< Mahukunta 1 >

1 Bayan da Yoshuwa ya rasu, Isra’ilawa suka tambayi Ubangiji suka ce, “Wane ne zai fara tafiya don yă yaƙi Kan’aniyawa dominmu?”
And it came to pass, after the death of Joshua, that the sons of Israel asked of Yahweh, saying, —Who shall go up for us against the Canaanites, first, to make war upon them?
2 Sai Ubangiji ya ce, “Yahuda zai tafi. Na riga na ba da ƙasar a hannunsu.”
And Yahweh said—Judah, shall go, —lo! I have delivered the land into his power.
3 Sa’an nan mutane Yahuda suka ce wa mutanen Simeyon “Ku zo tare da mu a yankin da aka ba mu rabon mu don mu yaƙi Kan’aniyawa. Mu ma mu bi ku wurin naku.” Saboda haka mutanen Simeyon suka tafi tare da su.
Then said Judah, unto Simeon his brother—Come up with me into the territory allotted me, and let us make war on the Canaanites, then will, I also, go with thee, into thy territory. So Simeon went with him.
4 Sa’ad da Yahuda ya fāɗa musu, Ubangiji kuwa ya ba da Kan’aniyawa da Ferizziyawa a hannunsu, suka kuwa kashe mutum dubu goma a Bezek.
And Judah went up, and Yahweh delivered the Canaanites and the Perizzites into their hand, —and they smote them in Bezek, ten thousand men.
5 A can suka iske Adoni-Bezek, suka yaƙe shi, suka fatattaki Kan’aniyawa da Ferizziyawa.
And they found Adoni-bezek in Bezek, and fought with him, —and smote the Canaanites and the Perizzites.
6 Sai Adoni-Bezek ya gudu, amma suka bi shi suka kama shi, suka yayyanka manyan yatsotsinsa na hannu da na ƙafa.
But Adoni-bezek fled, and they pursued him, —and took him, and cut off his thumbs, and his great toes.
7 Sa’an nan Adoni-Bezek ya ce, “Sarakuna saba’in waɗanda aka yayyanka manyan yatsotsinsu na hannu da na ƙafa, sun yi kalan abinci a ƙarƙashin teburina. Ga shi yanzu Allah ya rama abin da na yi musu.” Suka zo da shi Urushalima, a can kuwa ya mutu.
Then said Adoni-bezek—Seventy kings, with their thumbs and great toes cut off, have been picking up crumbs under my table, as I have done, so, hath God requited me. And they brought him into Jerusalem, and he died there.
8 Mutanen Yahuda suka yaƙi Urushalima ita ma suka ci ta. Suka karkashe mutanen birnin suka cinna mata wuta.
And the sons of Judah made war upon Jerusalem, and captured it, and smote it with the edge of the sword, —and, the city, they set on fire.
9 Bayan wannan, mutanen Yahuda suka gangara suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a ƙasar tudu, Negeb, da gindin tuddai a yammanci.
And, afterwards, the sons of Judah went down to make war upon the Canaanites, —dwelling in the hill country, and in the south, and in the lowland.
10 Suka ci gaba suka yaƙi Kan’aniyawan da suke zaune a Hebron (wadda dā ake kira Kiriyat Arba) suka kuma ci Sheshai, Ahiman da Talmai da yaƙi.
And Judah went against the Canaanites who were dwelling in Hebron, now, the name of Hebron, formerly, was Kiriath-arba, —and they smote Sheshai and Ahiman, and Talmai.
11 Daga nan kuma suka ci gaba suka yaƙi mutanen da suke zaune a Debir (da ake kira a dā Kiriyat Sefer).
And he went from thence, against the inhabitants of Debir, —now, the name of Debir, formerly, was Kiriath-sepher.
12 Sai Kaleb ya ce, “Duk wanda ya fāɗa wa Kiriyat Sefer ya kuma ci ta da yaƙi, zan ba shi’yata Aksa yă aura.”
And Caleb said, He that smiteth Kiriath-sepher, and captureth it, I will give unto him Achsah my daughter, to wife.
