< Mahukunta 18 >

1 To, a kwanakin nan Isra’ila ba ta da sarki. A kwanakin kuwa zuriyar Dan tana neman wurinsu na zama, gama ba su riga sun sami gādo tare da kabilan Isra’ila ba.
En ce temps-là il n'y avait point de roi en Israël; et la tribu de Dan cherchait en ce temps-là un domaine pour elle, afin d'y habiter; car jusqu'alors il ne lui était point échu d'héritage parmi les tribus d'Israël.
2 Saboda haka mutanen Dan suka aika jarumawa guda biyar daga Zora da Eshtawol don su leƙi asirin ƙasar su kuma bincike ta. Waɗannan mutanen sun wakilci dukan kabilar. Suka ce musu, “Ku je, ku bincike ƙasar.” Mutanen suka shiga ƙasar tudu ta Efraim suka zo gidan Mika, inda suka kwana.
Les enfants de Dan envoyèrent donc cinq hommes de leur famille, pris d'entre eux tous, gens vaillants, de Tsora et d'Eshthaol, pour explorer le pays et le reconnaître; et ils leur dirent: Allez, explorez le pays. Ils vinrent dans la montagne d'Éphraïm jusqu'à la maison de Mica, et ils y passèrent la nuit.
3 Sa’ad da suka yi kusa da gidan Mika, sai suka gane muryar saurayin nan Balawe; saboda haka suka shiga wurin suka tambaye shi, “Wa ya kawo ka nan? Me kake yi a nan? Me ya sa kake a nan?”
Et comme ils étaient auprès de la maison de Mica, ils reconnurent la voix du jeune Lévite; et, s'étant approchés de cette maison, ils lui dirent: Qui t'a amené ici? que fais-tu dans ce lieu? et qu'as-tu ici?
4 Ya gaya musu abin da Mika ya faɗa masa ya ce, “Ya ɗauke ni aiki ya kuma sa in zama masa firist.”
Et il répondit: Mica fait pour moi telle et telle chose, il me donne un salaire, et je lui sers de sacrificateur.
5 Sa’an nan suka ce masa, “Muna roƙonka ka nemi mana nufin Allah don mu sani ko tafiyarmu tana da nasara.”
Ils dirent encore: Nous te prions, consulte Dieu, afin que nous sachions si le voyage que nous entreprenons sera heureux.
6 Firist ya amsa ya ce, “Ku sauka lafiya, gama tafiyarku tana da yardan Ubangiji.”
Et le sacrificateur leur dit: Allez en paix; l'Éternel a devant ses yeux le voyage que vous entreprenez.
7 Saboda haka mutum biyar ɗin suka tashi suka iso Layish, inda suka ga mutane suna zamansu a huce, kamar Sidoniyawa, ba sa zato ga tsaro. Kuma da yake ƙasarsu ba ta bukata kome, suna da wadata. Suna kuma nesa da Sidoniyawa, ba sa kuma hulɗa da kowa.
Ces cinq hommes partirent donc, et ils arrivèrent à Laïs. Ils virent que le peuple qui y était, habitait en sécurité, à la manière des Sidoniens, tranquille et confiant, sans que personne dans le pays eût autorité sur eux et leur fît injure en rien; ils étaient éloignés des Sidoniens, et ils n'avaient à faire avec personne.
8 Da suka komo Zora da Eshtawol,’yan’uwansu suka tambaye su, “Me kuka gano?”
Ils revinrent ensuite auprès de leurs frères à Tsora et à Eshthaol, et leurs frères leur dirent: Que rapportez-vous?
9 Suka ce, “Ku zo mu yaƙe su! Mun ga ƙasar tana da kyau sosai. Ba za ku yi wani abu ba? Kada ku yi wata-wata, ku je kun mallaki ƙasar.
Et ils répondirent: Allons, montons contre eux; car nous avons vu le pays, et voici, il est très bon. Quoi! vous êtes sans rien dire? Ne soyez point paresseux à partir, pour aller posséder ce pays.
10 Sa’ad da kun kai can, za ku iske mutanen suna zama a sake, ƙasar kuwa mai faɗi ce wadda Allah ya sa a hannuwanku, ƙasar da ba tă rasa kome ba.”
