona ta manta da bukukkuwanta da kuma ranakunta na Asabbaci; a cikin zafin fushinsa ya watsar da sarki da firist.
And he hath violently taken away his tabernacle, as if it were of a garden; he hath destroyed his place of assembly: the LORD hath caused solemn assembly and sabbath to be forgotten in Zion, and hath despised in the indignation of his anger the king and the priest.
7 Ubangiji ya ƙi bagadensa ya kuma yi wofi da haikalinsa. Ya ba maƙiyinta fadodinta; suka yi sowa a cikin gidan Ubangiji kamar a ranar da ake yin biki.
The Lord hath cast off his altar, he hath abhorred his sanctuary, he hath given up into the hand of the enemy the walls of her palaces: they have made a noise in the house of the LORD, as in the day of a solemn assembly.
8 Ubangiji ya ƙuduri niyya yă rushe bangon da yake kewaye da Diyar Sihiyona. Ya auna da igiyar awo bai fasa hallaka ta ba. Ya sa katanga da katanga duk suka lalace.
The LORD hath purposed to destroy the wall of the daughter of Zion; he hath stretched out the line, he hath not withdrawn his hand from destroying: but he hath made the rampart and wall to lament; they languish together.
9 Ƙofofinta sun nutse a cikin ƙasa; ya kakkarya ƙarafanta. Sarakunanta da’ya’yan sarakunanta duk an kai su bauta cikin waɗansu ƙasashe, babu sauran doka, annabawa kuma ba su samun wahayi daga wurin Ubangiji.
Her gates are sunk into the ground; he hath destroyed and broken her bars: her king and her princes are among the nations where the law is not; yea, her prophets find no vision from the LORD.
10 Dattawan Diyar Sihiyona sun zauna shiru a ƙasa; suka kuma sa rigar buhu.’Yan matan Urushalima suka sunkuyar da kawunansu ƙasa.
The elders of the daughter of Zion sit upon the ground, they keep silence; they have cast up dust upon their heads; they have girded themselves with sackcloth: the virgins of Jerusalem hang down their heads to the ground.
11 Idanuna sun dushe don yawan kuka, raina na cike da baƙin ciki; zuciyata ta karaya domin mutanena sun hallaka, domin yara da jarirai suna suma a kan hanyoyi a cikin birni.
Mine eyes do fail with tears, my bowels are troubled, my liver is poured upon the earth, for the destruction of the daughter of my people; because the young children and the sucklings swoon in the streets of the city.
12 Suna ce wa uwayensu, “Ina burodi da ruwan inabi?” Yayinda suke suma kamar mutanen da aka ji masu ciwo a cikin birni, sa’ad da suke mutuwa a hannuwan uwayensu.
They say to their mothers, Where is corn and wine? when they swoon as the wounded in the streets of the city, when their soul is poured out into their mothers’ bosom.
13 Me zan ce miki? Da me zan kwatanta ki, ke Diyar Urushalima? Da me zan misalta ki, yadda zan iya yi miki ta’aziyya, Ke Budurwa Diyar Sihiyona? Ciwonki yana da zurfi kamar teku. Wane ne zai iya warkar da ke?
What shall I testify unto thee? what shall I liken to thee, O daughter of Jerusalem? what shall I equal to thee, that I may comfort thee, O virgin daughter of Zion? for thy breach is great like the sea: who can heal thee?
14 Wahayin annabawanki ƙarya ne kuma marasa amfani; ba su tona zunubanki ba yadda za su iya ceto ki daga bauta ba. Sun yi miki annabcin ƙarya marar amfani.
Thy prophets have seen visions for thee of vanity and foolishness; and they have not discovered thine iniquity, to bring again thy captivity: but have seen for thee burdens of vanity and causes of banishment.
15 Duk masu wucewa suna yi miki tafi na reni; suna yi wa Diyar Urushalima tsaki suna kaɗa kai suna cewa, “Wannan ne birnin da aka ce kyakkyawa ne, mai farantawa dukan duniya rai?”
All that pass by clap their hands at thee; they hiss and wag their head at the daughter of Jerusalem, [saying]: Is this the city that men called The perfection of beauty, The joy of the whole earth?
16 Maƙiyanki duka suna ta surutu game da ke; suna tsaki suna cizon haƙora suna cewa, “Mun hallaka ta. Wannan ce ranar da muke jira; yau mun gan ta.”
All thine enemies have opened their mouth wide against thee; they hiss and gnash the teeth; they say, We have swallowed her up; certainly this is the day that we looked for; we have found, we have seen it.
17 Ubangiji ya yi abin da ya shirya; ya cika maganarsa, wadda ya umarta tun daɗewa. Ya jefar da ke ba tausayi, ya bari maƙiya sun yi nasara da ke, ya ɗaukaka ƙahon maƙiyanki.
The LORD hath done that which he devised; he hath fulfilled his word that he commanded in the days of old; he hath thrown down, and hath not pitied: and he hath caused the enemy to rejoice over thee, he hath exalted the horn of thine adversaries.
18 Zuciyar mutane ta yi kuka ga Ubangiji. Ya bangon Diyar Urushalima, bar hawayenki su zuba kamar rafi dare da rana; kada ki huta, kada idanunki su huta.
Their heart cried unto the Lord: O wall of the daughter of Zion, let tears run down like a river day and night; give thyself no respite; let not the apple of thine eye cease.
19 Ki tashi, ki yi kuka cikin dare, dare na yi sai ki fara kuka; kina buɗewa Ubangiji zuciyarki. Ki ɗaga hannuwanki gare shi domin rayukan’ya’yanki, waɗanda suka suma don yunwa a kan kowane titi.
Arise, cry out in the night, at the beginning of the watches; pour out thine heart like water before the face of the Lord: lift up thy hands toward him for the life of thy young children, that faint for hunger at the top of every street.
20 “Ka duba, ka gani ya Ubangiji. Wane ne ka taɓa yi wa haka? Ko ya kamata uwaye su ci’ya’yansu,’ya’yan da suka yi reno? Ko ya kamata a kashe firistoci da annabawa a cikin haikalin Ubangiji?
See, O LORD, and behold, to whom thou hast done thus! shall the women eat their fruit, the children that are dandled in the hands? shall the priest and the prophet be slain in the sanctuary of the Lord?
21 “Matasa da tsofaffi duk suna kwanciya a cikin ƙurar tituna; an karkashe matasa da’yan matana da takobi. Ka kashe su a ranar fushinka; ka kashe su ba tausayi.
The youth and the old man lie on the ground in the streets; my virgins and my young men are fallen by the sword: thou hast slain them in the day of thine anger; thou hast slaughtered, [and] not pitied.
22 “Kamar yadda kake yin gayyata a ranar biki, haka kake kawo mini tsoro a kowane gefe. A ranar fushin Ubangiji ba mai tserewa ba wanda zai tsira; maƙiyina ya kashe waɗanda na yi renonsu, na kuma lura da su.”
Thou hast called, as in the day of a solemn assembly, my terrors on every side, and there was none that escaped or remained in the day of the LORD’S anger: those that I have dandled and brought up hath mine enemy consumed.

< Makoki 2 >