13 Sai Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kaleb ya ci birnin, saboda haka Kaleb ya ba shi’yarsa Aksa ya aura.
Then Othniel, son of Kenaz, Caleb’s younger brother, captured it, —and he gave him Achsah his daughter, to wife.
14 Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ta zuga shi yă roƙi mahaifinta fili. Sa’ad da ta sauko daga jakinta, sai Kaleb ya ce mata, “Me zan yi miki?”
And it came pass, when she came, that she moved him to ask of her father a field, and, when she alighted from off the ass, Caleb said unto her—What aileth thee?
15 Sai ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman. Da yake ka ba ni ƙasa a Negeb, to, sai ka ba ni maɓulɓulan ruwa kuma.” Sai Kaleb ya ba ta maɓulɓulan bisa da kuma na ƙasa.
And she said unto him—Give me a present; for, south land, hast thou given me, give me therefore pools of water. So Caleb gave her Upper-pools, and Lower-pools.
16 Zuriyar surukin Musa, Keniyawa, suka haura daga Birnin dabino tare da mutanen Yahuda don su zauna cikin mutanen Hamadan Yahuda a cikin Negeb kusa da Arad.
Now, the sons of the Kenite, father-in-law of Moses, had come up from the city of palm-trees, with the sons of Judah, into the wilderness of Judah, which is in the south of Arad, —so they went and dwelt with the people.
17 Sa’an nan mutanen Yahuda suka tafi tare da’yan’uwansu mutanen Simeyon suka fāɗa wa Kan’aniyawan da suke zaune cikin Zefat, suka kuwa hallaka birnin gaba ɗaya. Saboda haka aka kira wurin Horma.
Then went Judah, with Simeon his brother, and they smote the Canaanites dwelling in Zephath, —and devoted it to destruction, and the name of the city was called Hormah.
18 Mutanen Yahuda kuma suka ci Gaza, Ashkelon, da Ekron, kowace birni tare da yankinsa.
And Judah captured Gaza with the boundaries thereof, and Ashkelon, with the boundaries thereof, —and Ekron, with the boundaries thereof.
19 Ubangiji kuwa yana tare da mutane Yahuda. Suka mallaki ƙasar tudu, amma ba su iya suka kori mutanen daga filaye ba, domin suna da keken yaƙin ƙarfe.
And it same to pass that Yahweh was with Judah, and he took possession of the hill country, —but did not dispossess the inhabitants of the vale, because they had, chariots of iron.
20 Yadda Musa ya yi alkawari, sai aka ba Kaleb Hebron, wanda ya kori daga cikinta’ya’ya maza uku na Anak.
So they gave unto Caleb Hebron, as spake Moses, —and he drave out from thence the three sons of Anak.
21 Ko da yake mutanen Benyamin sun kāsa su kori Yebusiyawa, waɗanda suke zaune a Urushalima; har yă zuwa yau, Yebusiyawa suna zaune a can tare da mutanen Benyamin.
But, the Jebusites dwelling in Jerusalem, the sons of Benjamin did not drive out, —but the Jebusites have dwelt with the sons of Benjamin, in Jerusalem, unto this day.
22 To, gidan Yusuf suka auka wa Betel, Ubangiji kuwa yana tare da su.
Then went up the house of Joseph—they also, —unto Bethel, —and, Yahweh, was with them.
23 Sa’ad da suka aike mutane don su leƙi asirin Betel (da dā ake kira Luz),
And the house of Joseph sent to spy out Bethel, —now, the name of the city, formerly, was, Luz.
24 ’yan leƙen asirin suka ga wani ya fito daga birnin sai suka ce masa, “Ka nuna mana yadda za mu shiga birnin, mu kuwa za mu yi maka alheri.”
So the watchers saw a man, coming forth from the city, —and they said unto him—Shew us, we pray thee, the way to get into the city, and we will deal with thee, in lovingkindness.