Quand vous y entrerez, vous arriverez vers un peuple qui est en pleine sécurité. Le pays est de grande étendue, et Dieu l'a livré entre vos mains. C'est un lieu où rien ne manque de tout ce qui est sur la terre.
11 Sai mutane ɗari shida daga kabilar Dan suka yi ɗamarar yaƙi, suka tashi daga Zora da Eshtawol.
Il partit donc de là, de Tsora et d'Eshthaol, de la famille de Dan, six cents hommes munis de leurs armes.
12 A kan hanyarsu suka kafa sansani kusa da Kiriyat Yeyarim a Yahuda. Shi ya sa a ana kira wurin nan yamma da Kiriyat Yeyarim Mahane Dan har wa yau.
Ils montèrent et campèrent à Kirjath-Jéarim, en Juda; et on a appelé ce lieu-là Machané-Dan (camp de Dan), jusqu'à ce jour; il est derrière Kirjath-Jéarim.
13 Daga can suka tafi ƙasar tudu ta Efraim suka zo gidan Mika.
Puis de là ils passèrent dans la montagne d'Éphraïm, et arrivèrent jusqu'à la maison de Mica.
14 Sa’an nan mutum biyar ɗin nan da suka leƙi asirin ƙasar Layish suka ce wa’yan’uwansu, “Kun san cewa ɗaya daga cikin gidajen nan yana da efod, waɗansu allolin iyali, siffar da aka sassaƙa da kuma gunki na zubi? To, kun san abin da za ku yi.”
Alors les cinq hommes qui étaient allés pour explorer le pays de Laïs, prenant la parole, dirent à leurs frères: Savez-vous que dans ces maisons il y a un éphod et des théraphim, une image taillée et une image de fonte? Voyez donc maintenant ce que vous avez à faire.
15 Saboda haka suka juya a wurin suka shiga gidan saurayin nan Balawe a wajen Mika suka gaishe shi.
Alors ils s'approchèrent de là, et entrèrent dans la maison du jeune Lévite, dans la maison de Mica, et le saluèrent.
16 Mutanen Dan ɗari shida da suka sha ɗamarar yaƙi suka tsaya a bakin ƙofa.
Or, les six cents hommes d'entre les fils de Dan, qui étaient sous les armes, s'arrêtèrent à l'entrée de la porte.
17 Sai mutum biyar da suka leƙi asirin ƙasar suka shiga ciki suka ɗauke gunkin da aka sassaƙa, efod, sauran allolin gida da kuma gunki na zubi yayinda firist ɗin tare da mutane ɗari shida da suka yi ɗamarar yaƙi suna tsaye a bakin ƙofa.
Mais les cinq hommes qui étaient allés pour explorer le pays, montèrent, entrèrent dans la maison, et prirent l'image taillée, l'éphod, les théraphim et l'image de fonte, pendant que le sacrificateur était à l'entrée de la porte, avec les six cents hommes armés.
18 Sa’ad da waɗannan mutane suka shiga gidan Mika suka ɗauke gunkin da aka sassaƙa, efod, sauran allolin gida da kuma gunki na zubi, sai firist ya ce musu, “Me kuke yi?”
Étant donc entrés dans la maison de Mica, ils prirent l'image taillée, l'éphod, les théraphim et l'image de fonte. Et le sacrificateur leur dit: Que faites-vous?
19 Suka ce, “Ka yi shiru! Kada ka ce wani abu. Zo tare da mu, ka zama mahaifinmu da kuma firist. Bai fi maka ka yi wa kabila da kuma zuriya a Isra’ila aikin firist ba, da ka bauta wa iyali guda kawai?”
Mais ils lui dirent: Tais-toi, et mets ta main sur ta bouche, et viens avec nous; tu nous serviras de père et de sacrificateur. Lequel vaut mieux pour toi, d'être sacrificateur de la maison d'un seul homme, ou d'être sacrificateur d'une tribu et d'une famille en Israël?
20 Sai firist ya yi farin ciki. Ya ɗauki efod, sauran allolin gida da siffar da aka sassaƙa ya tafi tare da mutanen.
Alors le sacrificateur eut de la joie en son cœur; il prit l'éphod, les théraphim et l'image taillée, et se mit au milieu du peuple.
21 Suka sa’ya’yansu ƙanana a gaba, dabbobinsu da mallakansu a gabansu, suka juya suka tafi.
Ils se remirent donc en chemin, et marchèrent, en plaçant devant eux les petits enfants, le bétail et les bagages.
22 Sa’ad da suka yi ɗan nisa daga gidan Mika, sai aka kira mutanen da suke maƙwabtakar da Mika suka taru suka bi mutanen Dan suka cim musu.
Ils étaient déjà loin de la maison de Mica, lorsque ceux qui étaient dans les maisons voisines de celle de Mica, se rassemblèrent à grand cri, et poursuivirent les enfants de Dan.
23 Da suna ihu suna binsu, sai mutanen Dan suka waiga suka cewa Mika, “Mece ce damuwarka da ka kira mutanenka su zo su fāɗa mana?”
Et ils crièrent après eux. Mais eux, tournant visage, dirent à Mica:
24 Ya amsa ya ce, “Kun kwashe allolin da na yi, da kuma firist nawa, kuka tafi. Me kuma nake da shi? Yaya za ku ce, ‘Mece ce damuwata?’”
Qu'as-tu, que tu cries ainsi? Il répondit: Vous avez enlevé mes dieux, que j'avais faits, ainsi que le sacrificateur, et vous êtes partis. Que me reste-t-il? Et comment me dites-vous: Qu'as-tu?
25 Mutanen Dan suka ce, “Kada ka kuskura ka ce kome, in ba haka ba mutanen nan za su harzuƙa, da kai da iyalinka duka ku rasa rayukanku.”
Mais les enfants de Dan lui dirent: Ne nous fais point entendre ta voix, de peur que des hommes irrités ne se jettent sur vous, et que vous n'y laissiez la vie, toi et ta famille.
26 Saboda haka mutanen Dan suka kama hanyarsu, Mika kuwa da ya ga an fi ƙarfinsa, sai ya juya ya koma gida.
Les descendants de Dan continuèrent donc leur chemin. Et Mica, voyant qu'ils étaient plus forts que lui, tourna visage et revint en sa maison.
27 Sa’an nan suka ɗauko abin da Mika ya yi, da firist nasa, suka tafi Layish, suka fāɗa wa mutanen da suke zaman lafiya, ransu kuma a kwance. Suka fāɗa musu suka kuma ƙone birninsu.
Ainsi, ayant pris les choses que Mica avait faites et le sacrificateur qu'il avait, ils tombèrent sur Laïs, sur un peuple tranquille et qui se croyait en sûreté; et ils le firent passer au fil de l'épée; puis, ayant mis le feu à la ville, ils la brûlèrent.
28 Ba wanda zai cece su domin suna nesa da Bet-Sidon kuma ba sa hulɗa da kowa. Birnin yana a kwari kusa da Bet-Rekob. Mutanen Dan suka sāke gina birnin suka zauna a can.
Et il n'y eut personne qui la délivrât; car elle était loin de Sidon; ses habitants n'avaient aucun commerce avec personne, et elle était située dans la vallée qui s'étend vers Beth-Réhob. Ils rebâtirent la ville, et y habitèrent.
29 Suka sa wa birnin suna Dan, wato, sunan kakansu Dan, wanda aka haifa wa Isra’ila, ko da yake a dā ana kira birnin Layish.
Et ils nommèrent cette ville-là, Dan, d'après le nom de Dan, leur père, qui était né à Israël; mais le nom de la ville était auparavant Laïs.
30 A can mutanen Dan suka kafa wa kansu gumaka, Yonatan ɗan Gershom, ɗan Musa, da’ya’yansa maza firistoci ne na kabilar Dan har lokacin da aka kwashe mutane zuwa bauta.
Puis les enfants de Dan dressèrent pour eux l'image taillée; et Jonathan, fils de Guershon, fils de Manassé, lui et ses enfants, furent sacrificateurs pour la tribu de Dan jusqu'au jour où ils furent conduits hors du pays.
31 Suka ci gaba da amfani da gumakan da Mika ya yi, a duk wannan lokacin gidan Allah yana a Shilo.
Ils établirent pour eux l'image taillée que Mica avait faite, pendant tout le temps que la maison de Dieu fut à Silo.

< Mahukunta 18 >