25 Saboda haka ya nuna musu, suka kuwa hallaka birnin, suka bar mutumin da dukan iyalinsa da rai.
And he shewed them the way to get into the city, and they smote the city, with the edge of the sword, —but, the man and all his family, they let go.
26 Sa’an nan ya tafi ƙasar Hittiyawa, inda ya gina birni ya kuma kira shi Luz, haka ake kira birnin har wa yau.
And the man went into the land of the Hittites, —and built a city, and called the name thereof, Luz, that, is the name thereof, unto this day.
27 Amma Manasse ba su kori mutane Bet-Sheyan ko Ta’anak ko Dor ko Ibileyam ko Megiddo tare da ƙauyukansu ba, gama Kan’aniyawa sun dāge su zauna a wannan ƙasa.
But Manasseh took not possession of Beth-shean and her towns, nor of Taanach and her towns, nor dispossessed the inhabitants of Dor and her towns, nor the inhabitants of Ibleam, and her towns, nor the inhabitants of Megiddo, and her towns, —but the Canaanites were determined to remain in this land;
28 Sa’ad da Isra’ila ta yi ƙarfi, sai suka tilasta Kan’aniyawa yin aikin gandu amma ba su kore su gaba ɗaya ba.
when Israel, however, had waxed strong, they put the Canaanites under tribute, —though they, dispossessed, them not.
29 Haka Efraim ma bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Gezer ba, amma Kan’aniyawa suka ci gaba da zama tare da su.
And, Ephraim, dispossessed not the Canaanites who were dwelling in Gezer, —so the Canaanites remained in their midst, in Gezer.
30 Haka kuma Zebulun bai kori Kan’aniyawa da suke zaune a Kitron da Nahalol, waɗanda suka rage a cikinsu ba; sai dai sun sa su aikin gandu.
Zebulun, dispossessed not the inhabitants of Kitron, nor the inhabitants of Nahalol, —but the Canaanites remained in their midst, and came under tribute.
31 Haka Asher ma bai kori waɗanda suke zama a Akko ko Sidon ko Ahlab ko Akzib ko Helba ko Afik ko kuma Rehob ba,
Asher, dispossessed not the inhabitants of Acco, nor the inhabitants of Zidon, —nor of Ahlab, nor of Achzib, nor of Helbah, nor of Aphik, nor of Rehob;
32 kuma saboda wannan ne mutanen Asher suke zaune cikin mazaunan ƙasar Kan’aniyawa.
but the Asherites dwelt in the midst of the Canaanites, the inhabitants of the land, —for they dispossessed them not.
33 Haka kuma Naftali bai kori waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh ko Bet-Anat; amma mutanen Naftali su ma suna zama a ciki Kan’aniyawa mazaunan ƙasar, waɗanda suke zaune a Bet-Shemesh da Bet-Anat kuwa suka zama masu yi musu aikin gandu.
Naphtali, dispossessed not the inhabitants of Beth-shemesh nor the inhabitants of Beth-anath, but they dwelt in the midst of the Canaanites, the inhabitants of the land, —and, the inhabitants of Beth-shemesh, and of Beth-anath, became theirs, under tribute.
34 Amoriyawa suka matsa wa mutanen Dan a ƙasar tudu, ba su yarda musu su gangaro zuwa filaye ba.
And the Amorites forced the sons of Dan into the hill country, —for they suffered them not to come down into the vale;
35 Su Amoriyawa kuma suka dāge su zauna a Dutsen-Heres, Aiyalon, da Sha’albim. Amma yayinda mutanen Yusuf suka ƙara ƙarfi, sai suka su yin musu aikin gandu.
and, though the Amorites were determined to remain in the hill country of Heres, in Aijalon, and in Shaalbim, yet was the hand of the house of Joseph heavy, so that they came under tribute.
36 Iyakar Amoriyawa kuwa daga Mashigin Kunama zuwa Sela da kuma zuwa gaba.
And, the boundary of the Amorites, was from the ascent of Akrabbim, from Sela and upwards.

< Mahukunta 1 >